29/05/2026
Gwamnatin mulkin sojin Burkina Faso ƙarƙashin jagorancin Ibrahim Traoré ta rufe babban masallacin Sunni da ke birnin Ouagadougou bayan k**a wasu mabiyan wani malamin addini da s**a gudanar da zanga-zanga.
Mahukunta sun ce an ɗauki matakin ne domin kauce wa rikici da tarzoma bayan masu zanga-zangar sun nemi a saki malamin da aka tsare. Rahotanni sun ce an k**a kusan mutum 100 a lamarin.