YMC Hausa

YMC Hausa Muryar Al’umma, hasken gaskiya, Labarai sahihai da shirye shiryen al’umma.

Yadda Daliban Makarantar Islamiyya ta Matrix International Academy da ke Gombe s**a gudanar da bikin cika shekaru 10 da ...
29/07/2026

Yadda Daliban Makarantar Islamiyya ta Matrix International Academy da ke Gombe s**a gudanar da bikin cika shekaru 10 da kafuwar makarantar.

An kammala taron horaswa na tsawon kwanaki uku da aka shirya domin ƙarfafa ƙwarewar shugabannin Hukumar Hisbah ta Jihar ...
29/07/2026

An kammala taron horaswa na tsawon kwanaki uku da aka shirya domin ƙarfafa ƙwarewar shugabannin Hukumar Hisbah ta Jihar Yobe, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Hukumar, Assoc.Prof Yahuza Hamza Abubakar.

An gudanar da taron ne domin inganta ayyukan gudanarwa da ƙarfafa ingancin aikin hukumar.

29/07/2026

Yadda Daliban Geidam da ke karatu a Jami’ar Yobe (YSU) s**a nuna al’adunsu a yayin taron gabatarwa na Ƙungiyar Daliban Geidam (GAISA) reshen Jami’ar Yobe.

Taron ya kasance wata dama ta haɗa kan ɗalibai tare da nuna kyawawan al’adun Geidam.

29/07/2026

Yadda Daliban Geidam da ke karatu a Jami’ar Yobe (YSU) s**a nuna al’adunsu a yayin taron gabatarwa na Ƙungiyar Daliban Geidam (GAISA) reshen Jami’ar Yobe.

Taron ya kasance wata dama ta haɗa kan ɗalibai tare da nuna kyawawan al’adun Geidam.

Ƙabarin Sayyida Halimatus Sa'adiyya Radiyallahu Ta'ala Anha Wacce Ta Raini Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam, Ann...
25/07/2026

Ƙabarin Sayyida Halimatus Sa'adiyya Radiyallahu Ta'ala Anha Wacce Ta Raini Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam, Annabi Muhammad Ya Kasance Yana Girmamata Sosai Domin Duk Lokacin Data Ziyarce Shi Yakan Tashi Ya Tarbeta Sannan Ya Shimfiɗa Mata Mayafinsa Mai Tsarki Ta Zauna Akansa.

Ya Allah Ka Bamu Albarkacin Sayyida Halimatus Sa'adiyya Radiyallahu Ta'ala Anha Ka Ƙara Mana Ƙaunar Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam
please following 👉 YMC Hausa

23/07/2026
Jami'an Hukumar Alhazai ta Jihar Yobe sun kai ziyarar wayar da kai da fadakarwa ga masu ruwa da tsaki kan harkokin aikin...
23/07/2026

Jami'an Hukumar Alhazai ta Jihar Yobe sun kai ziyarar wayar da kai da fadakarwa ga masu ruwa da tsaki kan harkokin aikin Hajji a ƙananan hukumomin Geidam da Yunusari, a wani ɓangare na shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2027.

A yayin ziyarar, jami'an hukumar sun yi bayani kan muhimmancin fara shirin aikin Hajji da wuri, tare da ƙarfafa masu niyyar zuwa Hajji da su gaggauta kammala rajistarsu.

Hukumar ta kuma sanar da cewa ranar 25 ga Satumba, 2026, ita ce wa'adin ƙarshe na rajistar maniyyatan Hajjin 2027. Haka kuma, an buƙaci masu niyyar zuwa Hajji su biya mafi ƙarancin kuɗin ajiya na Naira miliyan 7.5 (₦7,500,000) kafin Hukumar Alhazji ta Ƙasa (NAHCON) ta bayyana kuɗin ƙarshe na kuɗin Hajjin shekarar 2027.

Jami'an hukumar sun ce fara biyan kuɗin da wuri zai taimaka wajen sauƙaƙa shirye-shiryen tafiyar maniyyata da kuma tabbatar da an kammala duk wasu matakan da ake buƙata kafin lokacin aikin Hajjin.

