Arewa A Yau

Arewa A Yau Muradin Arewacin Najeriya da jama’arta ne a gaba.

YANZU-YANZU: Musulmi da Kirista Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya a AbujaMusulmi da mabiya addinin Kirista s...
13/08/2026

YANZU-YANZU: Musulmi da Kirista Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya a Abuja

Musulmi da mabiya addinin Kirista sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar zaman lafiya da fahimtar juna, domin karfafa zaman tare da mutunta juna a tsakanin al’ummomin addinai biyu.

An rattaba hannu kan yarjejeniyar ne a yayin wani babban taron kasa da kasa da aka gudanar a Abuja, wanda ya hada da kungiyar , tare da halartar manyan malamai da wakilan addinai daga kasashe daban-daban na Afirka da Turai.

Jagororin Musulmi da wakilan kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) sun sanya hannu kan yarjejeniyar, wadda ke da nufin tabbatar da zaman lafiya, fahimtar juna da mutunta addinan juna.

A cewar rahoton Jibwis Nigeria, yarjejeniyar ba ta nufin Musulmi da Kirista su hade addinai ko su zama mabiya addini guda ba. Maimakon haka, manufarta ita ce kusantar juna, fahimtar koyarwar addinin juna da kuma girmama abin da kowane bangare ya yi imani da shi.

A yayin taron, jagororin bangarorin biyu sun kawo hujjoji daga Alkur’ani da Baibul, inda s**a bayyana abubuwan da ke karfafa fahimtar juna da zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kirista.

Shawarwarin da aka cimma a taron za a mika su ga gwamnati domin duba hanyoyin da za a karfafa su, musamman wajen magance wasu al’adu da dabi’un da ke haddasa rashin fahimta da rikici tsakanin Musulmi da Kirista.

Haka kuma, an wallafa wani kundin da aka tsara domin ya zama abin koyi da jagora wajen taimakawa wajen dakile duk wata arangama, kiyayya ko rashin fahimta tsakanin bangarorin biyu.

Taron ya kuma jaddada cewa ba alheri ba ne Musulmi ya tsangwami Kirista, ko kuma Kirista ya tsangwami Musulmi, musamman ganin cewa dukkansu ‘yan kasa daya ne kuma suna zaune tare a kasa guda.

12/08/2026

Hon. Fahad Kabo, ya taya Sakataren karamar hukumar murnar sauke shi daga mukamin sakataren karamar hukumar Kabo da akayi, sak**akon nuna goyon baya ga Barau da Tinubu.

Ana zargin Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano, Hon. Lawan Najume Kabo, da hannu wajen k**a da tsare wani matash...
11/08/2026

Ana zargin Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano, Hon. Lawan Najume Kabo, da hannu wajen k**a da tsare wani matashi mai suna Aliyu Muhammad Haruna, wanda aka fi sani da Babagana, bisa zargin ya bayyana ra’ayinsa kan wasu batutuwan siyasa.

An bayyana hakan ne cikin wata takardar ƙorafi mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Agusta, 2026, wadda aka miƙa wa Sufeto-Janar na Rundunar ’Yan Sandan Najeriya a Hedikwatar ’Yan Sanda da ke Louis Edet House, Abuja.

Takardar ta ƙunshi ƙorafi kan k**awa da tsarewa ba bisa ka’idar doka ba, da kuma zargin amfani da ikon ’yan sanda ba daidai ba wajen k**a matashin.
‎A cikin ƙorafin, lauyoyin Aliyu Muhammad Haruna sun bayyana cewa:

“Mu ne lauyoyin Mr. Aliyu Muhammad Haruna (Babagana), kuma bisa umarninsa, mun rubuto wannan wasiƙa domin sanar da ku halin da ya dabaibaye k**awa da tsare shi da jami’an ’yan sanda da ke aiki a Sashen ’Yan Sandan Kabo.”

A cewar takardar, lauyoyin sun yi zargin cewa k**awa da tsare Babagana ya faru ne bisa umarni ko sa hannun Shugaban Karamar Hukumar Kabo, Hon. Lawan Najume Kabo.

