Climate Watch Hausa

Climate Watch Hausa Climate Watch Hausa shafi ne da ke wayar da kai kan sauyin yanayi da tasirinsa ga rayuwa.

Muna kawo labarai, bincike da hanyoyin kare muhalli a Najeriya da duniya. 🌱
Kare Muhalli, Kare Rayuwa

Gwamnatin Kano Ta Haɗa Kai da Makarantun Gaba da Sakandare Wajen Shuka Bishiyoyi.Ma’aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da ...
17/08/2026

Gwamnatin Kano Ta HaÉ—a Kai da Makarantun Gaba da Sakandare Wajen Shuka Bishiyoyi.

Ma’aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi ta Jihar Kano ta ƙaddamar da wani sabon shiri na haɗa gwiwa da manyan makarantun gaba da sakandare domin faɗaɗa dashen bishiyoyi da ƙarfafa kiyaye muhalli a faɗin jihar.

Kwamishinan ma’aikatar, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ne ya ƙaddamar da shirin a Kwalejin Musulunci da Ilimin Shari’a ta Mallam Aminu Kano, wato Aminu Kano College of Islamic and Legal Studies.

Mahukuntan makarantar da wakilan ɗalibai sun nuna goyon bayansu ga shirin, tare da alƙawarin kula da bishiyoyin da aka dasa da kuma kare su daga lalacewa.

A ƙarƙashin shirin, kowace bishiya da za a dasa za ta samu lambar tantancewa ta musamman, yayin da za a ware wasu jami’an makarantu domin kula da bishiyoyin, bibiyar yadda suke girma da kuma tabbatar da cewa an kare su.

Kwamishinan ya bayyana cewa shirin wani ɓangare ne na babban shirin dashen bishiyoyi da gwamnatin Jihar Kano ke aiwatarwa ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Ya ce gwamnatin ta aiwatar da shirye-shiryen dashen bishiyoyi miliyan ɗaya da kuma miliyan uku, yayin da yanzu take faɗaɗa ƙoƙarin zuwa babban shirin dashen bishiyoyi miliyan goma a wannan shekara.

Dakta Dahiru ya bayyana dashen bishiyoyi a matsayin jari na dogon lokaci da ke da muhimmiyar gudummawa wajen kare muhalli. Ya ce bishiyoyi na taimakawa wajen tsaftace iska, rage zafin yanayi, yaƙi da zaizayar ƙasa, samar da inuwa da kuma kare halittu.

Ya kuma ƙarfafa gwiwar ɗalibai da su zama jakadun kare muhalli ta hanyar shiga ayyukan dashen bishiyoyi, kula da wuraren renon tsirrai da kuma kare bishiyoyin da aka dasa.

Makarantar Ta Nemi Tallafin Gwamnati
A yayin taron, mahukuntan makarantar sun gabatar da wasu buƙatu ga kwamishinan, ciki har da samar da ingantaccen ruwan sha.

Sun bayyana cewa samun isasshen ruwa na da matuƙar muhimmanci wajen tsafta, kiwon lafiya da kuma ayyukan lambu da ake gudanarwa a makarantar, musamman ganin yadda ɗalibai ke samun horo na aikace-aikacen noma.

Makarantar ta kuma nemi taimakon gwamnati wajen samar da katafaren É—akin noman zamani, wato greenhouse, domin inganta koyar da aikin gona, gudanar da bincike da kuma noman amfanin gona bisa hanyoyin da s**a dace da sauyin yanayi.

Haka kuma, an nemi tallafin magungunan kashe ƙwari, kayan yaƙi da cututtukan amfanin gona da kuma shawarwarin ƙwararru domin magance matsalolin ƙwari da cututtuka da ke lalata amfanin gonar makarantar.

Gwamnati Ta Jaddada Ƙudirin Inganta Ruwa da Muhalli
Da yake mayar da martani, Kwamishinan ya sake tabbatar da ƙudirin ma’aikatar na tallafa wa cibiyoyin ilimi da kuma magance ƙalubalen da s**a shafi muhalli da albarkatun ruwa a jihar.

