Wali Bukhar

Wali Bukhar CEO/MD of Wali Tech Solutions LTD. Damagum International Farms Limited. Albukhari Travel and Tour Services. Philanthropist | Agrarian 👨‍🌾 | Renewable Energy

17/12/2025

Malumfashi, Katsina
Allah kawo zaman lafiya wa kasar mu

Sheikh Mohammed Auwal tareda Sheikh Baba Chinedu
05/12/2025

Sheikh Mohammed Auwal tareda Sheikh Baba Chinedu

GWAMNAN JAHAR BORNO, Prof. Babagana Umara Zulum, yace gwamnatin sa ta kashe akalla Naira billion 100, aharka tsaro aduka...
05/12/2025

GWAMNAN JAHAR BORNO, Prof. Babagana Umara Zulum, yace gwamnatin sa ta kashe akalla Naira billion 100, aharka tsaro aduka fadin jahar a 2025.

Nima fa Opay sun min aika-aika, zasu biyani anan ne ko sai munje can?
05/12/2025

Nima fa Opay sun min aika-aika, zasu biyani anan ne ko sai munje can?

MUSULMAI AKWAI KIRKI DA KARAMCI Maigirma Shugaban Kasa Tinubu ya rantsar da General Christopher Musa a matsayin Babban M...
04/12/2025

MUSULMAI AKWAI KIRKI DA KARAMCI

Maigirma Shugaban Kasa Tinubu ya rantsar da General Christopher Musa a matsayin Babban Ministan tsaron Nigeria

Kamar yadda wani bawan Allah ya fada, ba shakka Musulmai suna da kirki, hakuri, juriya da kuma karamci

A lokacin da Christopher Musa wanda Kirista ne yake aiki a matsayin Shugaban Hafsoshin tsaron Nigeria Chief of Defence Staff (CDS), Sojojin saman Nigeria sun yi kuskuren harin b0ma-b0mai da ya shafi fararen hula Musulmi a lokuta guda uku:
👇
(1) A ranar 3 ga Disamba 2023 jirgin yakin Nigeria ya jefa b0mb bisa kuskure a wani kauye da ake kira Tudun Biri jihar Kaduna, kimanin Musulmi 126 da ke bikin Mauludi s**a rasa ra¥ukansu

(2) A ranar 25 ga Disamba 2023 jirgin yakin Nigeria ya jefa b0mb a wani gari dake jihar Sokoto Kimanin Musulmi 10 sun rasa ra¥ukansu a lokacin da suke barci

( 3) A ranar 13 ga Janairu 2025 jirgin yakin Nigeria ya jefa b0mb a yankin Zurmi na jihar Zamfara aka ya ka$he fararen hula Musulmi mutum 16

Da ace irin wannan abin ya faru akan Kiristoci ne kuma Shugaban rundinonin Sojin Nigeria CDS Musulmi ne da labarin ya fita ta wani salo dabam, kuma da wasu daga cikin Kiristoci da dama sunce harin yana da nasaba da ki$an kare dangi wa Kiristoci saboda banbancin addini

Amma ku kalli yadda Musulmi s**a dauki lamarin, sun yi jimami lokacin da aka sauke General Christopher daga mukamin CDS, sannan mafi akasari Musulmai ne s**a fi tayashi murna bayan an ayyana nadashi Ministan tsaro a lokacin da aka sauke Ministan tsaro Musulmi

Wannan yana ishara zuwa ga zahirin tarbiyyan Musulmi masu hakuri, juriya da kaunar zaman lafiya da kyautata zato ba tare da lura da banbancin addini ba

Muna kara kira ga 'yan uwa abokan zaman mu Kiristoci, don Allah kar ku biye wa wawayen cikinku masu cewa ana yiwa Kiristoci ki$an kare dangi saboda banbancin addini wanda ba gaskiya bane, ki$an da akeyi a Nigeria bashi da wata alaka da banbancin addini

'Yan uwa Kiristoci ku zo mu hada kai mu tabbatar da zaman lafiyar Kasarmu Nigeria, hakan zai sa kowa yayi addininsa ba tare da cutarwa ba

Tabbas General Christopher Musa an kyautata masa zato, babu abinda yake bukata daga garemu Musulmi da Kiristoci face addu'ah akan Allah Ya sa ya fitar da 'yan Nigeria kunya musamman wadanda s**a yabeshi

Muna rokon Allah Ya bamu zaman lafiya da hadin kai a Kasarmu Nigeria

Marubuci Datti Assalafiy

03/12/2025

Assalamu alaikum.