Rokon Ga Gwamnan Jihar Kano Kan Nada PS Ahmad Tijjani Abdullahi Cikin Majalisar Zartarwar Jihar KanoDaga Jabiru Hassan, ...
22/07/2026

Rokon Ga Gwamnan Jihar Kano Kan Nada PS Ahmad Tijjani Abdullahi Cikin Majalisar Zartarwar Jihar Kano

Daga Jabiru Hassan, Kano

Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf
Gwamnan Jihar Kano
Gidan Gwamnati, Kano.
Da kuma
Dr. Abdullahi Umar Ganduje, CON
Tsohon Gwamnan Jihar Kano
Tsohon Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa.
Mai Girma Ku,
Mu, abokai, 'yan uwa, masoya da kuma al'ummar Jihar Kano masu fatan alheri, muna miƙa wannan roƙo cikin girmamawa, domin neman a yi la'akari da Malam Ahmad Tijjani Abdullahi (Ph.D na kan gudana) wajen ba shi muƙami a cikin Majalisar Zartarwar Jihar Kano.
Malam Ahmad Tijjani ɗan asalin Jihar Kano ne, an haife shi a shekarar 1966 a garin Ganduje, ƙaramar hukumar Dawakin Tofa. Yana da sama da shekaru 34 na aiki na gaskiya da nagarta wajen hidimtawa jiharsa da ƙasarsa.

Shi ƙwararren malami ne kuma gogaggen jami'in gudanarwa. Ya samu Digirin Babbar Kwaleji (Master's Degree) a fannin Guidance and Counselling daga Jami'ar Bayero Kano (BUK) a shekarar 2025, kuma a halin yanzu yana karatun Digirin Digirgir (Ph.D) a wannan fanni a jami'ar.
Haka kuma yana da:
Digirin B.Sc. Mathematics Education daga Jami'ar Abuja.
PGDE daga Jami'ar Bayero Kano.
NCE daga Jami'ar Ahmadu Bello (ABU).

Aikin gwamnati da na ilimi da ya yi ya nuna jajircewa da ƙwarewa. Ya fara aiki a matsayin malamin lissafi, sannan ya yi aiki a makarantu daban-daban na gwamnati da masu zaman kansu a Kano, Legas da Abuja. Daga bisani ya zama Mataimakin Shugaban Makaranta (Vice Principal) sannan Administrative Officer a Muslim Community Centre, Abuja.
Ya kuma yi aiki a National Commission for Mass Literacy, kafin daga bisani a naɗa shi Sakataren Zartarwa na Hukumar Kimiyya da Makarantun Fasaha ta Jihar Kano (2015–2023).
Saboda ƙwazon aikinsa da nagartarsa, an ɗaga shi zuwa matsayin Permanent Secretary a shekarar 2023. Ya yi aiki a Ma'aikatar Ilimi sannan a Ofishin Shugaban Ma'aikatan Gwamnatin Jihar Kano, kafin ya yi ritaya a ranar 31 ga Agustan 2024.

A halin yanzu yana aiki a matsayin Mataimakin Babban Manajan Tsare-tsare (Deputy General Manager – Planning) a Federal Airports Authority of Nigeria (FAAN), Abuja.
A duk tsawon aikinsa, an san shi da ƙwazo, gaskiya, ƙwarewa da jajircewa wajen gudanar da ayyukan gwamnati. Yana da zurfin ilimi game da tsarin mulki da gudanar da gwamnati, tare da himma wajen bunƙasa ilimi, matasa da hidimar jama'a.

Ya Mai Girma Gwamna, yayin da gwamnatinku ke aiwatar da manufar "Kano First Agenda" tare da daidaita ta da "Renewed Hope Agenda" na Shugaban Ƙasa, muna da tabbacin cewa gogewa da ƙwarewar Malam Ahmad Tijjani a fannonin ilimi, gudanarwa da tsara manufofi za su kasance babban ƙari ga gwamnatin Jihar Kano.

Haka kuma, abin a yaba ne cewa Malam Ahmad Tijjani ya taɓa neman takarar Majalisar Dokokin Jihar Kano a ƙarƙashin jam'iyyar APC. Sai dai saboda haɗin kai da maslahar jam'iyya, ya janye takararsa domin bai wa wani ɗan takara dama. Har ila yau, ya roƙi magoya bayansa da su amince da wannan mataki tare da ci gaba da mara wa jam'iyyar baya.
Wannan sadaukarwa da biyayyarsa ga jam'iyya na nuna kishinsa da sanya muradun jama'a a gaba.

