SHURA TV

SHURA TV An bude Wannan Gidan Talabijin ne domin ilmantar wa hadi da fadakarwa, zamu cigaba da wallafa muku labaran duniya a ko da yaushe.

Jigon siyasar gidan Kwankwaso Hajiya Shafa'atu Ahmad ( Landon B) Ta zabi kasancewa tare da Gwamna Abba Kabir Yusuf, baya...
27/01/2026

Jigon siyasar gidan Kwankwaso Hajiya Shafa'atu Ahmad ( Landon B) Ta zabi kasancewa tare da Gwamna Abba Kabir Yusuf, bayan dogon Nazarin da tayi na irin nasarorin Da Abba yayi a jihar Kano.

‎Ta bayyana komawarta jam'iyyar APC ne cikin wani sakon Faifan video da ya karade kafafen sada zumunta, inda a jiyo ta tana bawa masoyan Abba Kabir da Kanawa Hakuri kan kuskuren kalamai da tayi, inda ta bada Hakuri ta bukaci a yafe mata, tana tare da Me girma Gwamna kanawa Abba Kabir Yusuf.

‎Masu sharhi na ganin wannan mataki na iya ƙara ƙarfin siyasa ga gwamnatin Abba Kabir Yusuf, tare da sauya yanayin fafatawa a cikin jam’iyyu da kungiyoyin siyasa a Kano, musamman a duba da tasirin da Hajiya Shafa’atu ke da shi a tsakanin magoya baya.

https://www.facebook.com/share/p/1DyuvThsqm/

Jigon siyasar gidan Kwankwaso Hajiya Shafa'atu Ahmad ( Landon B) Ta zabi kasancewa tare da Gwamna Abba Kabir Yusuf, bayan dogon Nazarin da tayi na irin nasarorin Da Abba yayi a jihar Kano.

‎Ta bayyana komawarta jam'iyyar APC ne cikin wani sakon Faifan video da ya karade kafafen sada zumunta, inda a jiyo ta tana bawa masoyan Abba Kabir da Kanawa Hakuri kan kuskuren kalamai da tayi, inda ta bada Hakuri ta bukaci a yafe mata, tana tare da Me girma Gwamna kanawa Abba Kabir Yusuf.

‎Masu sharhi na ganin wannan mataki na iya ƙara ƙarfin siyasa ga gwamnatin Abba Kabir Yusuf, tare da sauya yanayin fafatawa a cikin jam’iyyu da kungiyoyin siyasa a Kano, musamman a duba da tasirin da Hajiya Shafa’atu ke da shi a tsakanin magoya baya.

Ofishin Malami Ya Zargi DSS da EFCC da Take Umarnin Kotu da Hana Shi Kare Kansa a Gaban Shari’aOfishin tsohon Ministan S...
24/01/2026

Ofishin Malami Ya Zargi DSS da EFCC da Take Umarnin Kotu da Hana Shi Kare Kansa a Gaban Shari’a

Ofishin tsohon Ministan Shari’a kuma Lauya Babba, Abubakar Malami, SAN, ya zargi Hukumar DSS da EFCC da aikata matakai da ke nuna take umarnin kotu tare da tauye haƙƙinsa na kundin tsarin mulki na samun adalci da cikakkiyar damar kare kansa a gaban shari’a.

Rahoton ofishin ya bayyana cewa bayan Hukumar EFCC ta shigar da ƙara a kansa, Kotun Tarayya ta bayar da belin Malami k**ar yadda doka ta tanada. Sai dai duk da haka, EFCC ta jinkirta miƙa fasfofinsa na cikin gida da na ƙetare zuwa kotu na tsawon kusan mako guda, alhali kuwa miƙa fasfon na daga cikin muhimman sharuddan kammala beli.

Ofishin Malami ya ce wannan jinkiri ya jawo tsawaita tsare shi ba bisa ka’ida ba, tare da hana aiwatar da sahihin umarnin kotu, lamarin da ya nuna raini ga ikon shari’a.

Rahoton ya ƙara da cewa bayan da Malami ya kammala dukkan sharuddan belin da kotu ta gindaya kuma aka sake shi daga Gidan Gyaran Hali na Kuje, nan take Hukumar DSS ta sake cafke shi. An tsare shi na tsawon kwanaki biyar ba tare da ba shi damar ganawa da lauyoyinsa ko iyalansa ba.

Sai a ranar Juma’a ne kawai aka ba shi damar ganawa da tawagar lauyoyinsa, bayan tsawon lokaci na keɓewa, jinkiri da kuma abin da ofishin ya bayyana a matsayin munanan take-taken haƙƙin ɗan Adam.

