Hamshakiya

Hamshakiya Labarai cikin harshen Hausa da dumi-dumin su

wuceKotu ta yanke wa Samha hukuncin ɗaurin wata shidaBabbar kotun tarayya da ke jihar Kano ta yanke wa jarumar fina-fina...
13/02/2026

wuceKotu ta yanke wa Samha hukuncin ɗaurin wata shida

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ta yanke wa jarumar fina-finan Kannywood Samha M Inuwa hukuncin ɗaurin wata shida saboda samunta da laifin wulakanta naira.

Makonni biyu da s**a gabata ne jami'an hukumar EFCC, mai yaƙi da almundahanar kuɗi a Najeriya ta s**a k**a jarumar bayan ɓullar wani bidiyo da a ciki take face majina da takardar naira 1,000.

Jaridar Daily Nigerian ta ce an gurfanar da matashiyar jarumar a gaban kotu bisa zargin, wanda EFCC ta ce ya saɓa wa sashe na 21 na dokar CBN ta 2007.

Samha M Inuwa ta amsa lafin da ake zarginta da shi, tare neman sassauci daga kotun, tana mai cewa wannan ne karon farko da aka sameta da laifi.

Daga nan ne kuma alƙalin kotun, Maishari'a M.S Shuaibu ya yanke mata hukuncin ɗaurin wata shida a gidan yari tare da zaɓin biyan tarar naira 200,000.

🌞 DUHU YA ƘARE! 🌞🔥 Solar yanzu – biya daga baya! 🔥Ka fara amfani da haske yau, ka biya a hankali.💡 Mai ƙarfi | 💰 Tanadin...
06/02/2026

🌞 DUHU YA ƘARE! 🌞
🔥 Solar yanzu – biya daga baya! 🔥
Ka fara amfani da haske yau, ka biya a hankali.
💡 Mai ƙarfi | 💰 Tanadin kuɗi | 🏠 Gida & kasuwanci
📲 Tuntuɓe mu yanzu!

TA GOGE MAJINA DA TAKARDAR DUBU DAYA Hukumar Yaƙi da Rashawa Da Masu Yiwa Tattalin arzikin ƙasa Zagon Kasa EFCC Ta Cafke...
04/02/2026

TA GOGE MAJINA DA TAKARDAR DUBU DAYA

Hukumar Yaƙi da Rashawa Da Masu Yiwa Tattalin arzikin ƙasa Zagon Kasa EFCC Ta Cafke Wata Jarumar Kannywood mai Suna Samha Inuwa Bisa Tuhumamàr ta Da wulakanta Takardar Naira

A Baya Bayan Nan Dai Bidiyon Samha Ya Yaɗu Inda Aka Ganta Tana Goge Majina Da Tàkardar Naira ₦1000

Wane Hukunci Kuke Ganin Ya dace Da wannan Jaruma?

Fitaccen malamin ya rasu ne bayan fama da gajeriyar jinya a asibitin sojoji na 44 da ke jihar Kaduna.Malamin ya rasu ne ...
02/02/2026

Fitaccen malamin ya rasu ne bayan fama da gajeriyar jinya a asibitin sojoji na 44 da ke jihar Kaduna.

Malamin ya rasu ne yana da shekara 57, kuma ya rasu ya bar mata huɗu da ƴaya 37.

An fitar da sunayen mutanen da aka sace a KadunaAn fitar da sunayen mutum 170 da aka sace a ƙauyen Kurmin Wali a jihar K...
21/01/2026

An fitar da sunayen mutanen da aka sace a Kaduna

An fitar da sunayen mutum 170 da aka sace a ƙauyen Kurmin Wali a jihar Kaduna, bayan rahotanni sun bayyana cewa wasu mahara sun kai hari a ƙauyen da ke fama da matsalar tsaro.

A ranar Litinin ne rahotanni s**a bayyana cewa wasu mahara sun kai farmaki a ƙauyen sa'ilin da al'umma ke ibada a coci-coci, inda s**a yi musu ƙofar raggo tare da kora su zuwa daji.

Daga baya al'ummar sun bayyana cewa mutane 10 sun samu tserewa daga hannun ƴan bindigar.

A jiya Talata shalkwatar rundunar ƴansanda ta Najeriya ta tabbatar da faruwar al'amarin bayan musantawa da ta yi tun farko.

Sanarwar da ta samu sa hannun mai magana da yawun rundunar ta ƙasa, Benjamin Hundeyin ta ce binciken da sashin tattara bayanan sirri na rundunar ya gudanar ya tabbatar masu cewa an yi garkuwa da mutanen.

Jerin sunayen waɗanda aka sacen da al'ummar s**a fitar ya ƙunshi mutum 177 da kuma shekarunsu.

Al'ummar sun bayyana cewa sun tattara sunayen ne daga coci-cocin da aka shiga aka aka kwashe masu ibadar a ranar Lahadi.

ZAKARAN DA ALLAH YA NUFA DA CARA...A Karshe Kasar Senegal Sun Yi Nasarar Cin Kofin Kasashen Afrika, Bayan Zargin Magudi ...
19/01/2026

ZAKARAN DA ALLAH YA NUFA DA CARA...

A Karshe Kasar Senegal Sun Yi Nasarar Cin Kofin Kasashen Afrika, Bayan Zargin Magudi Da Aka So AYi Musu

18/01/2026

Dalilan da s**a sa aka kasa shawo kan matsalar tsaro a Najeriya - Janar Christopher Musa

A tattaunawar da muka yi da ministan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya ce ya aika wa wasu jihohi gargadin cewa sulhun suke yi da ‘yan bindiga yana kawo cikas ga aikin da suke yi.