Saboda haka, cikin girmamawa muna roƙon Mai Girma Gwamna da ya yi la'akari da naɗa Malam Ahmad Tijjani Abdullahi a cikin gwamnatin Jihar Kano ko kuma duk wani muƙami da ya dace.
Muna da cikakken yaƙini cewa zai gudanar da duk wani nauyi da za a ɗora masa cikin gaskiya, ƙwarewa da nagarta, tare da kawo ci gaba ga wannan gwamnati.
Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ba ku hikima da shiriya a dukkan shawarwarinku domin ci gaban Jihar Kano.
Allah Ya albarkaci Jihar Kano.
Allah Ya albarkaci Tarayyar Najeriya.
Wanda s**a sanya hannu:
A madadin abokai, 'yan uwa da masu fatan alheri na Malam Ahmad Tijjani Abdullahi.

Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta k**a wasu mutane biyar da ake zargi da damfarar wani ɗan kasuwa ta hanyar amfani da s...
22/07/2026

Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta k**a wasu mutane biyar da ake zargi da damfarar wani ɗan kasuwa ta hanyar amfani da saƙon ƙarya na tura kuɗi, tare da kwato wasu kuɗaɗen ƙasashen waje da ake zargin na bogi ne.

Kakakin rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Damaturu, inda ya ce waɗanda ake zargin sun haɗa kai wajen karɓar buhunan taki guda 10 da darajarsu ta kai Naira 488,000, bayan sun yaudari mai kayan da cewa sun tura masa kuɗi ta banki.

Ya ce wanda abin ya shafa ya kai rahoto hedikwatar ’yan sanda ta Potiskum ranar Asabar, inda ya bayyana cewa waɗanda ake zargin sun nuna masa saƙon ƙarya na tura kuɗi kafin su karɓi takin.

Rundunar ta ce jami’anta sun yi amfani da bayanan sirri wajen cafke mutanen kafin su samu damar sayar da kayan. Daga bisani, binciken da aka gudanar a ɗakin otal ɗin da ake zargin suke zaune a Damaturu ya kai ga kwato takardun dala 100 guda 10 da ake zargin na bogi ne, da kuma takardun kuɗin Somaliya na 50,000 guda 56, tare da wasu abubuwa da ake zargin na tsafi ne.

’Yan sandan sun ce suna ci gaba da bincike domin gano tushen kuɗaɗen da ake zargin na bogi ne, da kuma tabbatar da ko ƙungiyar tana da hannu wajen ƙera ko yaɗa kuɗaɗen bogi da kuma gano sauran mambobinta.

Kwamishinan ’yan sandan Jihar Yobe, Usman Kamfani Jibrin, ya shawarci ’yan kasuwa da jama’a da su tabbatar da sahihancin duk wani kuɗin da aka tura ta banki kafin su miƙa kaya, tare da yin taka-tsantsan wajen mu’amala da kuɗaɗen ƙasashen waje.

An gano maganin karfin maza a dakin Otal na magidanci mai shekaru 60 da ya mutu, a sa'ilin da ya shiga da budurawa 'yar ...
22/07/2026

An gano maganin karfin maza a dakin Otal na magidanci mai shekaru 60 da ya mutu, a sa'ilin da ya shiga da budurawa 'yar shekara 20 a Jigawa

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Jigawa ta fara bincike kan rasuwar wani mutum mai shekaru 60 da ta faru a wani otal da ke birnin Dutse.

A cewar 'yan sanda, mamacin ya shiga otal ɗin tare da wata budurwa mai shekaru 20, bayan ya nemi a kawo masa abinci, ba zato ba tsammani ya fara fama da matsananciyar wahalar numfashi.

An garzaya da shi zuwa Babban Asibitin Dutse, amma likitoci sun tabbatar da rasuwarsa bayan an kai shi.

Jami'an bincike sun killace ɗakin da lamarin ya faru, inda s**a tattara abinci, abubuwan sha da kuma wani sinadari da ake zargin na ƙara ƙarfin jima'i ne domin gudanar da binciken kimiyya.

An miƙa gawar mamacin ga iyalansa domin yi masa jana'iza, yayin da budurwar da ke tare da shi ke ci gaba da ba da haɗin kai ga jami'an bincike.

'Yan sandan Jigawa sun ce bincike na ci gaba, tare da kira ga jama'a da su guji yaɗa jita-jita ko yanke hukunci kafin sak**akon bincike ya fito.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when YMC Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to YMC Hausa:

Shortcuts

Share