Ofishin Malami ya jaddada cewa wannan tsarewa ta faru ne a wani muhimmin lokaci da ake buƙatar Malami ya shirya tare da buɗe kariyarsa a shari’ar kwace kadarori ta wucin-gadi da EFCC ke jagoranta a gaban Kotun Tarayya. Hana shi damar ganawa da lauyoyi a wannan lokaci, a cewar rahoton, ya raunana ikon sa na shiryawa, ba da umarni da kuma gabatar da takardu a gaban kotu.

Rahoton ya bayyana wannan jerin abubuwa a matsayin alamar tsarin da ake bi na cafke mutum kafin kammala bincike, sannan a fara neman hujjoji bayan tsarewa, wani salo da ke saɓa wa doka da kuma kundin tsarin mulki. Ofishin ya nuna damuwa kan yadda DSS ke bin irin wannan hanya ta cafke mutum, tsare shi, sannan daga baya a fara tattara hujjoji.

Ofishin Malami ya nanata cewa belin da kotu ta bayar dole ne ya zama mai ma’ana, ba wai a tauye shi ta hanyar jinkiri, sake cafke mutum ko hana shi damar samun wakilcin lauya ba. Rahoton ya yi gargaɗi cewa irin waɗannan ayyuka na rage martabar kotuna tare da barazana ga haƙƙin ɗan Adam da bin doka da oda a Najeriya.

A ƙarshe, Abubakar Malami, SAN, ya bayyana cewa yana shirye tsaf domin kare kansa a gaban kotu bisa tafarkin doka, tare da kira ga dukkan hukumomin gwamnati da su mutunta umarnin kotu, kundin tsarin mulki da kuma ƙa’idojin mulkin doka.

DA DUMI-DUMI: Hukumar Shari'a Ta Horas da Alkalan Majistiri Kan Sabbin Hanyoyin Koyan Dabarun Aiki da Fasahar AI a Katsi...
06/01/2026

DA DUMI-DUMI: Hukumar Shari'a Ta Horas da Alkalan Majistiri Kan Sabbin Hanyoyin Koyan Dabarun Aiki da Fasahar AI a Katsina

Hukumar Shari’a ta Jihar Katsina ta shirya Workshop na Kara Kwarewa ga Magistoci kan fasahar sadarwa (ICT), musamman Artificial Intelligence (AI) da Sabbin Hanyoyin Yada Labarai, domin ƙara ƙarfin ilimin shari’a a zamanin dijital.

Shugaban Alkalan Jihar Katsina, Hon. Justice Musa Danladi Abubakar, ya bayyana cewa kotuna dole ne su daidaita da sabbin hanyoyin yada labarai yayin da ake yawan fuskantar al’amura daga ayyukan jama’a a social media, wallafe-wallafen yanar gizo, da hujjojin da aka samar ta hanyar dijital. Ya kara da cewa, duk da sabbin hanyoyin yada labarai sun sauƙaƙa samun bayani, sun kuma kawo kalubale k**ar yaduwar labaran karya, laifukan yanar gizo, barna ga suna, da amfani da kafafen dijital ba bisa ka’ida ba.

Babban Rajistar Shari’a, Dr. Basira Umar, ta ce taron ya zo a kan lokaci, inda ta yi kira ga magistoci da su yi amfani da wannan dama wajen ƙara ilimi da ƙwarewa, ganin yadda ICT, AI, da sabbin hanyoyin yada labarai ke tasiri a tsarin gwamnati da shari’a.

Malam Ahmed Abdulkadir, a madadin Matasa Media Links, ya jaddada cewa ci gaban fasaha, musamman AI da kafafen sada zumunta, ba za a iya dakatarwa ba a rayuwar zamani. Ya lura cewa kotunan magistoci yanzu suna yawan fuskantar shari’o’i da s**a shafi lafiyar mutum a yanar gizo, satar bayanai, karya sunaye, zamba ta dijital, da canza abubuwan bidiyo da sauti.

Zaman horo ya kunshi, Professor Mainasara Kurfi ya tattauna yadda jami’an shari’a za su kula da ayyukansu a yanar gizo, amfani da asusun hukuma da na kashin kai, da kyawawan hanyoyi wajen kiyaye gaskiya, sirri, da amincewar jama’a.

Injiniya Abbas Abdullahi ya gabatar da takarda kan AI, inda ya nuna haɗarin deepfakes, kwaikwayon murya, da yin karya da taimakon AI, tare da jaddada bukatar ƙwararru wajen tantance hujjojin dijital.

Taron ya ƙare da bayar da takardun shaidar halarta, sannan mahalarta sun nuna farin ciki da horon, inda s**a ce zai taimaka wajen ƙara ingancin aikinsu da bayar da adalci a Jihar Katsina.

