Jama’ar Arewa

Jama’ar Arewa Labarai da Dumi-Duminsu daga ciki da wajen Najeriya
(1)

WATA SABUWA: Jigo A Jam’iyyar APC Ya Gargadi Nasiru El-Rufa’i Kan Ya Rage Shan Kwaya, Domin Ta Fara Sashi Sambatu — Dakt...
24/06/2025

WATA SABUWA: Jigo A Jam’iyyar APC Ya Gargadi Nasiru El-Rufa’i Kan Ya Rage Shan Kwaya, Domin Ta Fara Sashi Sambatu — Dakta Sani Ahmad Zangina

Mai Fashin Baki kan Lamuran Siyasa Dakta. Sani Ahmad Zangina ya shawarci tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufa’i, da ya daina shan kayan maye, yana mai cewa alamu sun nuna hakan ya fara yin tasiri ga hankalinsa.

Dakta Zangina ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa kwayar da El-Rufa’i ke sha ita ce ke haddasa masa haukace-haukace, har ta kai ga ya fara zagin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu, shugaban da ke da ƙaunar Nijeriya da al'ummar ƙasa, musamman talakawa.

A cikin zazzafan martanin da ya fitar, Zangina ya caccaki El-Rufa’i bisa sukar mulkin Tinubu, yana mai cewa hakan ya nuna ba don gyara ba ne yake zage zage, sai don wata manufa ta kashin kansa.

Idan da gaske ne El-Rufa’i na son cigaban Nijeriya, da bai bijire wa gaskiya ba. Amma yau sai ga shi yana ƙoƙarin ɓata sunan shugaba Tinubu da gwamnatin sa, saboda kawai ba a sake damƙa masa mukami ba,” in ji Zangina.

Ya ƙara da cewa lokaci ya yi da El-Rufa’i zai koma ya gyara kansa, “domin duk wanda ke zagin wanda ya fi shi tausayi da adalci, to tabbas akwai matsala a tattare da shi.

Mayu 29: Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Arewa Online ta Aika Saƙon Gaisuwa ga Ƙasa, Ta Ƙara Jaddada Kudurinta ga Yankin ArewaYa...
29/05/2025

Mayu 29: Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Arewa Online ta Aika Saƙon Gaisuwa ga Ƙasa, Ta Ƙara Jaddada Kudurinta ga Yankin Arewa

Yayinda Najeriya ke bikin ranar Democracy Day da cika shekaru na mulkin farar hula a yau, 29 ga Mayu, Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Arewa (Arewa Online Journalists Forum - AOJF) ta aike da saƙon gaisuwa mai cike da ƙauna ga daukacin ‘yan ƙasa, musamman ga al’ummar Arewa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, ƙungiyar ta yaba da juriyar ‘yan Najeriya, da haɗin kai da kuma ruhin dimokuraɗiyya da suke nunawa, tare da kira ga kowa da kowa da ya ci gaba da kasancewa da bege da kuma kishin ƙasa wajen gina Najeriya mai ɗorewa.

“Ranar 29 ga Mayu, ba kawai biki ba ne na dimokuraɗiyya; tana tunatar da mu nauyin da ya rataya a wuyar kowa wajen gina ƙasa mafi kyau. Muna girmama jaruntakar ‘yan Najeriya daga kowane yanki, musamman mutanen Arewa masu daraja, waɗanda ke ci gaba da tsayawa kan gaskiya, ɗa’a da kishin ƙasa duk da ƙalubale da dama,” in ji ƙungiyar.

Ƙungiyar ta kuma jaddada muhimmancin kafafen yaɗa labarai masu ‘yanci, aikin jarida na gaskiya, da kuma ƙarfafa ‘yan ƙasa wajen shiga cikin harkokin ƙasa, musamman a Arewa, a matsayin hanyoyi na sanya shugabanni su zama masU riko da gaskiya, da kuma ƙarfafa tushen dimokuraɗiyya a ƙasar.

“Muna sake tabbatar da kudurinmu na amfani da dandalinmu wajen inganta gaskiya, ba da dama ga marasa murya, da kuma tallafa wa ci gaba a Arewa da ma Najeriya baki ɗaya.”

Ƙungiyar ta kuma yi kira ga shugabanni a kowane mataki da su fifita tsaro, ilimi, ƙarfafa matasa, da bunƙasa tattalin arziki, musamman a cikin al’ummomin da ba su da isasshen kulawa a Arewacin ƙasar.

Yayinda ƙasa ke tunani kan tafiyar dimokuraɗiyya da ci gaban da aka samu, AOJF ta bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da jajircewa wajen neman zaman lafiya, haƙuri da kuma shugabanci mai haɗin kai, tana mai jaddada cewa makomar Najeriya na hannun kowane ɗan ƙasa.

Sa Hannun : Sakataren kungiyar na Kasa : Sani Ahmed

Tsohon Ministan Shari'ar Najeriya Abubakar Malami SAN.Da me kuke tunawa dashi?
21/04/2025

Tsohon Ministan Shari'ar Najeriya Abubakar Malami SAN.

Da me kuke tunawa dashi?

Ku kyautatawa Tinubu zato na alkhairi domin yana da kyakkyawar manufa kan mutanen Arewa.Ministan Yada Labarai Muhammed I...
21/04/2025

Ku kyautatawa Tinubu zato na alkhairi domin yana da kyakkyawar manufa kan mutanen Arewa.

Ministan Yada Labarai Muhammed Idris

Muhimmin sako daga ministan yada labarai na Najeriya.
21/04/2025

Muhimmin sako daga ministan yada labarai na Najeriya.

Shahadar Fafaroma Francis abin sha'awa ce. Tinubu
21/04/2025

Shahadar Fafaroma Francis abin sha'awa ce. Tinubu

01/04/2025
20/03/2025
20/03/2025
20/03/2025

Anya N'Golo Kante yasan yadda ake kashe kudi kuwa....

Wannan itace matar da ya Aura....

Zahiri ba gaibu ba.

Address

Kano State

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jama’ar Arewa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share