YOBE 360 TV

YOBE 360 TV Gidan Tv/Radio Wanda zai dunga watsa shirye shiryen sa cikin awa 24

Zakaran Duniya A Gasar Turanci Nafisa ta Ziyarci Farfesa Isa Ali Pantami, CON (Majidadin Daular Usmaniyya)!Jiya, daliba ...
14/09/2025

Zakaran Duniya A Gasar Turanci Nafisa ta Ziyarci Farfesa Isa Ali Pantami, CON (Majidadin Daular Usmaniyya)!

Jiya, daliba mai shekaru 17, Nafisa Abdullah Aminu daga Jihar Yobe, ta kai ziyara wurin Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami domin nuna godiya kan jagoranci da shawarwari da yake bata tare da gabatar masa da kyautar zakaran duniya da ta samu a bara.

Wannan gagarumin lambar yabo ta samu ne bayan ta bayyana a matsayin mace ta farko daga Najeriya da ta fi kowa iya harshen Turanci a duniya a gasar TeenEagle Global Finals 2025 da aka gudanar a birnin London, ƙasar Birtaniya.

Nafisa, dalibar Nigerian Tulip International College (NTIC), ta samu nasara ne a tsakanin fiye da ‘yan takara 20,000 daga ƙasashe 69 – ciki har da ƙasashen da harshen Turanci shi ne na asali – abin da ya sa ta dauki kambun zakara. Wannan nasara ta zama shaida cewa idan ɗaliban Najeriya s**a samu dama, shawarwari, da kuma goyon baya mai kyau, suna da cikakken ƙarfin iya ficewa a duniya.

A lokacin ziyarar, Nafisa ta bayyana godiyarta ga Farfesa Pantami saboda goyon bayan da yake bata a fannin ilimi da addini. Ta kuma roƙi ci gaba da jagoranci da shawarwari a gaba.

Farfesa Pantami ya gode wa iyaye, masu kula da ita, da malamai bisa kawo Nafisa ofishinsa. A wurin, ya bata shawarwari masu daraja don samun nasarar rayuwa, ya kuma kyauta mata sabuwar kwamfutar HP mai ƙarfi tare da littattafai na ƙarin karatu da shawarwari.

Iyalan Pantami sun ƙarfafa Nafisa da ta ci gaba da tafiya a harkar ilimi har sai ta kammala digiri, ta samu digirin digirgir (master’s), da kuma PhD. Sun jaddada cewa wannan zamani yana da buƙatar fitattun mata a ilimi fiye da da.

A ƙarshe, Farfesa Pantami ya amince da roƙonta na ci gaba da kasancewa cikin jagoranci da shawarwarinsa, tare da ƙarin tsare-tsare na tallafi.

13/09/2025
DA DUMI DUMI: Ni Da kaina Zan Dauki Ragamar Shigar Da Ƙara Kotu, Duk Wani Musulmi Da Yakara Cewa Wani Arne A Ɗaureshi Ko...
11/09/2025

DA DUMI DUMI: Ni Da kaina Zan Dauki Ragamar Shigar Da Ƙara Kotu, Duk Wani Musulmi Da Yakara Cewa Wani Arne A Ɗaureshi Ko Waye, Bazamu Bari Aci Gaba Da Raba Mana Kan Kasa Da Sunan Musulunci Ba, Wai Kawai Don Neman Fitina Da Rashin Son Hadin Kai Irin Na Mutanen Mu Sai Kaji Wani Kalli Abokin Zamansa Kirista Yace Masa Arne, To Ko Waye Mutum Zamu Shigar Da Kara Sai An Ɗaureshi~ Sheikh Nuru Khalid.