WATA SABUWA: Wani Mai Harkar Haƙar Ma’adinai Ya Karyata Zargin Hukumar NSCDC Kan Yin Haƙar Ba Bisa Ƙa’ida Ba a AbujaWani...
05/01/2026

WATA SABUWA: Wani Mai Harkar Haƙar Ma’adinai Ya Karyata Zargin Hukumar NSCDC Kan Yin Haƙar Ba Bisa Ƙa’ida Ba a Abuja

Wani ɗan kasuwa a fannin haƙar ma’adinai da ke Abuja, Dahiru Salihu, wanda aka fi sani da Mundasa, ya ƙaryata zargin da rundunar Mining Marshals ƙarƙashin Hukumar Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC) ta yi masa, na cewa yana aikata haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.

Kwamandan rundunar Mining Marshals a Babban Birnin Tarayya, John Attah, ya zargi Salihu, wanda shi ne mamallakin kamfanin Mundasa Global Limited, da yin ayyukan haƙar ma’adinai ba bisa doka ba, tare da amfani da sunan NSCDC.

Sai dai Salihu, a wata sanarwa da ya bai wa Peoples Gazette a ranar Lahadi, ya ce shi sanannen mai haƙar ma’adinai ne, kuma dukkan takardunsa na aiki suna nan daidai tare da sahalewar hukumomin da s**a dace a Najeriya.

Ya zargi NSCDC da rashin bin ƙa’ida, yana mai cewa ba a taɓa gayyatarsa ko aika masa da wata wasiƙa ba kafin a ayyana shi a matsayin wanda ake nema.

“Babu wanda ya kira ni. Babu wanda ya gayyace ni ko ya aika min da wasiƙa,” in ji Salihu.

Rahotanni sun nuna cewa rundunar Mining Marshals ta k**a wasu ma’aikatan Salihu guda biyar a ranar 27 ga Disamba, 2025, a Kebi Mangoro, ƙaramar hukumar Kuje, bisa zargin haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba da kuma kwaikwayon jami’an tsaro.

Waɗanda aka k**a sun haɗa da: Muhammed Aliyu (39), Abdulrahman Hashimu (32), Tahir Muhammed (43), Awaje Abduljalal (19), da Kabiru Adamu (38).

Kwamandan rundunar, Mr Onoja, ya ce amfani da motar Hilux mai tambarin NSCDC da ake zargin an yi, na iya barazana ga amincewar jama’a da tsaron ƙasa.

A nasa ɓangaren, lauyan Salihu, Douglas Najime, ya musanta dukkan zarge-zargen, yana mai bayyana cewa motar da ake magana a kanta an bayar da ita ne a matsayin gudummawa ga NSCDC, kuma wani jami’in hukumar ne ya tuka ta ba tare da izini ko rakiyar jami’an da aka ɗora mata ba.

Lauyan ya ƙara da cewa ya tattauna da kwamandan Mining Marshals sau da dama kan lamarin, amma ba a taɓa neman Salihu ya bayyana ba, yana mai jaddada cewa har yanzu abokin aikinsa yana nan a wurin aikinsa..

WATA SABUWA: Bayan Bata Suna da Jingina Aikin Zamba cikin Aminci, Tsohon Ministan Shari’a Malami Ya Zargi EFCC da Sauya ...
30/12/2025

WATA SABUWA: Bayan Bata Suna da Jingina Aikin Zamba cikin Aminci, Tsohon Ministan Shari’a Malami Ya Zargi EFCC da Sauya Tuhuma a Kotu

Tsohon Ministan Shari’a na Tarayya, Abubakar Malami, SAN, ya bayyana damuwarsa kan yadda hukumar EFCC ta yada zarge-zarge masu tsanani a kafafen watsa labarai kafin a fara shari’a, inda ya ce an yi masa “trial by media”.

Malami ya ce, zarge-zarge irin su tallafawa ta’addanci, bacewar triliyoyin naira daga kudaden Abacha, da satar dala biliyan 67 a kan abin da ake kira “golden crude” sun ɓace lokacin da aka kai lamarin kotu, inda yanzu ake tuhumar sa ne kawai kan laifin wanke kudade da wasu abokan aikinsa.

Ya kara da cewa, wannan sauyin tuhuma daga manyan zarge-zargen da aka yada zuwa tuhuma mai sauki yana nuna son zuciya da amfani da shari’a a matsayin makami na siyasa, kuma ya jaddada cewa yanzu lokaci ne na neman gaskiya ta hanyar kotu, ba ta kafafen watsa labarai ba.

DA DUMI-DUMI: Shugaba Tinubu ya ba wa daraktan Farin Kaya DSS lambar yabo bisa kare ‘yancin ‘yan jarida a NajeriyaShugab...
22/12/2025

DA DUMI-DUMI: Shugaba Tinubu ya ba wa daraktan Farin Kaya DSS lambar yabo bisa kare ‘yancin ‘yan jarida a Najeriya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Darakta-Janar na Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), Adeola Oluwatosin Ajayi, murna bisa samun lambar yabo ta girmamawa daga Kwamitin Najeriya na International Press Institute (IPI), wadda ta karrama shi bisa jajircewarsa wajen kare ‘yancin ‘yan jarida a Najeriya.

