HIMMA TV

HIMMA TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from HIMMA TV, Kano.

Himma TV Mun zo don gina zuciya, farfaɗo da tunani, da kunna hasken gaskiya a cikin duhun rayuwa—batare da bangaranci ba.Himma ba ta ga rago—ta ga gaskiya, ta tsaya a kai.Muryarmu tana motsa zuciya, tana ƙarfafa gwiwa, tana ba da murya ga marasa murya.

Kai Tsaye dubbanin mutane Daga Wajen Taron Maulidi a Bauchi, Shekaran Farko Kenan Da Za'ayi Maulidi Babu Sheikh Dahiru U...
26/08/2026

Kai Tsaye dubbanin mutane Daga Wajen Taron Maulidi a Bauchi, Shekaran Farko Kenan Da Za'ayi Maulidi Babu Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Kai tsaye wasu daga cikin hotunan Zagayen Mauludi.Ghana Accra hosts  Maulud Walk of Pride 2K26🤍✨
25/08/2026

Kai tsaye wasu daga cikin hotunan Zagayen Mauludi.
Ghana Accra hosts Maulud Walk of Pride 2K26🤍✨

Allah Ya yi wa fitaccen malami a Kano, Malam Salisu, wanda aka fi sani da “Dan Kargo,” rasuwa.Muna roƙon Allah Ya gafart...
25/08/2026

Allah Ya yi wa fitaccen malami a Kano, Malam Salisu, wanda aka fi sani da “Dan Kargo,” rasuwa.

Muna roƙon Allah Ya gafarta masa, Ya jiƙansa da rahama, Ya sa Aljannatul Firdausi ce makomarsa. Allah Ya ba iyalansa, ɗalibansa da sauran al’ummar Musulmi haƙurin jure wannan babban rashi. Amin.

Annobar Ciwon Koda na ci gaba da bazuwa kamar ruwan dare, musamman tsakanin ’yan asalin Gashuwa da ke Jihar Yobe. Harda ...
25/08/2026

Annobar Ciwon Koda na ci gaba da bazuwa kamar ruwan dare, musamman tsakanin ’yan asalin Gashuwa da ke Jihar Yobe. Harda ma wasu yan kunan Kazaure dake Jahar Jigawa.


🌙✨ BARKA DA EID MAULUD MAI ALBARKA! ﷺA yau, muna taya daukacin al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen...
25/08/2026

🌙✨ BARKA DA EID MAULUD MAI ALBARKA! ﷺ

A yau, muna taya daukacin al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta, Annabi Muhammad ﷺ.

Allah Ya sa mu kasance cikin waɗanda suke ƙaunarsa, suke bin sunnarsa, kuma suke koyi da kyawawan halayensa. 🤲💚

DAGA HIMMA TV 📺
Muna yi muku fatan alheri, zaman lafiya da albarka a wannan rana mai daraja.

👇 Tambayar mu gare ku:
Wane hali ko koyarwa daga Annabi Muhammad ﷺ kuke ganin ya kamata Musulmi su fi mayar da hankali a kai a wannan zamani?

✍️ Ku rubuta amsar ku a comment, sannan ku share wannan saƙo domin ya isa ga sauran ‘yan uwa Musulmi.

Ina mutanen Doguwa da Tudun Wada Falle Na wace?
25/08/2026

Ina mutanen Doguwa da Tudun Wada Falle Na wace?

NELFUND TA YABAWA SHUGABA TINUBU KAN DOREWAR TALLAFIN LAMUNIN DALIBAIAsusun Ba da Lamunin Ilimi na Najeriya (NELFUND) ya...
24/08/2026

NELFUND TA YABAWA SHUGABA TINUBU KAN DOREWAR TALLAFIN LAMUNIN DALIBAI

Asusun Ba da Lamunin Ilimi na Najeriya (NELFUND) ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa ƙudirin tabbatar da dorewar tsarin ba da lamunin karatu ga ɗaliban Najeriya.

NELFUND ta ce Shugaban Ƙasar ya bayar da umarnin karkatar da kuɗaden da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa da sauran Laifukan Tattalin Arziƙi (EFCC) ta kwato zuwa asusun NELFUND, domin ƙarfafa shirin ba da lamunin karatu ga ɗalibai.

A cikin wata sanarwa da Daraktar Sadarwa ta NELFUND, Mrs Oseyemi Oluwatuyi, ta fitar a ranar 19 ga Agusta, 2026, asusun ya kuma yi maraba da amincewar Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) kan tura ribar da ba a karɓa ba daga Capital Market Trust Fund da Dormant Account Trust Fund zuwa NELFUND.

NELFUND ta ce waɗannan matakai za su taimaka wajen samar da ingantaccen tushen kuɗaɗen da za su ci gaba da tallafa wa shirin lamunin ɗalibai, musamman yayin da yawan masu neman tallafin ke ƙaruwa.

A cewar asusun, zuwa watan Agustan 2026, NELFUND ta riga ta fitar da sama da Naira biliyan 322 ga ɗalibai, daga cikin sama da miliyan 1.6 na buƙatun lamunin karatu da aka gabatar.

Shugaban Hukumar Gudanarwar NELFUND, Jim Ovia, ya bayyana godiyarsa ga Shugaba Tinubu bisa ci gaba da goyon baya da amincewar da yake bai wa asusun. Ya ce hakan ya ƙara ƙarfafa ƙudirin gwamnati na tabbatar da cewa rashin kuɗi bai zama dalilin hana wani ɗan Najeriya samun ilimi mai zurfi ba.

Shi ma Manajan Daraktan NELFUND, Akintunde Sawyer, ya ce sabon ƙudurin Shugaban Ƙasar ya nuna irin muhimmancin da gwamnati ke bai wa ilimi, tare da ƙoƙarin gina tsarin ba da lamunin karatu mai ɗorewa.

Sawyer ya tabbatar da cewa NELFUND za ta ci gaba da amfani da dukkan kuɗaɗen da aka damƙa mata cikin gaskiya da riƙon amana, domin amfanin ɗaliban Najeriya.

NELFUND ta ce sabon tsarin samar da kuɗaɗen zai ƙara wa Gwamnatin Tarayya ƙarfin faɗaɗa shirin, tare da kai lamunin karatu ga ƙarin ɗaliban Najeriya da s**a cancanta.

Adam Muhammad Mukhtar ya bayyana haka ne a shafinsa na sada zumunta, inda ya yi jan hankali tare da tunatar da ’yan ƙasa...
24/08/2026

Adam Muhammad Mukhtar
ya bayyana haka ne a shafinsa na sada zumunta, inda ya yi jan hankali tare da tunatar da ’yan ƙasa na Najeriya, duba da ƙarato­war zaɓe.

Ina Mamakin Naga Yadda Wasu Mutane Ke Wa Wadansu Mutane Har Na Kusa Da Su Hassada Da Bakin Ciki Don Sun Samu Nasarar Ray...
24/08/2026

Ina Mamakin Naga Yadda Wasu Mutane Ke Wa Wadansu Mutane Har Na Kusa Da Su Hassada Da Bakin Ciki Don Sun Samu Nasarar Rayuwa! Why?

Kada ka yarda a saɓa wa Allah da Manzonsa ﷺ  da kai saboda ranar zagayowar haihuwar. (Takutaha) Ka tuna cewa biyayya ga ...
24/08/2026

Kada ka yarda a saɓa wa Allah da Manzonsa ﷺ da kai saboda ranar zagayowar haihuwar. (Takutaha) Ka tuna cewa biyayya ga Allah da Manzonsa ita ce mafi muhimmanci.”

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HIMMA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share