‎LauyoyinLauyoyin sun kuma nemi a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa domin gano halaccin k**awa da tsarewar, yanayin da ya kai ga jami’an ’yan sanda ɗaukar matakin, da kuma rawar da Shugaban Karamar Hukumar ya taka a cikin lamarin.

Takardar ta bayyana Babagana a matsayin ɗan Najeriya, ɗalibi kuma ɗan asalin Jihar Kano, tare da cewa, bisa bayanan lauyoyinsa, ba shi da wani tarihin aikata laifi da ya shafi wannan ƙorafi.


A ranar 3 ga Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 1:00 na rana, jami’an ’yan sanda da ke aiki a Sashen ’Yan Sandan Kabo sun je gidan Babagana da ke Gidan Alh. Haruna, Kabo, inda s**a k**a shi tare da kai shi ofishin ’yan sanda.

A cewar Babagana, jami’an sun ɗauki matakin ne bisa umarni ko sa hannun Hon. Lawan Najume Kabo, Shugaban Karamar Hukumar Kabo.

Takardar ta ƙara da cewa Babagana ya taɓa samun rashin jituwa da Shugaban Karamar Hukumar kan wasu batutuwan siyasa da kuma yadda ake gudanar da harkokin ƙaramar hukumar.

Kafin k**a shi, Babagana ya kasance yana bayyana ra’ayoyinsa da rashin amincewarsa da wasu manufofi ko matakan gudanarwa da s**a shafi Shugaban Karamar Hukumar.

‎A halin yanzu, lauyoyin matashin suna neman a gudanar da bincike domin tabbatar da ainihin dalilin k**awa da tsare shi, da kuma gano ko an yi amfani da ikon ’yan sanda ba bisa ka’ida ba.

TIRKASHI: K**a Masu Sukar Gwamnati Ba Zai Ba Ka Tikitin Komawa Gidan Gwamnatin Katsina Ba — Zahraddeen Sirajo Abbas ga D...
06/08/2026

TIRKASHI: K**a Masu Sukar Gwamnati Ba Zai Ba Ka Tikitin Komawa Gidan Gwamnatin Katsina Ba — Zahraddeen Sirajo Abbas ga Dikko Radda

Ɗan jarida Zahraddeen Sirajo Abbas ya zargi gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dikko Umar Radda da rashin jure s**a da kuma abin da ya bayyana a matsayin takaita 'yancin faɗin albarkacin baki.

A cewarsa, duk lokacin da aka yi s**a ko aka nuna rashin gamsuwa da wasu matakan gwamnati, sai a ce an k**a mai s**ar maimakon a saurari korafin da ya gabatar.

"Ban taɓa ganin gwamnatin da ba ta jure adawa ba irin gwamnatin Jihar Katsina ta Dikko Radda. Da an taɓa ku kaɗan, sai ku sa a k**a mutum. Mene ne laifin ɗan ƙasa ya faɗi ra'ayinsa kan yadda ake gudanar da mulki?" in ji Zahraddeen.

Ya kuma yi tambaya ga gwamnatin da kuma al'ummar jihar, yana mai cewa idan har gwamnati ta ci gaba da k**a masu s**a maimakon saurar ra'ayoyinsu, hakan na iya haifar da tambayoyi game da yadda jama'a za su mayar da martani a zaɓe.

"Idan kuka ci gaba da k**a 'yan jihar da s**a bayyana ra'ayinsu, shin wa kuke sa ran zai zaɓe ku a lokacin zaɓe? Katsinawa ne za su yanke hukunci ta hanyar ƙuri'arsu," in ji shi.

Zahraddeen ya yi kira da a mutunta 'yancin faɗin albarkacin baki da kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada, yana mai cewa gwamnati ta fi amfana idan ta saurari korafe-korafe da shawarwari daga al'umma maimakon ɗaukar matakin k**a masu s**a.