An bai wa Ajayi wannan lambar yabo ne a Taron Shekara-shekara na IPI Najeriya da aka gudanar a ranar 2 ga Disamba, 2025, a birnin Abuja, inda aka yaba masa bisa kyakkyawar mu’amala da kafafen yaɗa labarai tun bayan naɗa shi Darakta-Janar na DSS.

A cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Lahadi, Shugaba Tinubu ya bayyana jin daɗinsa kan wannan karramawa, yana mai yabawa Ajayi bisa mutunta ‘yancin faɗar albarkacin baki, kare haƙƙin ‘yan ƙasa, da kuma tafiyar da ayyukan DSS bisa doka da oda.

Shugaban ƙasa ya ce a ƙarƙashin jagorancin Ajayi, DSS ta fara sauya tsohon hotonta na gaba da ‘yan jarida, inda a yanzu hukumar ke fifita tattaunawa, fahimtar juna da haɗin kai maimakon takaddama. Tinubu ya kuma ƙarfafa sauran hukumomin tsaro da su ɗauki kafafen yaɗa labarai a matsayin abokan aiki, ba abokan gaba ba, bisa rawar da kundin tsarin mulki ya ba wa manema labarai na sa ido kan masu mulki.

A nata ɓangaren, IPI Najeriya ta ce tun bayan naɗa Ajayi a watan Agusta 2024, ya nuna ƙwarewa, kamun kai da buɗaɗɗen zuciya wajen mu’amala da ‘yan jarida, inda rikice-rikice da dama ke warwarewa ta hanyar tattaunawa maimakon amfani da ƙarfi. Kungiyar ta ce karramawar ba yabo kaɗai ba ce, illa ƙarfafa shi ya ƙara ƙoƙari tare da zama abin koyi ga sauran jami’an tsaro.

Sai dai kuma, ƙungiyoyin kare ‘yancin faɗar albarkacin baki sun nuna damuwa kan ƙaruwa hare-hare da tsangwama ga ‘yan jarida a sassa daban-daban na ƙasar. Rahoton CJID Openness Index ya nuna an samu lamura 48 na tauye ‘yancin ‘yan jarida daga Disamba 2023 zuwa Nuwamba 2024, inda aka danganta yawancin su da jami’an tsaro a jihohi da Babban Birnin Tarayya.

Da yake mayar da martani, Ajayi ya sake jaddada ƙudirin DSS na kare ‘yan jarida, yana mai cewa hukumar za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau da zai ba su damar gudanar da aikinsu yadda ya k**ata, bisa manufar Shugaba Tinubu ta kare dukkan ‘yan Najeriya ba tare da nuna bambanci ba. Ya ƙara da cewa DSS na ci gaba da tattaunawa da shugabannin sauran hukumomin tsaro domin fifita kare ‘yan jarida a faɗin ƙasar.

A gefe guda kuma, IPI Najeriya ta bayyana cewa ta sanya wasu jami’ai a cikin “littafin baƙi” bisa zargin tauye ‘yancin ‘yan jarida. Daga cikin su akwai Gwamnan Jihar Niger, Mohammed Bago, Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Egbetokun, da Gwamnan Akwa Ibom, Umo Eno. IPI ta ce wasu daga cikinsu sun fara tattaunawa domin cire sunayensu, yayin da wasu ke ƙin amincewa da bita ko gyara.

IPI ta kammala da cewa karrama Daraktan DSS na nuna sabon salo na girmama ‘yancin ‘yan jarida a Najeriya, tare da fatan sauran hukumomin tsaro da na gwamnati za su bi wannan tafarki domin ƙarfafa dimokuraɗiyya da walwalar aikin jarida a ƙasar.

DA DUMI-DUMI: Asirin EFCC da Malami Ya Fallasa Ya Haifar da Rikicin Ramuwar Gayya A KansaHukumar Yaƙi da Cin Hanci da Ra...
21/12/2025

DA DUMI-DUMI: Asirin EFCC da Malami Ya Fallasa Ya Haifar da Rikicin Ramuwar Gayya A Kansa

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (EFCC) na fuskantar zargi da gudanar da ramuwar gayya ta kashin kai kan tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a na Ƙasa, Abubakar Malami, SAN, biyo bayan fitar da wata sanarwa da ya yi dangane da Babi na 9 na Rahoton Kwamitin Binciken Shari’a karkashin jagorancin Mai Shari’a Ayo Salami.

