25/08/2026
TAYA AL’UMMAR MUSULMI MURNAR MAULUDI ﷺ
Kafin aiko da Manzon Allah ﷺ, aljanu sun kasance suna neman jin labaran sama. Amma da Allah Ya so a kare abin da ke cikin sama, sai aka sanya masu gadi da shauhun wuta domin kada su sake samun damar satar jin labarin.
Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce:
﴿وَأَنَّا لَا نَدْرِي أَشَرٌّ أُرِيدَ بِمَن فِي الْأَرْضِ أَمْ أَرَادَ بِهِمْ رَبُّهُمْ رَشَدًا﴾
Ma’ana: “Ba mu sani ba, shin an nufi waɗanda suke cikin ƙasa da sharri ne, ko kuwa Ubangijinsu Ya nufe su da shiriya.”
(Suratul Jinn: 10)
Wannan yana tunatar da mu girman alherin da Allah Ya kawo wa duniya ta hanyar aiko da Annabin rahama, Muhammad ﷺ, wanda Allah Ya aiko shi da shiriya da haske.
Kamar yadda mawaƙin Larabci Ahmad Shawqi ya bayyana:
«وُلِدَ الهُدَى فَالكَائِنَاتُ ضِيَاءُ»
“An haifi shiriya, sai halittu s**a haskaka.
Allah Ya aiko ManzonSa ﷺ domin ya fitar da mutane daga duhun jahilci zuwa hasken imani, ya koyar da su gaskiya, adalci, tausayi da kyawawan ɗabi’u.
Allahumma salli wa sallim wa baarik ‘ala Sayyidina Muhammadin wa ‘ala alihi wa sahbihi ajma’in.
Muna taya daukacin al’ummar Musulmi murnar Mauludin Annabi Muhammad ﷺ.
Allah Ya ƙara mana ƙaunarsa, Ya sanya mu cikin waɗanda za su bi Sunnarsa, Ya kuma haɗa mu da shi a Aljannar Firdausi. Amin.