TIRKASHI: "Ba Mu Son Musulmi a Kujerar Majalisar Wakilai, Kiristoci Muke So" — Zargin Abin da Shugaban NDC Ya Faɗawa Hon...
06/08/2026

TIRKASHI: "Ba Mu Son Musulmi a Kujerar Majalisar Wakilai, Kiristoci Muke So" — Zargin Abin da Shugaban NDC Ya Faɗawa Hon. Zahraddeen Bayan Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwani

Ɗan takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai neman wakiltar mazabar Keffi/Karu/Kokona a Jihar Nasarawa ƙarƙashin jam'iyyar New Democratic Congress (NDC), Zahradeen Ahmad Zangina, ya zargi jam'iyyarsa da nuna wariyar addini, inda ya ce an cire sunansa daga cikin jerin 'yan takarar jam'iyyar duk da ikirarinsa na cewa shi ne ya lashe zaɓen fidda gwani.

A cikin wata sanarwar manema labarai da ya fitar, Zangina ya bayyana cewa shugaban jam'iyyar NDC na Jihar Nasarawa, Dogo Shama, ne ya sanar da shi cewa shi ne ya yi nasara a zaɓen fidda gwani na kujerar Majalisar Wakilai.

Sai dai, ya ce bayan wasu kwanaki ya samu labarin cewa an cire sunansa daga jerin sunayen 'yan takarar jam'iyyar.

A cewarsa, Mataimakin Shugaban jam'iyyar na shiyyar Arewa ta Tsakiya, Barnabas Ijisi Dankunama, ya shaida masa cewa ba sa son Musulmi ya zama ɗan takarar jam'iyyar a wannan kujera, domin suna son dukkan 'yan takarar Majalisar Wakilai na jam'iyyar a Jihar Nasarawa su kasance Kiristoci.

Zangina ya ce ya yi watsi da duk wani nau'in wariya bisa addini, yana mai jaddada cewa Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya bai wa kowane ɗan ƙasa damar samun daidaito da adalci ba tare da la'akari da addini ko ƙabila ba.

Ya kuma yi ikirarin cewa yana da bidiyon tattaunawarsa da Barnabas Ijisi Dankunama cikin harshen Hausa, wanda ya ce na goyon bayan zarge-zargen da yake yi.

Dangane da ƙoƙarinsa na neman mafita, Zangina ya ce ya gana da Shugaban Jam'iyyar NDC na ƙasa, Cleopas Moses, wanda, a cewarsa, ya bayyana masa cewa ba zai iya sauya matakin da aka ɗauka ba, tare da ba shi shawarar ya tattauna da shugaban jam'iyyar.

Haka kuma, ya ce ya gana da shugaban jam'iyyar, Saraki Dickson, inda ya gabatar masa da ƙorafinsa. A cewarsa, bayan sauraron bayanansa, shugaban jam'iyyar ya ba shi shawarar ya nemi hakkinsa ta hanyar kotu.

Har ila yau, Zangina ya bayyana cewa ya kai ƙorafinsa ga ɗan takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa na jam'iyyar, Rabiu Musa Kwankwaso, domin neman shiga tsakani, amma har zuwa lokacin fitar da wannan sanarwa bai samu wata mafita ba.

Ya yi gargaɗin cewa idan aka bar lamarin ba tare da warware shi ba, hakan na iya kawo cikas ga dimokuraɗiyyar cikin gida ta jam'iyyar tare da rage amincewar jama'a da tsarin zaɓe.

Saboda haka, ya yi kira ga shugabannin jam'iyyar NDC da su sake duba lamarin tare da tabbatar da adalci. Haka kuma, ya roƙi INEC, ƙungiyoyin farar hula, shugabannin addinai da daukacin 'yan Najeriya masu kishin adalci da su sanya ido kan lamarin domin tabbatar da an yi masa adalci.