Rahoton, wanda aka ce an rufe shii tsawon lokaci, na zargin Shugaban EFCC, Ola Olukoyede, da aikata laifuffukan almundahana ta kuɗi da cin zarafin ofis. Ofishin Malami ya bayyana cewa samamen da EFCC ta kai kwanan nan kan ofisoshinsa da gidajensa na sirri da ke Abuja da Jihar Kebbi, martani ne kai-tsaye ga kiran da Malami ya yi na Olukoyede ya janye daga shugabancin EFCC saboda zargin son kai da nuna bangaranci.

Samamen, waɗanda aka ce ba tare da sanarwa ba, sun fi karkata ne wajen neman takardu da s**a shafi Babi na 9 na rahoton, lamarin da ya haifar da damuwa game da tsoratarwa, ramuwar gayya, da barazanar tsaro ga Malami da ma’aikatansa. Ofishin Malami ya bayyana matakin EFCC a matsayin “tsoratarwa da aka tsara tun da fari”, da kuma yunƙurin tozarta gaskiya da hana ta fitowa fili.

Majiyoyi sun ce Babi na 9 na Rahoton Kwamitin Ayo Salami na ƙunshe da manyan zarge-zarge masu nauyi kan Olukoyede, ciki har da cin hanci, amfani da ofis ba bisa ƙa’ida ba, da hana adalci gudana.

Rahoton ya kuma zargi Olukoyede da shiga yarjejeniyoyi masu duhu, ciki har da ba da manyan kwangiloli ga abokansa da ’yan uwansa.

Ofishin Malami ya ce matakan EFCC wani yunƙuri ne na rufe baki da hana shi fitar da cikakken rahoton. “Matakan EFCC hujja ce a sarari cewa suna da abin ɓoyewa,” in ji Mohammed Bello Doka, Mataimakin Malami kan Harkokin Yaɗa Labarai.
“Ba za mu yarda a tsoratar da mu ko a rufe bakinmu ba. Za mu ci gaba da gwagwarmayar gaskiya da rikon amana.”

EFCC ta musanta dukkan zarge-zargen, tana mai cewa samamen wani ɓangare ne na binciken da take gudanarwa kan Malami. Sai dai ofishin Malami ya nuna shakku sosai, yana mai cewa lokacin da aka kai samamen yana da matuƙar alamar tambaya.

“Muna tambayar lokaci da izinin da aka yi amfani da su wajen wadannan binciken,” in ji Doka.
“Me ya sa aka jira sai bayan mun fitar da sanarwarmu kan Babi na 9? Me suke ƙoƙarin ɓoyewa?”

Lamarin ya jawo ƙorafe-ƙorafe daga kungiyoyin farar hula da masu kare haƙƙin ɗan Adam, inda s**a nemi a gudanar da bincike mai zaman kansa kan ayyukan EFCC.

“Wannan bayyanannen cin zarafin iko da tsoratarwa ne,” in ji kakakin Human Rights Writers Association of Nigeria (HURIWA).
“Muna neman Shugaban EFCC ya sauka daga mukaminsa domin a yi bincike cikin adalci.”

Yayin da rikicin ke ƙara k**ari, Malami ya jaddada cewa yana shirye ya fuskanci ingantaccen tsarin doka mai zaman kansa, yana mai cewa tsoratarwa da shari’ar kafafen yaɗa labarai ba za su maye gurbin adalci ba.

Hakan ya kuma haifar da tambayoyi game da ’yancin cin gashin kan EFCC da kuma iya gudanar da bincike cikin adalci.

“Idan aka bar EFCC ta ci gaba da wannan hanya, hakan zai lalata tsarin mulki da amincewar jama’a,” in ji wani babban lauya.

Haka kuma an nuna damuwa kan lafiyar Malami da ma’aikatansa, inda ofishinsa ya ce EFCC za ta ɗauki alhakin duk wani abu da ya same su.

Yayin da rikicin ke ci gaba, ’yan Najeriya na ci gaba da tambaya, “Wane sirri ne EFCC ke ƙoƙarin ɓoyewa a Babi na 9?”

An kuma ƙara kiran Olukoyede ya ajiye mukaminsa, domin bai wa bincike damar gudana cikin adalci.
“Idan babu abin ɓoyewa, ya k**ata ya sauka gefe,” in ji wani fitaccen ɗan siyasa.

Kungiyar Lauyoyin Najeriya (NBA) ma ta soki EFCC, tana zargin ta da cin zarafin iko da take hakkin doka.

A ƙarshe, an bukaci gwamnati ta shiga tsakani domin tabbatar da cewa EFCC ba ta zama kayan tsangwama na siyasa ba.