Ya amince da cewa akwai ƙalubale wajen samar da ruwa da ababen more rayuwa, yana mai cewa gwamnati na ci gaba da gyara da inganta manyan masana’antun sarrafa ruwa da tsarin samar da ruwa a sassa daban-daban na jihar.

Ya bayyana cewa ana sa ran ruwa zai fara samun ingantaccen yanayi a cikin birnin Kano cikin watanni biyu masu zuwa.
Domin magance matsalar ruwa a makarantar cikin gaggawa, Kwamishinan ya bayar da umarnin a hako mata rijiyar burtsatse domin samar da ruwa.

An kammala taron da dashen bishiyoyi, inda ɗalibai da shugabannin makarantar s**a shiga aikin tare da Kwamishinan, a matsayin wata alama ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da cibiyoyin ilimi wajen kare muhalli.

Climate Watch Hausa: Takaddamar Makiyayar Gwamma da Turare Ta Jaddada Muhimmancin Kare Wuraren Kiwo a KanoKaramar Hukuma...
11/08/2026

Climate Watch Hausa: Takaddamar Makiyayar Gwamma da Turare Ta Jaddada Muhimmancin Kare Wuraren Kiwo a Kano

Karamar Hukumar Bunkure ta Jihar Kano ta musanta zargin sayar da makiyayar Fulani da rugagen da ke yankin Gwamma da Turare, tana mai cewa za ta ci gaba da kare wuraren kiwo da sauran wuraren da aka ware domin makiyaya.

Shugaban Karamar Hukumar Bunkure, Hon. Muhammad Aliyu Basheer, ya bayyana hakan yayin wata ziyara da shugabannin kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN), reshen Jihar Kano, tare da jami'an Hukumar Karbar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), s**a kai yankin Gwamma da Turare.

Ziyarar ta biyo bayan ikirarin wani mutum mai suna Alhaji Kabiru, wanda ake cewa yana da'awar mallakar wasu wurare a yankin, ciki har da wuraren da makiyaya ke amfani da su wajen kiwo da zama.

A yayin ziyarar, hukumomin sun duba wuraren da ake takaddama a kansu domin fahimtar halin da ake ciki da kuma neman tabbatar da gaskiyar lamarin.

Shugaban Karamar Hukumar Bunkure ya musanta cewa gwamnatin karamar hukumar ta sayar da makiyayar ko rugagen Fulani da ke Gwamma da Turare.

Ya ce duk wanda yake ikirarin cewa ya sayi makiyayar daga hannun karamar hukumar ya gabatar da hujjar sayen, yana mai jaddada cewa gwamnatin karamar hukumar za ta ci gaba da kare wuraren da aka ware domin kiwo da zaman makiyaya.

Hon. Basheer ya kuma tabbatar wa shugabannin MACBAN cewa gwamnatin karamar hukumar za ta ci gaba da bai wa makiyaya goyon baya wajen kare hakkokinsu da kuma tabbatar da cewa wuraren kiwo ba su zama sanadin rikici tsakanin al'umma ba.

Kare makiyaya da muhalli

A nata bangaren, kungiyar MACBAN ta yi kira ga gwamnatin Karamar Hukumar Bunkure da ta dauki matakan da s**a dace domin dakile duk wani yunkuri na mamaye ko kwace makiyayar Fulani a yankin.

Shugaban MACBAN na Jihar Kano, Ambasada Abdullahi Bakoji Adamu, ya bukaci al'umma da su mutunta wuraren da gwamnati ta ware domin kiwo, tare da kauce wa ayyukan da za su iya kara takura wa makiyaya ko haifar da rikici.

Ya kuma yi kira ga manoma da makiyaya da su zauna lafiya, yana mai cewa bangarorin biyu suna da muhimmiyar rawa wajen samar da abinci da bunkasa tattalin arzikin jihar.

Me ya sa kare makiyaya ya shafi muhalli?

A mahangar Climate Watch Hausa, batun kare makiyaya ba wai batun kiwon dabbobi kawai ba ne; yana da alaka da sarrafa albarkatun kasa, ruwa, ciyayi da dorewar rayuwar al'ummomin karkara.