Labari Da Gaskiya ✍️

An kammala Zagayen Takutaha a Geidam A yau Alhamis 11/9/2025 aka gudanar da zagayen Takutahar Maulidi a Garin Geidam dak...
11/09/2025

An kammala Zagayen Takutaha a Geidam

A yau Alhamis 11/9/2025 aka gudanar da zagayen Takutahar Maulidi a Garin Geidam dake jihar Yobe wakilin mu ya sheda mana cewa kimanin Makarantu dari da hamsin na Geidam da wajan Geidam s**a halarci zagayen a yau

Hon. Yusuf Adamu Gagdi yayin da ya kai ziyara gidan marayun da amaryarsa Layla Ali Othman ta gina a Abuja domin ganawa d...
10/09/2025

Hon. Yusuf Adamu Gagdi yayin da ya kai ziyara gidan marayun da amaryarsa Layla Ali Othman ta gina a Abuja domin ganawa da yara marayun da ke ciki.

Abin Yabawa: Sama da Mata 200 a ƙaramar hukumar Akko sun amfana da kayan tallafi daga Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma...
10/09/2025

Abin Yabawa: Sama da Mata 200 a ƙaramar hukumar Akko sun amfana da kayan tallafi daga Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar, Hon. Habibu Hassan Kumo (Gatan Akko)

Mata da dama daga sassan ƙaramar hukumar Akko sun karɓi kayan tallafi da mataimakin shugaban ƙaramar hukumar, Hon Habibu Hassan Kumo, ya bayar.

A wajen taron, shugaban ƙaramar hukumar Akko, Alhaji Muhammad Dalladi Adamu, wanda shi ne babban bako na musamman, ya yaba da wannan shiri na mataimakinsa, inda ya bayyana shi a matsayin babbar gudummawa wajen tallafawa mata a yankin. Ya kuma nuna cewa gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ta samar da tallafi iri-iri domin inganta rayuwar jama’a tare da rage musu ƙuncin tattalin arziki.

Alhaji Dalladi ya kuma gode wa Hukumar Cigaban Arewa maso Gabas (NEDC) bisa samar da kayan da aka raba. Yayin da yake jaddada muhimmancin rawar da mata s**a taka a zaɓen baya, ya yi kira gare su da su ci gaba da goyon bayan gwamnati tare da tabbatar da sun karɓi Katin Zaɓe na Dindindinsu (PVC) domin shirye-shiryen manyan zaɓe masu zuwa.

A nasa jawabin, mataimakin shugaban ƙaramar hukumar, Alhaji Habibu Hassan, wanda Alhaji Baba Chiroma Dawa ya wakilta, ya bayyana cewa wannan tallafi ya samu ne da goyon baya da kuma ƙarfafawar Gwamna Inuwa Yahaya. Ya shawarci waɗanda s**a amfana da su yi amfani da kayan yadda ya dace, yana mai jaddada cewa an ba su ne domin tallafa musu wajen kula da iyalansu da kuma bunƙasa harkokin kasuwancinsu.

Sauran masu jawabi a wurin sun haɗa da Mai taimakawa Gwamna ta musamman, Hajiya Amina Abubakar; kansila mai wakiltar Kumo Center, Hajiya Aisha Muhammad Buba; da kuma Mai taimakawa Shugaban ƙaramar hukuma ta musamman, Hajiya Ladi. Dukkansu sun nuna godiya ga mataimakin shugaban bisa wannan tallafi, inda s**a ce kayan za su taimaka matuƙa wajen inganta rayuwar mata da iyalai.

Wasu daga cikin waɗanda s**a amfana sun gode wa mataimakin shugaban ƙaramar hukumar, Hon. Habibu Hassan Kumo, bisa wannan kyakkyawan taimako da yayi musu.

10/09/2025

Ina al'ummar Jihar Yobe jiha mai albarka ga taku sabuwa YOBE 360 TV domin samun Ingantattun Labarai nagida Jihar Yobe dama na duniya Baki Daya kasance da tashar Zamani

28/08/2025

Zamu dawo da shirye shiryen mu nan kusa in sha Allah

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when YOBE 360 TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to YOBE 360 TV:

Share