"Tsawon lokaci har izuwa yau, al’ummar Gwarzo da Kabo sunata kiraye-kiraye Domin nazo nayi takarar ɗan Majalisar tarayya...
15/12/2025

"Tsawon lokaci har izuwa yau, al’ummar Gwarzo da Kabo sunata kiraye-kiraye Domin nazo nayi takarar ɗan Majalisar tarayya na Gwarzo da Kabo, kuma na aminta zanzo mu bada gaggarumar gudunmuwa a Siyasance"

Haka Zalika yace "A yanzu haka, Ina kira ga masoya da sauran al’umma da a maida hankali kan neman haɗin kan jama'a domin shiga jam’iyya kuma a dakatar da duk wani tallan takara saboda a maida hankali wajan haɗa kan al'umma da kuma tsarin shiga jam’iyya har zuwa nan gaba kaɗan da jam’iyya zata karɓe mu a hukumance cikin shekarar nan mai zuwa ta 2026"

Matashin da ya shafe shekaru yana faranta ran al’ummar Gwarzo da Kabo a Jahar Kano, Hon Fahad Dankabo Ya Bayyana haka ne a shafinsa na Facebook a daren jiya.

Inda Ya kara da cewa ya ku Masoyana Masu albarka Ina so a ajjiye maganar takara a gefe, mu shiga jam’iyya da buɗɗiyar zuciya, a ƙulla mu’amala mai kyau da al'ummah, 'yan Jam'iyya kuma mu bada irin gudunmawar mu ta Kowacce fuska.

‘Sannan maganar takara sai wanda Jam’iyya ta tsayar, kuma duk hukunci da Allah ya yanke, mun yarda shi ne mafi alheri garemu da kuma al'ummah.

Zanyi amfani da Wannan damar na sanar da masoya da al’ummah gaba ɗaya cewa ban yarda a zagi wani ko aci mutunci wasu ba a Kowacce Jam'iyya Suke da sunan goyon bayana a faɗin jahar Kano da Najeriya baki ɗaya’

‘A ƙarshe muna addu'ah duk abinda yake alheri ne garemu, da al'ummah, Allah ya zaɓa mana baki ɗaya, Allah ya bamu zaman lafiya mai dorewa a jihar mu Kano da ƙasar mu Najeriya 🇳🇬 baki ɗaya.

YANZU-YANZU: "Ban Yadda Kuci Mutuncin Kowa Ba, Ko Zagin Wani A Kowacce Jam’iyya Yake Da Sunan Goyon Bayana" Gargadin Hon...
15/12/2025

YANZU-YANZU: "Ban Yadda Kuci Mutuncin Kowa Ba, Ko Zagin Wani A Kowacce Jam’iyya Yake Da Sunan Goyon Bayana" Gargadin Hon Fahad Dankabo Ga Masoyansa

Hon Fahad Dankabo Ya fitar da wata sanarwar da dinbin masoyansa ke jiran ji daga garesa, inda Ya ce "Tsawon lokaci har izuwa yau, al’ummar Gwarzo da Kabo sunata kiraye-kiraye Domin nazo nayi takarar ɗan Majalisar tarayya na Gwarzo da Kabo, kuma na aminta zanzo mu bada gaggarumar gudunmuwa a Siyasance"

Haka Zalika yace "A yanzu haka, Ina kira ga masoya da sauran al’umma da a maida hankali kan neman haɗin kan jama'a domin shiga jam’iyya kuma a dakatar da duk wani tallan takara saboda a maida hankali wajan haɗa kan al'umma da kuma tsarin shiga jam’iyya har zuwa nan gaba kaɗan da jam’iyya zata karɓe mu a hukumance cikin shekarar nan mai zuwa ta 2026"

Matashin da ya shafe shekaru yana faranta ran al’ummar Gwarzo da Kabo a Jahar Kano, Hon Fahad Dankabo Ya Bayyana haka ne a shafinsa na Facebook a daren jiya.

Inda Ya kara da cewa ya ku Masoyana Masu albarka Ina so a ajjiye maganar takara a gefe, mu shiga jam’iyya da buɗɗiyar zuciya, a ƙulla mu’amala mai kyau da al'ummah, 'yan Jam'iyya kuma mu bada irin gudunmawar mu ta Kowacce fuska.

‘Sannan maganar takara sai wanda Jam’iyya ta tsayar, kuma duk hukunci da Allah ya yanke, mun yarda shi ne mafi alheri garemu da kuma al'ummah.

Zanyi amfani da Wannan damar na sanar da masoya da al’ummah gaba ɗaya cewa ban yarda a zagi wani ko aci mutunci wasu ba a Kowacce Jam'iyya Suke da sunan goyon bayana a faɗin jahar Kano da Najeriya baki ɗaya’

‘A ƙarshe muna addu'ah duk abinda yake alheri ne garemu, da al'ummah, Allah ya zaɓa mana baki ɗaya, Allah ya bamu zaman lafiya mai dorewa a jihar mu Kano da ƙasar mu Najeriya 🇳🇬 baki ɗaya.