I am delighted to formally share the invitation to our Wedding Fatiha.
With utmost respect, we humbly request your presence, prayers, and blessings as we begin this new chapter of our lives.

The ceremony will take place on:

📅 Date: Saturday, 27th December
🕙 Time: 10:00 AM
📍 Venue: Dass Emirate Council, Dass L.G.A., Bauchi State.

Your attendance will be a great honour to us and our families.
We look forward to celebrating this special and blessed occasion with you.
Thank you for your continuous support, kindness, and prayers.

SENATOR SHEHU BUBA A MIZANI NA ADALCIA cikin satan da ya gabata, Majalisar Dattawan Nigeria ta tsige Senator Shehu Buba ...
03/12/2025

SENATOR SHEHU BUBA A MIZANI NA ADALCI

A cikin satan da ya gabata, Majalisar Dattawan Nigeria ta tsige Senator Shehu Buba daga mukamin Shugaban Kwamitin tsaro na Kasa da tattara bayanan sirri

A jiya sun bashi mukamin Shugaban kwamitin kiwo da dabbobi, Senator Yahaya Abdullahi daga jihar Kebbi shine zai jagoranci Kwamitin tsaro da bayanan sirri na Kasa a zauren Majalisar Dattawa

Me yasa Majalisar Dattawa ta tsige Senator Shehu Buba daga mukaminsa na Shugaban Kwamitin tsaro da tattara bayanan sirri?

(1) Senator Shehu Buba bafulatani ne daga jiharmu na Bauchi, shine Senator da yake wakiltar Bauchi ta kudu, tun kafin ya zama Senator yana da alaka ta sulhu tsakaninsa da barayin daji masu garkuwa da mutane bisa amincewar Gwamnatin tarayya

(2) Ya taka rawa sosai wajen hana 'yan uwansa kabilar fulani wadanda s**a dau makami suna ta'addanci da sunan daukar fansa, kuma mafi yawansu suna jin maganarsa, ya taimaka wajen kubutar da mutane, akan haka wasu s**ayi ta zarginsa bisa kuskure cewa yana tare da bandits alhali ba haka bane, duk abinda yayi da sanin masu iko da tsaro na Kasa

(3) Sai dai abinda watakila shi kansa Senator Shehu Buba bai gano ba shine kungiyoyin ta'addanci masu ikrarin kafa Gwamnatin Musulunci musamman Ansaru sun jima da yiwa fulanin daji kutse, shiyasa aka samu babbar gazawa a batun yin sulhu da 'yan ta'adda, ko da anyi sai abin ya wargaje, hakan ya haifar wa Shehu Buba matsala a aikinsa

(4) Munanan hari da garkuwa da mutane musamman daliban makarantar kwana da fulani barayin daji s**ayi bayan gargadi Amurka, faruwar haka ya sa Gwamnatin tarayya ta lura da rashin kwazon Senator Shehu Buba, wato bai taka rawa wajen hana faruwar harin ba da kuma kubutar da daliban da aka k**a ba, hakan yasa s**a saukeshi daga mukaminsa

A cikin bayanai guda biyar da na ambata a sama, zaku fahimci wasu daga cikin dalilan da yasa aka saukeshi daga mukaminsa na Shugaban Kwamitin tsaro da tattara bayanan sirri na Kasa a Majalisar Dattawa

Muna fatan Allah Ya sa hakan ya zama alheri wa tsaron Nigeria

03/12/2025
ZARGIN WASU 'YAN SIYASA DA HANNU A TA'ADDANCI Tsohon Shugaban rundinar Sojin Nigeria General Leo Irabor yayi zargin wasu...
03/12/2025

ZARGIN WASU 'YAN SIYASA DA HANNU A TA'ADDANCI

Tsohon Shugaban rundinar Sojin Nigeria General Leo Irabor yayi zargin wasu 'yan siyasar Nigeria da hannu a duk ta'addancin da yake faruwa a Nigeria

Yace wasu 'yan siyasa suna daukar nauyin ta'addanci saboda cimma burinsu na siyasa, shiyasa matsalar ba zata kare ba

Idan ba manyan mutane irinsu General Leo Irabor ba babu wanda ya isa ya fito fili yayi wannan zargi 'yan siyasa basu tura karnukansu an batar da shi ba

Duk wanda yake da hannu a ta'addanci Allah Ka shiryar da shi, wadanda ba zasu shiryu ba Allah Ka kawar dasu

Address

Kano

Telephone

+966562702188

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Wali Bukhar posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Wali Bukhar:

Share