Masana sun nuna cewa sauyin yanayi, sauyin tsarin ruwan sama, fari, hamadar da ke kara yaduwa da lalacewar kasa na iya rage samun ruwa da wuraren kiwo, wanda hakan ke kara gasar neman albarkatun kasa tsakanin manoma da makiyaya.

Saboda haka, kare wuraren kiwo da hanyoyin da makiyaya ke bi na iya zama wani bangare na kokarin rage matsin lambar da ke tattare da amfani da kasa, musamman a yankunan da ke fuskantar matsalar lalacewar kasa da karancin albarkatun muhalli.

Sai dai masana sun kuma jaddada cewa rikicin manoma da makiyaya ba ya da alaka da sauyin yanayi kadai; batutuwan mallakar fili, karuwar jama'a, fadadar noma, rashin kyakkyawan tsarin kula da kasa da kuma matsalolin tsaro na taka rawa.

Kira ga zaman lafiya da dorewar albarkatun kasa

Jagoran Fulani makiyaya na dajin Gwamma, Muhammad Bello, ya gode wa gwamnatin Karamar Hukumar Bunkure, MACBAN da PCACC bisa ziyartar yankin domin duba halin da wuraren suke ciki.

Ya ce irin wannan mataki na iya taimakawa wajen magance takaddamar cikin lumana tare da tabbatar da adalci ga dukkan bangarorin.

Climate Watch Hausa na kallon wannan lamari a matsayin wata tunatarwa kan muhimmancin samar da kyakkyawan tsarin kula da filaye, wuraren kiwo da albarkatun ruwa, domin tabbatar da zaman lafiya da kuma kare rayuwar al'ummomin da s**a dogara da noma da kiwo.

Al'amuran da s**a shafi makiyaya da manoma suna bukatar tattaunawa, bin doka da kuma tsarin kula da albarkatun kasa mai dorewa, domin kare muhalli tare da rage yiwuwar rikice-rikicen da ka iya tasowa sakamakon gasa kan kasa da ruwa.

07/08/2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Allah Wadai Da Yunkurin Sayar Da Hukumar Yaki Da Hamada Da Zaizayar Ƙasa Ta Najeriya Da Ke Jambulo

SANARWA GA MANEMA LABARAIMUTUNTA DOKAR ZARTARWA TA GWAMNATIN JIHAR KANO KAN BURTALAI DA FILAYEN KIWONi, Amb. Capt. Abdul...
06/08/2026

SANARWA GA MANEMA LABARAI

MUTUNTA DOKAR ZARTARWA TA GWAMNATIN JIHAR KANO KAN BURTALAI DA FILAYEN KIWO

Ni, Amb. Capt. Abdullahi Bakoji Adamu (Mai Ritaya), Shugaban Ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN), Reshen Jihar Kano, kuma mai sharhi da nazari kan harkokin tsaro a Najeriya, a madadin ɗaukacin mambobin ƙungiyar, ina sake tunatar da al'ummar Jihar Kano game da muhimmancin mutunta Dokar Zartarwa (Executive Order) da Gwamnatin Jihar Kano ta fitar wadda ta haramta sayarwa, rabawa ko mallakar burtalai da filayen kiwo na gwamnati ba tare da bin tanadin doka ba.

Muna kira ga manoma, makiyaya, masu sarautun gargajiya, shugabannin al'umma, jami'an ƙananan hukumomi da duk masu ruwa da tsaki da su mutunta wannan doka tare da gujewa duk wani mataki da zai saɓa da ita. Wannan doka an samar da ita ne domin kare muradun al'umma, tabbatar da zaman lafiya da kuma hana rikice-rikicen da ka iya tasowa sakamakon mamaye ko sayar da filayen kiwo ba bisa ƙa'ida ba.

Muna sanar da jama'a cewa mun riga mun tattauna da hukumomin da Gwamnatin Jihar Kano ta ɗora wa alhakin aiwatar da wannan Dokar Zartarwa. Saboda haka, duk wanda aka samu da karya dokar, ko ta hanyar saye, sayarwa, rabawa, ko mamaye irin waɗannan filaye, za a miƙa shi ga hukumomin da abin ya shafa domin ɗaukar matakin doka ba tare da nuna bambanci ba.