Nagode! Nagode!
Daga Ɗanku, Ɗan Uwanku, Fahad Muhammad Dankabo

WATA SABUWA: Tsohon Ministan Shari'a Malami Ya Zargi Hukumar EFCC da Hana Shi Cika Sharudan BelinOfishin tsohon Antoni-J...
14/12/2025

WATA SABUWA: Tsohon Ministan Shari'a Malami Ya Zargi Hukumar EFCC da Hana Shi Cika Sharudan Belin

Ofishin tsohon Antoni-Janar na Ƙasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN, ya bayyana cewa tsohon ministan ya shirya tsaf domin cika dukkan sharuɗɗan bel da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC ta gindaya masa, sai dai ya zargi hukumar da hana shi damar yin hakan kafin a tsare shi.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa ga manema labarai da Mohammed Bello Doka, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai ga Malami, ya sanya wa hannu, a matsayin martani ga sanarwar EFCC dangane da tsare Malami da batun bel dinsa.

Ofishin Malami ya jaddada cewa tsohon ministan ɗan ƙasa ne mai bin doka, wanda tun farko ya nuna haƙuri, haɗin kai da girmama hukumomin gwamnati, tare da bayyana cewa ba shi da wata niyya ta gujewa bincike.

Sanarwar ta ce, sabanin yadda EFCC ta nuna, Malami bai ƙi sharuɗɗan bel ba, kuma da zarar aka sanar da shi sabbin sharuɗɗan, ya bayyana a fili cewa a shirye yake ya cika su gaba ɗaya. Sai dai ofishinsa ya ce ba a ba shi isasshen lokaci ko dama ba kafin a tsare shi, lamarin da ya sa aka kira zargin rashin bin bel a matsayin bayani mara inganci.

Dangane da sharuɗɗan bel, ofishin Malami ya nuna damuwa kan buƙatar da EFCC ta shimfiɗa na kawo sakatarorin dindindin biyu masu aiki a gwamnati, waɗanda ke da gidaje a Abuja, su tsaya masa a matsayin masu garantin bel. A cewar sanarwar, wannan sharaɗi na jefa manyan jami’an gwamnati cikin yanayi na rikici da barazana, ganin cewa ana naɗa su ne ƙarƙashin gwamnatin da EFCC ke aiki a ƙarkashinta.

Sanarwar ta tambayi ko an shimfiɗa irin wannan sharaɗi ne da gaske domin a cika shi, ko kuwa an tsara shi ne domin hana bel da tsawaita tsarewa.

Har ila yau, ofishin Malami ya bayyana cewa har yanzu ba a sanar da shi wata tak**aiman tuhuma a rubuce ba, inda ya ce ba a miƙa masa wata ƙara, rahoton bincike, ko takardar tuhuma da ke nuna laifi da doka ta sani.

Sanarwar ta jaddada cewa bel na wucin-gadi bai k**ata ya zama hanyar hukunta mutum ko tsare shi ba tare da shari’a ba, tana mai cewa ci gaba da tsare wanda ya nuna shirinsa na bin sharuɗɗan bel yana tauye tanadin kundin tsarin mulki.

Dangane da batun siyasa, ofishin Malami ya ce bai zargi EFCC da siyasantar da lamarin ba, amma ya tsaya kan cewa lokutan janye bel da tsare shi sun haifar da tambayoyi, tare da jaddada cewa shiga harkokin siyasa bisa doka haƙƙi ne na kundin tsarin mulki.

A ƙarshe, Malami ya sake nanata aniyarsa ta cika sharuɗɗan bel idan aka ba shi dama, yin cikakken haɗin kai da EFCC, da kuma miƙa kansa gaban kotu idan aka shigar da tuhuma. Ofishinsa ya buƙaci hukumar da ta kammala bincike cikin gaggawa ko ta miƙa lamarin gaban kotu domin doka ta yi aikinta.

TIRKASHI: EFCC ta Ƙirƙiri Karya Don Batawa Tsohon Ministan Shari'a Abubakar Malami Suna, - In Ji Ofishin MalamiOfishin t...
13/12/2025

TIRKASHI: EFCC ta Ƙirƙiri Karya Don Batawa Tsohon Ministan Shari'a Abubakar Malami Suna, - In Ji Ofishin Malami

Ofishin tsohon Babban Lauyan Ƙasa (AGF) kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN, ya ƙaryata zargin da ke yawo a kafafen yaɗa labarai cewa yana da asusun banki 46 a sunansa, yana mai bayyana zargin a matsayin ƙarya kuma marar hujja.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Mohammed Bello Doka, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, ya fitar a madadin ofishin Malami, inda ya ce rahotannin sun dogara ne kan majiyoyi marasa tushe da ake dangantawa da Hukumar EFCC, ba tare da wata sanarwa ta hukuma ko hujja ba.

