Arewa Digital

Arewa Digital This is the official page for Arewa Digital Updates

TOH FA!!! MOOFY YA HAKA WANI ABU SAI MATA🥰😍🥰😍.Yawancin yaran nan masu cewa suna sona bakusan na haifeku bane 😡😡😡😡Kuke gi...
16/05/2023

TOH FA!!! MOOFY YA HAKA WANI ABU SAI MATA🥰😍🥰😍.

Yawancin yaran nan masu cewa suna sona bakusan na haifeku bane 😡😡😡😡

Kuke girmama mamanku please 🙏🏻

RA'AYI RIGA DAGA BAKIN MOOFY.Kullum Ina kara godewa tsohon saurayina da kuma mahaifiyarsa dayarabu dani.Ciwon rabuwarsa ...
14/05/2023

RA'AYI RIGA DAGA BAKIN MOOFY.
Kullum Ina kara godewa tsohon saurayina da kuma mahaifiyarsa dayarabu dani.Ciwon rabuwarsa danine yasani na koma karatu,Na samu nasarori bila adadin bayan yaudarata dayayi.Yanzu ko bashi da wani aiki sai zaman gulma a gindin bishiya.Wani hanin ga Allah……….

POV:Ina kara kira ga yan uwana mata da su dage wajen neman ilimi.Alhamdulillah gashi Ina bautawa kasata bayan wannan kuma sai digiri na biyu(Masters)

Yadda aka gudanar da sunan ƴaƴan Magen wata Matashiya a unguwar Sheka Kudu dake ƙaramar hukumar Kumbotso a Kano.Matashiy...
10/05/2023

Yadda aka gudanar da sunan ƴaƴan Magen wata Matashiya a unguwar Sheka Kudu dake ƙaramar hukumar Kumbotso a Kano.

Matashiyar mai suna Halima Adam mai laƙabin ƴar Madara, ta ce, har kwana biyu ta yi a gadon Asibiti, lokacin da aka sace ma ta uwar Magunanta.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Yanzu nake samun labarin rasuwar Dr Aminu Mai Chemist wanda aka fi sani da "KAWU MALA...
08/05/2023

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Yanzu nake samun labarin rasuwar Dr Aminu Mai Chemist wanda aka fi sani da "KAWU MALA" a cikin shirin DADIN KOWA.

Muna Addu'ar Allah Ya jikansa ya gafarta masa kurakuransa yasa Aljanna ce makomarsa. Idan tamu tazo Allah yasa mu cika da kyau da imani.

R.I.J.F 😭 😭 😭 😭

DAKTA NA’IMA IDRIS LIKITA ABAR ALFARIN ARÈWA DAMA NAHÍYAR AFRIKA GABA DAYÀAddinin Musulunci wayayyen addini ne wanda ya ...
05/05/2023

DAKTA NA’IMA IDRIS LIKITA ABAR ALFARIN ARÈWA DAMA NAHÍYAR AFRIKA GABA DAYÀ

Addinin Musulunci wayayyen addini ne wanda ya ba wa dukkan al'umma maza da mata damar neman ilimi da gudanar da ayyukan cigaban rayuwar al'umma.

Tun farkon zuwan Addinin Musulunci, mata sun samu damar sanin ilimin likitanci da kuma yi wa marasa lafiya maza da mata magani musamman ma a wurin yaƙi.

A zamanin Manzon Allah SAW an samu mace likita mai suna Rufayda Bint Sa'ad Al-Aslamiyya. A lokacin yaƙin Badar ranar 13 Ga Watan Mach, 624 CE ita ce ta yi wa musulmai mayaƙa magani kan raunukan da su ka samu. Rufaida ta samu mafi yawan iliminta na likitanci a wurin mahaifinta Sa'ad Al-Aslami wanda masanin kiwon lafiya ne.

Sai kuma Al-Shifa Bint Al-Quraishiyya Al-Adawiyah, ta kasance ɗaya daga cikin wayayyun mata a wancan lokacin wacce ta ke da ilimin magunguna. Sunanta na asali Layla, amma ta samu laƙabin suna "Shifa" (Waraka).

Bayan ita sai kuma Nusayba Bint Ka'ab Al-Mazneya wacce ta gudanar da aikinta na Likitanci a lokacin yaƙin Uhud. Da kuma Ummu Sinan Al-Islami wacce ita ma ta nemi izinin Manzon Allah SAW ta je wurin yaƙi ta gudanar da aikin yin magani ga waɗanda aka ji wa raunuka da kuma ba da ruwan sha ga mayaƙa.

Sai Ummu Warƙa Bint Harith wacce ta ba da gudunmawa wajen haɗa alqur'ani wuri guda, ita ma ta yi aikin likitanci a lokacin yaƙin Badar.

Daɗi da ƙari, akwai Nusayba Bint Al-Harith wacce aka fi sani da Ummu Al-Athia, ita ma likita ce har kaciya ta ke yi sannan kuma ta ba da gudunmawa wajen ba da agajin gaggawa ga mayaƙa a filin daga da kuma tallafa musu da ruwan sha.

Bayan fannin ilimin lafiya, sauran fannonin ilimi ma ba a bar mata a baya ba. Sutayta Al-Mahamili gogaggiyar masaniyar ilimin lissafi ce da adabin Larabci da hadisi da sanin hukunce-hukuncen shari'a.

Sutayta ta taso a gida na ilimi a birnin Baghadad ta rayuwa a tsakiyar ƙarni na 10. Ta samu yabo daga manyan malaman tarihi kamar su: Ibn al-Jawzi, Ibn al-Khatib Baghdadi da kuma Ibn Kathir.

Ayesha ƴa ce ga Prince Ahmed na Andulus wacce ta rayuwa a ƙarni na 11 gwana ce a fannin Ilimin Rhyme da Oratory. Sannan Labirare ɗinta ya kasance ɗaya daga cikin ƙayatattun labirare cikakku a masarautar Andulus.

A fannin fasaha da zane mai kyau akwai Thana, baiwa a gidan Ibn Qayyum. Sai kuma Rasa a ƙasar Indiya wacce ta wallafa littafi kan magunguna da kulawa da mata. Sai kuma Mariyah Al-Qibtiyya ƴar ƙasar Masar wacce ita ma ta yi wallafa a ƙarni na bakwai. Wata ƙwararriyar a fannin ilimin kimiyya ita ce Al-Ijiliyyah Bint Al-Ijili Al-Asturlabi wacce ta bi sahun aikin mahaifinta na kimiyya a birnin Aleppo a Arewacin Siriya a ƙarni na 10. Kaɗan kenan daga cikin manyan mata masana da aka taɓa yi a tarihin Duniya.

A wannan zamanin a kasa irin Nígeria Allah ya azurta mu da hazikan mata irin su Dr. Dr. Dr. Naima Idris Usman likita abar alfaharin Arewa dama Nahiyar Africa gaba daya.

Address

Block D4 Hamisu Abba Plaza Tarauni
Kano State

Telephone

+2349132919111

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Digital posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Digital:

Share