04/08/2026

DA DUMI-DUMI: Fiye da Mutum 1,500 Sun Amfana da Takin Zamani daga Gidauniyar Tsohon Ɗan Takarar Majalisar Kabo, Fahad Dan Kabo

TIRKASHI: Da Ace Akwai Abin Kushewa a Mulkin Tinubu, Ni Ne Na Farko Cikin Malaman Musulunci da Zan Ƙalubalance Shi — She...
04/08/2026

TIRKASHI: Da Ace Akwai Abin Kushewa a Mulkin Tinubu, Ni Ne Na Farko Cikin Malaman Musulunci da Zan Ƙalubalance Shi — Sheikh Isa Ali Pamtami

YANZU-YANZU: Motar Babban Lauya Ta ɓace a Helkwatar Sojin Najeriya Bayan Ya Shigar da Ƙara Kan Wani Babban SojaRahotanni...
04/08/2026

YANZU-YANZU: Motar Babban Lauya Ta ɓace a Helkwatar Sojin Najeriya Bayan Ya Shigar da Ƙara Kan Wani Babban Soja

Rahotanni sun tabbatar da cewa a ranar Litinin, 3 ga Agusta, 2026, wasu da ba a tantance ba sun sace motar wani babban lauya a harabar Helkwatar Sojin Najeriya da ke Abuja, bayan ya je ofishin domin gabatar da ƙorafi kan wani babban jami'in rundunar.

Lauyan ya bayyana cewa lamarin ya girgiza shi matuƙa, yana mai cewa bai taɓa tsammanin za a iya sace mota a cikin Helkwatar Sojin Najeriya ba, wuri da ake ɗauka a matsayin ɗaya daga cikin mafi tsauraran wuraren tsaro a Najeriya.

A cewarsa, motar ba ta ƙunshi kayan hawa kaɗai ba, domin a cikinta akwai laptop ɗinsa, muhimman case files masu alaƙa da aikinsa na lauya, diary, rigarsa, hularsa da sauran muhimman kayayyaki masu matuƙar amfani.

An bayyana cewa ɓacewar waɗannan takardu da kayayyaki na iya haifar da babbar illa ga aikinsa, saboda suna ɗauke da muhimman bayanai da takardun shari'o'i.

An yi kira ga duk wanda ya ga motar ko yake da wani bayani da zai taimaka wajen gano inda take, da ya gaggauta sanar da jami'an tsaro mafi kusa ko kuma ya kira wannan lambar: +234 902 225 0009.

Bayan Ta Yi Yunkurin Tona Asirin Atiku Abubakar Aka Bata Hakuri Dr. Aslam Aliyu Ta Kai Wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ziya...
03/08/2026

Bayan Ta Yi Yunkurin Tona Asirin Atiku Abubakar Aka Bata Hakuri Dr. Aslam Aliyu Ta Kai Wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ziyara Bayan Komawarta APC

TIRKASHI: Hukumar Tace Fina-finai Ta Rufe Shagon Kausar "Back to Back" Mai Maganin Karfin Maza Kan Zargin Tallata BatsaH...
02/08/2026

TIRKASHI: Hukumar Tace Fina-finai Ta Rufe Shagon Kausar "Back to Back" Mai Maganin Karfin Maza Kan Zargin Tallata Batsa

Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta ɗauki matakin rufe shagon Kausar Empire, wacce aka fi sani da lakabin "Back to Back", bisa zargin amfani da kalaman batsa da kuma hotunan da hukumar ta ce sun saɓa da ƙa'idojin tace fina-finai da ɗabi'un al'umma.

Rahotanni sun bayyana cewa Babban Sakataren Hukumar, Abba El-Mustapha, ne ya ba da umarnin rufe shagon bayan hukumar ta karɓi ƙorafe-ƙorafe daga jama'a kan yadda ake tallata wasu magungunan ƙarfin maza ta hanyar da ake zargin ta saɓa da dokokin hukumar.

A cewar Hukumar Tace Fina-finai ta Kano, matakin na daga cikin ƙoƙarin tabbatar da bin dokokin tacewa, kare tarbiyya da kyawawan ɗabi'u, tare da dakile yaɗuwar abubuwan da ake ganin sun saɓa da al'adun Hausawa da koyarwar addinin Musulunci.

Hukumar ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da ɗaukar matakan doka kan duk wani mutum ko kamfani da ya karya ƙa'idojin da aka shimfiɗa domin kare martabar al'umma.

Address

Kano

Telephone

+2349124943407

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa A Yau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa A Yau:

Shortcuts

Share