A matsayina na mai nazari kan harkokin tsaro, ina ganin rashin bin wannan doka na iya haifar da manyan barazana ga tsaron jihar, ciki har da:

- Ƙaruwar rikice-rikicen manoma da makiyaya.
- Mamayar filayen gwamnati ba bisa ƙa'ida ba da haddasa rikice-rikicen mallakar ƙasa.
- Barazana ga zaman lafiya da tsaro a matakin ƙauyuka da ƙananan hukumomi.
- Ƙara yawan shari'o'i, tashin hankali da ɗaukar doka a hannu.
- Hana gwamnati aiwatar da manufofinta na bunƙasa harkar kiwo da noma cikin tsari.

Saboda haka, muna roƙon kowa da kowa da ya bi doka, ya mutunta umarnin Gwamnatin Jihar Kano, kuma ya guji duk wani abu da zai iya jefa al'umma cikin rikici ko rashin zaman lafiya.

Muna tabbatar wa gwamnati cikakken goyon bayan Ƙungiyar Miyetti Allah ta Jihar Kano wajen wayar da kan al'umma da kuma haɗin gwiwa da hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da bin doka.

Idan kunne ya ji, jiki ya tsira.

Amb. Capt. Abdullahi Bakoji Adamu (Rtd.)
Shugaban, Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN), Jihar Kano
Mai Sharhi da Nazari kan Harkokin Tsaro a Najeriya

Tinubu Ya Amince da Karin Albashin Sojoji Tsakanin Kashi 30 zuwa 80 Cikin 100.Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya aminc...
04/08/2026

Tinubu Ya Amince da Karin Albashin Sojoji Tsakanin Kashi 30 zuwa 80 Cikin 100.

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ƙarin albashin jami'an rundunar sojin Najeriya da zai kai tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin 100, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Satumban 2026.

A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata, an bayyana cewa karin albashin zai shafi kusan sojoji 250,000 a faɗin ƙasar.

Sabon tsarin ya tanadi cewa manyan hafsoshi daga mukamin Kanar zuwa sama za su samu karin albashi na kashi 30 cikin 100, yayin da jami'ai daga Lieutenant Colonel zuwa Warrant Officer za su amfana da karin kashi 50 cikin 100.

Haka kuma, sojoji daga mukamin Private zuwa Staff Sergeant za su samu karin albashi na kashi 80 cikin 100.

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta walwalar jami'an soji tare da nuna godiya ga sadaukarwar da suke yi wajen yaƙi da ta'addanci, garkuwa da mutane da sauran barazanar tsaro a Najeriya.

Ya kuma jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da samar wa rundunar soji kayan aiki da fasahohin zamani domin ƙara inganta ƙwarewa da tasirin ayyukansu.

04/08/2026

Mazauna yankin Gidan Ruwa na Guzu-Guzu sun yaba da ƙoƙarin Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, na samar da ruwan sha, tare da bayyana aikin a matsayin babban sauƙi ga al’ummar yankin.

Gwamnatin Kano Ta Buɗe Ƙofa Ga Masu Zuba Jari a Fannin Tsaftar Muhalli.Gwamnatin Jihar Kano ta yi kira ga 'yan kasuwa da...
03/08/2026

Gwamnatin Kano Ta Buɗe Ƙofa Ga Masu Zuba Jari a Fannin Tsaftar Muhalli.

Gwamnatin Jihar Kano ta yi kira ga 'yan kasuwa da masu zuba jari da su saka hannun jari a fannin tsaftar muhalli domin inganta lafiyar al'umma, samar da ayyukan yi da kuma bunƙasa tattalin arzikin jihar.

Kwamishinan Ma'aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da shirin haɗa gwiwar gwamnati da masu zaman kansu wajen magance matsalolin tsaftar muhalli, wanda aka gudanar a Otal ɗin Porto Golf da ke Kano.

