Oriya Reporters Hausa

Oriya Reporters Hausa Labaran abubuwan dake faruwa a Kano, Najeriya dama Duniya baki ɗaya.

Zamu Dinga baku labarai da ɗumi-ɗuminsu kuma Sahihai ingantattu a kowanne Lokaci awa 24 babu ƙaƙƙautawa

Yanayin sanyi da dusar ƙanƙara fa ya tsananta a Jamus musamman yankin arewacin ƙasar, lamarin da ya tilasta mutane zama ...
10/01/2026

Yanayin sanyi da dusar ƙanƙara fa ya tsananta a Jamus musamman yankin arewacin ƙasar, lamarin da ya tilasta mutane zama a cikin gidajensu tare da ɗaukar matakan kariya. Hukumomi a ƙasar sun sanar da dakatar da zirga-zirgar sufurin jiragen ƙasa masu tafiya nesa tare da rufe wasu hanyoyin mota saboda tsanantar zubowar dusar ƙanƙarar.

📸DW News

Talauci Da Yunwa Suna Tasiri Ga Sha’awar Maza Wajen Son Manyan Mama— Bincike​Maza da ke zaune a yankunan karkara masu ka...
10/01/2026

Talauci Da Yunwa Suna Tasiri Ga Sha’awar Maza Wajen Son Manyan Mama— Bincike
​Maza da ke zaune a yankunan karkara masu karamin karfi sun nuna fin son manyan nonuwa, yayin da maza daga matsakaitan garuruwa s**a fi son matsakaita zuwa manya, su kuma maza daga birane masu babban kudin shiga s**a fi karkata ga kanana zuwa matsakaitan mama.
​A cewar binciken, “Maza daga yankuna masu raunin tattalin arziki sun bayyana manyan nonuwa a matsayin abun da ya fi burge su fiye da maza da ke yankuna masu matsakaicin karfi, wadanda su ma s**a fi son manyan nonuwa fiye da maza da ke zaune a yankuna masu babban matsayi na tattalin arziki.”

Kowa ya zo ya ga, abin da gwamnonin jihohinsu, s**a ware na kasafin kudi (Budget) don yi wa al'ummarsu hidima da su a wa...
10/01/2026

Kowa ya zo ya ga, abin da gwamnonin jihohinsu, s**a ware na kasafin kudi (Budget) don yi wa al'ummarsu hidima da su a wanan sabuwar shekarar ta 2026

1. Lagos: N4.24trn

2. Rivers: N1.85trn

3. Delta: N1.73trn

4. Ogun: N1.67trn

5. Enugu: N162trn

6. Akwa Ibom: N1.58trn

7. Kano: N1.48trn

8. Imo: N1.44trn

9. Niger: N1.07trn

10. Abia: N1.02trn

11. Bayelsa: N1.02trn

12. Kaduna: N985.9bn

13. Cross River: N961.62bn

14. Edo: N939.85bn

15. Jigawa: N901.84bn

16. Katsina: N897.87bn

17. Oyo: N892bn

18. Borno: N890.33bn

19. Ebonyi: N884.87bn

20. Bauchi: N877.05bn

21. Zamfara: N861.3bn

22. Kogi: N820.49bn

23. Plateau: N817.51bn

24. Anambra: N766.37bn

25. Sokoto: N758.7bn

26. Osun: N723.45bn

27. Benue: N695.01bn

28. Taraba: N653.5bn

29. Kwara: N644bn

30. Kebbi: N642.93bn

31. Gombe: N617.95bn

32. Adamawa: N583.3bn

33. Nasarawa: N545.18bn

34. Ondo: N524.41bn

35. Yobe: N515.5bn

36. Ekiti: N415.57bn

Jiharka lamba ta nawa ta fito a jerin waɗannan jihohin?

Arewa ta fara samun zarata masu basiraMatashi ɗan Zamfara Ya Ƙera Robot Mai Gano Gobara Da Gas Domin Kare RayukaWani mat...
10/01/2026

Arewa ta fara samun zarata masu basira

Matashi ɗan Zamfara Ya Ƙera Robot Mai Gano Gobara Da Gas Domin Kare Rayuka

Wani matashi mai basira daga Jihar Zamfara, Abdulbasid Dauda, ya ƙera wani robot na tsaro da aka tsara domin kare rayuka da dukiya ta hanyar gano hayakin gas da gobara tun kafin su haddasa babbar illa.

Abdulbasid ya bayyana cewa robot ɗin na da hankali na musamman (brain) da ke ba shi damar fahimtar magana tare da ba da amsa, lamarin da ya bambanta shi da sauran na’urorin tsaro na gargajiya.

Ya ce wannan ƙirƙira ta zo ne da nufin taimakawa al’umma, musamman wajen rage asarar rayuka da dukiya da gobara ko gas ke haddasawa, tare da ƙarfafa gwiwar matasa masu sha’awar kimiyya da fasaha.

Matashin inventor ɗin ya nemi goyon baya daga jama’a da hukumomi domin duba wannan ƙirƙira tare da yaɗa labarinta, domin ta samu ci gaba da kuma amfani ga al’umma baki ɗaya.

“Ina fatan wannan ƙirƙira za ta zama abin ƙarfafawa ga matasan Arewa da Najeriya gaba ɗaya,” in ji Abdulbasid Dauda.

