VON Hausa

VON Hausa Manufa Da Tsari Tsage Gaskiya Komai Ɗa Cinta Shine Taken Mu VON Hausa Muryar Najeriya.

“Muna bibiyar wannan batu sosai kuma muna kira ga dukkan ɓangarorin da abin ya shafa su bi ƙa’idojin dokokin ƙasa da ƙas...
07/11/2025

“Muna bibiyar wannan batu sosai kuma muna kira ga dukkan ɓangarorin da abin ya shafa su bi ƙa’idojin dokokin ƙasa da ƙasa a tsanaki,” in ji mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Rasha, Maria Zakharova a ranar Jumma’a

HOTUNA: Yadda aka gudanar da sallar Juma'a a Masallacin Harami na Saudiyya
07/11/2025

HOTUNA: Yadda aka gudanar da sallar Juma'a a Masallacin Harami na Saudiyya

Bama-bamai da harsasai ba su san addini ko ƙabila ba – ShettimaMataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ce kalubale...
07/11/2025

Bama-bamai da harsasai ba su san addini ko ƙabila ba – Shettima

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ce kalubalen tsaro da Najeriya ke fuskanta na buƙatar haɗin kai tsakanin ’yan ƙasa gaba ɗaya.

Ya bayyana cewa hare-haren ta’addanci da tashin bam ba su bambanta tsakanin Musulmi ko Kirista, ko kuma tsakanin mai arziki da talaka.

Shettima ya jaddada cewa lokaci ya yi da ’yan Najeriya za su tashi tsaye su haɗa kai domin kawo ƙarshen ta’addanci da rikice-rikice a ƙasar.

“Tsaro na buƙatar haɗin kai, domin harsasai da bama-bamai ba su san addini ko ƙabila ba.”

Da Dumi Dumi: Majalisar dattawan Nijeriya za ta haramta barasar leda daga karshen wannan shekarar
07/11/2025

Da Dumi Dumi: Majalisar dattawan Nijeriya za ta haramta barasar leda daga karshen wannan shekarar

Maganar gaskiyya ya kamata hankalin matasan mu yadawo kan Aikin Gadar mu, Sabo da Ita ce Babbar matsalar da ta dade Tana...
07/11/2025

Maganar gaskiyya ya kamata hankalin matasan mu yadawo kan Aikin Gadar mu, Sabo da Ita ce Babbar matsalar da ta dade Tana cimana Tuwo a Ƙwarya a Rogo ta Yamma - Comrade Mudanssir Abubakar

Ƙungiyar Nigeria Evangelical Fellowship (NEF) ta roƙi Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa wajen murƙushe ‘yan ...
06/11/2025

Ƙungiyar Nigeria Evangelical Fellowship (NEF) ta roƙi Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa wajen murƙushe ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga da sauran ƙungiyoyin tada zaune-tsaye da ke barazana ga zaman lafiya da haɗin kai a Najeriya.

Ƙungiyar ta fitar da wannan sanarwa ne bayan kammala taronta na cika shekaru 60 a Abuja, inda ta bayyana damuwa kan yadda ake ta kai hare-hare masu nasaba da addini da ƙabilanci a sassan ƙasar.

NEF ta kuma shawarci gwamnati da ta kare ‘yancin addini, ta dawo da mutanen da s**a rasa muhallansu, tare da magance matsalolin tattalin arziki da zamantakewa da ke haifar da rashin tsaro a ƙasar.

Matsalar Tsaro:Za mu Tsaurara kai hare-hare ta sama domin kakkaɓe ƴanbindiga.
06/11/2025

Matsalar Tsaro:Za mu Tsaurara kai hare-hare ta sama domin kakkaɓe ƴanbindiga.

Jakadan ƙasar China a Najeriya ya bayyana cewa ƙasarsu za ta ci gaba da ba da goyon baya ga Najeriya wajen yaƙi da ta’ad...
06/11/2025

Jakadan ƙasar China a Najeriya ya bayyana cewa ƙasarsu za ta ci gaba da ba da goyon baya ga Najeriya wajen yaƙi da ta’addanci da tabbatar da zaman lafiya a cikin gida.

Jakadan ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da Mai ba da shawara ga shugaban ƙasa kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, a yau bayan wani muhimmin taron dabarun tsaro da aka gudanar a Abuja.

A cewar jakadan, gwamnatin China za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwa da Najeriya musamman a fannin tsaro da tattalin arziki, domin ganin an cimma burin samar da dorewar zaman lafiya da cigaba mai ɗorewa.

Ya kuma jaddada cewa ƙasar su ba ta goyon bayan kowace ƙasa da ke tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wasu ƙasashe da sunan kare ‘yancin ɗan adam ko addini, tare da bayyana adawar su ga duk wata barazanar sanya takunkumi ba tare da hujja ba.

Da Dumi Dumi: Gwamnatin Kano za ta gina guraren Fakin na zamani don rage yawan haduran dake faruwa a Jihar.
06/11/2025

Da Dumi Dumi: Gwamnatin Kano za ta gina guraren Fakin na zamani don rage yawan haduran dake faruwa a Jihar.

Wasu da ba a san ko su waye ba sun fasa ofishin Shugaban Ƙaramar Hukumar Gaya ta jihar Kano, Hon. Mahmud Tajo Gaya, a da...
06/11/2025

Wasu da ba a san ko su waye ba sun fasa ofishin Shugaban Ƙaramar Hukumar Gaya ta jihar Kano, Hon. Mahmud Tajo Gaya, a daren Talata, inda s**a sace kayayyaki da na’urorin sola da ake amfani da su wajen gudanar da ayyukan yau da kullum.

Wannan na cikin sanarwar da mai taimaka wa shugaban kan harkokin yaɗa labarai, Comrade Naziru Mukhtar Gaya, ya fitar a ranar Laraba, 5 ga Nuwamba, 2025.

A cewarsa, hukumomin tsaro sun riga sun fara gudanar da bincike domin gano waɗanda ke da hannu a wannan aika-aika, tare da tabbatar da cewa za a gurfanar da su a gaban doka bayan an kammala bincike

Zaɓen 2027: Yadda wasu s**a fara gangamin kiraye-kirayen Tsohon shugaban kasa Dr. Goodluck Jonathan ya dawo ya ceto Naje...
06/11/2025

Zaɓen 2027: Yadda wasu s**a fara gangamin kiraye-kirayen Tsohon shugaban kasa Dr. Goodluck Jonathan ya dawo ya ceto Najeriya, Daga mulkin kangin Bauta da take cikin.

Kuna goyon bayan Goodluck ya sake tsayawa takara a 2027?

Sojojin Amurka sun kammala tsara irin farmakin da za su kawo wa Najeriya, sun mika shirin nasu domin samun amincewar gwa...
06/11/2025

Sojojin Amurka sun kammala tsara irin farmakin da za su kawo wa Najeriya, sun mika shirin nasu domin samun amincewar gwamnatin Trump

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when VON Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share