Sanarwar ta bayyana cewa Abubakar Malami, SAN, na da asusun banki guda shida (6) kacal, kuma dukkan su, an bayyana su a cikin bayanin kadarorinsa na doka, hukumomin da s**a dace, ciki har da EFCC, sun san da su, kuma suna bin dukkan ka’idojin kuɗi da dokokin ƙasa.

Ofishin ya ƙara da cewa Malami bai taɓa mallakar asusun banki 46 ba, kuma har zuwa yanzu EFCC ba ta taɓa sanar da shi a hukumance kan irin wannan zargi ta hanyar doka ba.

Domin tabbatar da gaskiya da amincewar jama’a ga hukumomin yaƙi da cin hanci, ofishin Malami ya kalubalanci EFCC da ta fito fili ta, bayyana aƙalla asusun banki 23 (kashi 50% na 46) da ake zargin na Malami ne; ko kuma ta janye ko ta musanta zargin “asusun banki 46” a sarari.

Sanarwar ta jaddada cewa bayani daga majiyoyi marasa tushe da yayata jita-jita a kafofin watsa labarai ba zai maye gurbin hujjar doka ba.

Abubakar Malami, SAN, ya sake nanata cewa bai aikata wani laifin kuɗi ba, ciki har da batun kadarorin da aka kwato k**ar na Abacha, kuma a shirye yake ya ba da cikakken haɗin kai ga kowanne bincike na doka, mai gaskiya da adalci.

Ofishin ya gode wa magoya baya da ‘yan Najeriya masu fatan alheri, tare da kira ga jama’a da su kwantar da hankali, su bi doka, su kuma guji yaɗa jita-jita, har sai gaskiya ta bayyana.

Sanarwar ta ƙare da jaddada kudirin ofishin na gaskiya, riƙon amana da tattaunawa mai alhaki a bainar jama’a.

TIRKASHI: EFCC Ta Tsare Malami Ba Tare da Kamasa Da Laifin Komai Ba Bayan Ya Halarci Wani Taron Siyasa a Kebbi — Inji La...
12/12/2025

TIRKASHI: EFCC Ta Tsare Malami Ba Tare da Kamasa Da Laifin Komai Ba Bayan Ya Halarci Wani Taron Siyasa a Kebbi — Inji Lauyoyinsa

Sabbin sanarwar manema labarai guda biyu da Mohammed Bello Doka, Mai Magana da Yawa ga tsohon Attorney-General na Tarayya, Abubakar Malami, SAN, ya fitar sun jefa wa EFCC tambayoyi game da tsare Malami ba tare da an gurfanar da shi ko tuhumarsa da wani laifi ba.

A cewar sanarwar, har yanzu EFCC ba ta miƙa wa Malami wani korafi, takardar bincike ko takardar tuhuma ba. Duk da cewa an saka wasu zarge-zargen “alleged financial misconduct” a cikin takardun belinsa, lauyoyinsa, ƙarƙashin Barrister Mohammed Sherrif Elhissain, sun ce babu ko ɗaya daga cikin waɗannan da aka gabatar masa a matsayin laifin da doka ta tanada.

Sanarwar ta ce an 4 belin Malami ne kawai saboda ya halarci wani taron siyasa cikin lumana a jihar Kebbi, inda ya gaishe da magoya baya. Daga dawowarsa Abuja a kan umarnin EFCC, aka tsare shi kai tsaye.

Lauyoyinsa sun bayyana cewa tun da farko EFCC ta saka sharadin hana Malami duk wata mu'amala ta siyasa musamman a Kebbi, abin da s**a ayyana a matsayin haramtacciyar doka da kuma yunƙurin danne karfinsa a siyasa.

Duk da cewa yana kan sahihin belin da bai karye ba, EFCC ta sake saka sabon sharadi: sai ya samo manyan sakatarori biyu da ke da filaye ko kadarori a Abuja. Sanarwar ta yi zargin cewa waɗannan sharudda sun yi ne don a hana shi samun beli.
Haka nan, har yanzu ana tsare da shi ba tare da umarnin kotu ba, ba tare da aikata babban laifi ba, kuma ba tare da an fayyace masa abin da ake zarginsa da shi ba, abin da lauyoyinsa s**a ce keta dokar ACJA da kundin tsarin mulki ne.

A bisa tanadin sashi na 32 na ACJA, tawagar lauyoyin Malami ta garzaya kotun koli tana neman ta duba yadda aka tsare shi tare da bada belin da ya dace muddin ba a gurfanar da shi a kotu ba. Sun ce Malami ya yi cikakken hadin kai da bincike, bai da wani laifi da aka tabbatar, kuma ba zai gudu ko'ina ba tunda fasfo nasa yana hannun EFCC.

Address

Gaida Makada Layina Taransufuma
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SHURA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share