10/01/2026

Da wanne Yanayi kuka tashi a Yankin ku?
Daga Wajen mu Oriya Reporters Hausa ga Yanayin da muka tashi dashi🙄🙄🤔

Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar KanoAkalla mutane 10 ne s**a mutu, wasu da dama kuma sun jikkata a wani mum...
10/01/2026

Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano

Akalla mutane 10 ne s**a mutu, wasu da dama kuma sun jikkata a wani mummunan hadarin mota da ya afku a kan hanyar Jama’are zuwa Azare a kan titin Kano zuwa Maiduguri, inda wata motar haya ke dauke da fasinjoji daga Gombe zuwa Kano. Hadarin ya faru ne, inda wata mota mai lambar rajista KTG 181 ZZ da ke dauke da fasinjoji 19 ta afka cikin hadari....

DA DUMI-DUMI: China ta ɗauki matsaya mai ƙarfi wajen goyon bayan Iran“China ba za ta tsaya kallon yadda ake take ikon ma...
10/01/2026

DA DUMI-DUMI: China ta ɗauki matsaya mai ƙarfi wajen goyon bayan Iran

“China ba za ta tsaya kallon yadda ake take ikon mallakar ƙasa na babbar al’ummar Iran ta hannun ‘yan daba da masu laifi da ke samun goyon bayan ƙasashen waje ba. Duk abin da gwamnatin Iran ke buƙata — ko a fannin kuɗi, fasaha, leƙen asiri ko na soja — China a shirye take ta bayar da taimako.” inji Abdul Journalist

Shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa INEC, Joash Amupitan, ya ce nasarar babban zaɓen 2027 za ta dogara ne kan yadda hukumar za...
10/01/2026

Shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa INEC, Joash Amupitan, ya ce nasarar babban zaɓen 2027 za ta dogara ne kan yadda hukumar za ta samu amincewar matasan Najeriya, musamman waɗanda za su yi zaɓe karo na farko.

Ya bayyana hakan ne a Legas yayin taron horaswa da shirin dabarun aiki na INEC na shekarar 2026.

Amupitan ya ce matasan zamani na bukatar gaskiya da sahihanci, don haka INEC za ta yi amfani da fasahar zamani da tsari mai ƙarfi domin tabbatar da amincewarsu.

Ya ƙara da cewa zaɓukan ƙananan hukumomin Abuja da na gwamnan Ekiti da Osun za su zama gwaji ga shirin hukumar.

Amupitan ya tabbatar da cewa INEC za ta gudanar da zaɓe bisa ‘yanci, adalci, gaskiya da sahihanci, tare da fatan zaɓen 2027 zai zama tarihi a Najeriya.

Bikin sunan jikan Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II kenan wanda ƴar Sarkin, Fulani Saliha ta haifa a ranar 1 ga watan 1 na...
10/01/2026

Bikin sunan jikan Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II kenan wanda ƴar Sarkin, Fulani Saliha ta haifa a ranar 1 ga watan 1 na wannan shekara a matsayin jika na 7 ga Sarki Sunusi. An sa wa yaron sunan Kakansa, Muhammad Sunusi (Khalifa).

DA ƊUMI-ƊUMI: Wata kotu a Kaduna ta yankewa Sarkin Yanka Musulmai Joshua hukuncin kisa bisa laifin kisan MUSULMAI a Kasu...
10/01/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Wata kotu a Kaduna ta yankewa Sarkin Yanka Musulmai Joshua hukuncin kisa bisa laifin kisan MUSULMAI a Kasuwar Magani dake Kajuru a jahar Kaduna.

Joshua ya yi fice wajen yankan rago wa Musulmin yankin musamman matafiya a yayin da duk aka samu rashin jituwa tsakanin Musulmai da Kiristocin yankin, kamar Yadda wani shaidan gani da ido ya tabbatar wa da kotu.

©️Zinariya

DA DUMI-DUMI: Daga ranar 21 ga wannan watan duk dan Najeriya, da zai shiga Amurka dole sai ya biya Naira miliyan 21. Me ...
10/01/2026

DA DUMI-DUMI: Daga ranar 21 ga wannan watan duk dan Najeriya, da zai shiga Amurka dole sai ya biya Naira miliyan 21.

Me za ku ce?

Kwamishinonin Kano Na Shirin Murabus Yayin da Gwamna Yusuf ke Shiri Koma APC​Majiyoyi da dama sun bayyana wa jaridar Kan...
10/01/2026

Kwamishinonin Kano Na Shirin Murabus Yayin da Gwamna Yusuf ke Shiri Koma APC
​Majiyoyi da dama sun bayyana wa jaridar Kano Times cewa ana sa ran wadannan murabus din suna da alaka da fadada rarrabuwar kawuna a fannin siyasa a cikin Majalisar Zartarwa ta Jihar, musamman tsakanin magoya bayan jagoran jam'iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da kuma masu goyon bayan shirin sauya shekar gwamnan.
​Wani babban jami’in gwamnati, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya bayyana cewa majalisar zartarwar ta rarrabu gida biyu masu adawa da juna, wanda hakan ya sa ci gaba da zaman wasu kwamishinonin a kan mukamansu ya zama “abu mai wahala a siyasance.”
​Majiyar ta kara da cewa: “Wannan gwamnati a zahiri ta rarrabu zuwa gundumomi biyu masu adawa da juna. Wasu kwamishinonin sun yi imanin cewa ba za su iya ci gaba da zama a kan mukamansu ba karkashin wata jam’iyya daban da wadda aka nada su a kai.”

Address

Kano

Telephone

+2348182936818

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Oriya Reporters Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Oriya Reporters Hausa:

Share