Ministan ya kuma bayyana aniyarsa ta gina katanga a wasu iyakokin Najeriya domin hana ƙarin ‘yan bindiga shiga ƙasar.

Hamshakiya

'Yan sanda a jihar Kano sun ce sun k**a mutanen ne bayan mummunar kisan gillar da aka yi wa wata màhaifiya da 'ya'yanta ...
18/01/2026

'Yan sanda a jihar Kano sun ce sun k**a mutanen ne bayan mummunar kisan gillar da aka yi wa wata màhaifiya da 'ya'yanta shida a unguwar Dorayi da ke jihar Kano.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun 'yan sandan jihar kano, Abdullahi Kiyàwa ya fitar, sun k**a su ne tare da kayan sawa masu jini, wayoyin wàdanda aka kashe da kuma wata adda.

Limamin da ya tseratar da Kristoci a Plateau ya rasuAlhaji Abubakar Abdullahi, limamin Yelwa, Gindin Akwati a Barikin La...
16/01/2026

Limamin da ya tseratar da Kristoci a Plateau ya rasu

Alhaji Abubakar Abdullahi, limamin Yelwa, Gindin Akwati a Barikin Ladi, Plateau, wanda ya yi fice a shekarun baya wajen kare mabiya Kirista daga kisa a rikicin Jos, ya rasu a daren Alhamis bayan fama da rashin lafiya.

Ɗan autan marigayin, Saleh Abdullahi Abubakar, ya tabbatar wa da BBC cewa malamin ya rasu ne da misalin ƙarfe 9 na dare yana da kimanin shekara 90 a duniya.

Saleh ya ce mahaifinsa ya yi fama da rashin lafiya ta ciwon zuciya inda aka kwantar da shi a asibiti a Filato.

"Har an sallame shi bayan jinya a asibiti saboda ya koma gida, sai bayan wajen wata uku zuwa huɗu ne ciwon ya tashi, sai muka mayar da shi asibiti a duba shi a makon da ya gabata, daga nan ne s**a sake kwantar da shi wanda daga bisani ya rasu jiya da dare."

Ɗan ya ce an riga an mayar da gawar shi gida a Yelwa, Gindin Akwati da ke Barikin Ladi domin yi masa jana'iza da ƙarfe biyu bayan sallar Juma'a.

Gwamnan Jihar Plateau, Barr. Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana jimami kan rasuwar limamin, inda ya bayyana rashin a matsayin babban rashi ga jihar baki ɗaya.

A cikin sakon ta’aziyyarsa, Gwamna Mutfwang ya bayyana marigayin a matsayin jajirtacce wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai, da kare mutane musamman mata da yara.

Gwamna Mutfwang ya ce rasuwar limamin rashi ne babba ga iyalinsa da al’ummarsa, da kuma jihar Plateau gaba ɗaya.

Ɗan marigayin ya ce mahaifinsa ya samu karramawa daban-daban bayan tseratar da Kiristoci da ya yi a wani rikicin Jos, ciki har da zuwa hajji sau biyu da kuma lambobin karrama daga gwamnatin Buhari.

Marigayin ya rasu yana da ‘ya’ya 19 da suke raye, ciki har da maza 12 da mata 7, sannan ya auri mata uku inda biyu daga cikinsu sun rasu.

Ba mu kawo sabon harajin cirewa da tura kuɗi ba - Hukumar harajin NajeriyaHukumar Haraji ta Najeriya NRS ta bayyana cewa...
16/01/2026

Ba mu kawo sabon harajin cirewa da tura kuɗi ba - Hukumar harajin Najeriya

Hukumar Haraji ta Najeriya NRS ta bayyana cewa rahotanni da ke yawo a wasu sassa na kafofin yaɗa labarai game da cewa an kawo sabon harajin cirewa da tura kuɗi wato VAT ba gaskiya bane.

Hukumar ta ce wannan bayani na yaudara ne kuma babu sabuwar haraji i da aka kafa a kan kwastomomi aka ce wajibi ne sai sun biya.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X.

NRS ta bayyana cewa tun farko dama wannan haraji na aiki a ƙarkashin dokar haraji na Najeriya da aka kafa tun shekaru da dama inda bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi ke cire kuɗin gudanarwa, da na hidima da s**a yi da sauran kuɗaden da suke cirewa, ba sabon haraji bane.

Ta bayyana cewa duk wani bayanin da ke cewa gwamnati ta umarci bankuna da su fara cire harajin kashi 7.5 a kan kudin da aka cire ko aka tura da s**a kai naira 100,000 ba dai dai bane.

Saboda haka ne hukumar ta buƙaci jama’a da masu ruwa da tsaki da su daina yarda da labaran da ba su da tushe, su kuma dogara ga sanarwar hukumar kai tsaye don samun sahihin bayani.

15/01/2026
Moroko ta kai wasan ƙarshe na Gasar AFCON bayan doke Najeriya a bugun fenariti.Moroko za ta fafata da Senegal a wasan ƙa...
15/01/2026

Moroko ta kai wasan ƙarshe na Gasar AFCON bayan doke Najeriya a bugun fenariti.

Moroko za ta fafata da Senegal a wasan ƙarshe ranar Lahadi.

Hamshakiya

Address

Kano
730010

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00

Telephone

+2347066102221

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hamshakiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hamshakiya:

Share