A cewarsa, Kano na kallon fannin tsaftar muhalli a matsayin wata babbar dama ta zuba jari, inda ya ce akwai damammaki a fannoni kamar gina bandakunan jama'a, sarrafa najasa, tace shara da mayar da ita albarkatu masu amfani.

Ya kuma bayyana cewa gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta aiwatar da muhimman sauye-sauye, ciki har da fara aiwatar da Dokar Kare Muhalli da Yaƙi da Gurɓata Muhalli, farfaɗo da hukumomin kula da muhalli, da gyaran cibiyoyin tace ruwa.

Hakazalika, Dakta Hashim ya ƙaddamar da shirin Smart Kano Waste and Sanitation Initiative, wanda ke da nufin inganta ayyukan tsaftar muhalli ta hanyar gina bandakunan zamani, bunƙasa tsarin sarrafa najasa, amfani da fasahar zamani wajen sa ido da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa da masu zaman kansu.

Ya yi kira ga masu zuba jari, cibiyoyin kuÉ—i da abokan hulÉ—ar ci gaba da su tallafa wa ayyukan tsaftar muhalli masu É—orewa ta hanyar sabbin hanyoyin samar da kuÉ—i, tallafin fasaha da haÉ—in gwiwar gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu.

Dakta Hashim ya jaddada cewa gwamnatin Kano za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari tare da tabbatar da cewa ayyukan tsaftar muhalli sun kasance masu inganci, masu dorewa kuma masu amfani ga al'umma baki É—aya.

Wai da gaske Bakan Gizo 🌈 ne ya ke shanye ruwan sama idan hadari ya hado?
03/08/2026

Wai da gaske Bakan Gizo 🌈 ne ya ke shanye ruwan sama idan hadari ya hado?

Kwamishinan Yaɗa Labarai na Kano Ya Bai Wa Ƙungiyar Gyaran Kayanka Babur, Ya Ƙara Alkawarin ₦1mZAWACHIKI, KANO — Kwamish...
02/08/2026

Kwamishinan Yaɗa Labarai na Kano Ya Bai Wa Ƙungiyar Gyaran Kayanka Babur, Ya Ƙara Alkawarin ₦1m

ZAWACHIKI, KANO — Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya kai ziyara ofishin Ƙungiyar Gyaran Kayanka ta Ƙaramar Hukumar Kumbotso da ke garin Zawachiki, inda ya gana da shugabanni da mambobin ƙungiyar.

Ziyarar, wadda ta gudana a yau Lahadi, 2 ga Agusta, 2026, ta mayar da hankali ne kan ƙarfafa haɗin gwiwa da tallafa wa ƙungiyar wajen gudanar da ayyukanta na ci gaba.

A yayin ziyarar, Kwamishinan Yaɗa Labarai, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya miƙa kyautar sabon babur kirar Hunter Hero ga shugaban Ƙungiyar Gyaran Kayanka ta Ƙaramar Hukumar Kumbotso, Malam Sagiru Sa'idu Zawachiki, domin taimaka masa wajen gudanar da ayyukan ƙungiyar.

Baya ga wannan kyauta, Kwamishinan ya kuma yi wa ƙungiyar alkawarin bayar da tallafin Naira miliyan ɗaya (₦1,000,000) domin gudanar da ayyukan ci gaba da bunƙasa ƙungiyar.

Da yake jawabi yayin taron, an bayyana wannan tallafi a matsayin wani mataki na ƙarfafa ƙungiyoyi da masu ruwa da tsaki wajen taka rawar gani wajen ci gaban al'umma.

Shugaban ƙungiyar, Malam Sagiru Sa'idu Zawachiki, ya nuna godiyarsa ga Kwamishinan bisa wannan tallafi, tare da tabbatar da cewa ƙungiyar za ta yi amfani da kayan da kuɗin tallafin wajen cimma manufofinta na ci gaba.

Rahoto: Al-Manasik Reporters Hausa (AMR Hausa)

Address

Zawachiki Quarters Kumbotso Local Government Area
Kano
700102

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Climate Watch Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share