13/06/2026
WATA SABUWA: Duk Wanda Ya Ce Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro Bai Ma San Mene Ne Tsaro Ba, Allah Ne Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Najeriya, In Ji Ministan Tsaro
Ƙaramin Ministan Tsaron Najeriya, Bello Muhammad Matawalle, ya zargi wasu ƴan adawa da siyasantar da matsalar tsaro ta hanyar yaɗa bayanan ƙarya, ciki har da tsofaffin bidiyoyi na lokacin Jonathan da na ƙasashen da ke cikin tashin hankali irin su Mali da Burkina-Faso amma ake danganta su da gwamnatin Tinubu a yanzu, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.
A cewarsa, matsalar tsaro a Najeriya ba abu ne da za a iya kawo ƙarshenta a lokaci guda ba, yana mai cewa hatta ƙasashe masu ci gaba na fuskantar irin wannan ƙalubale. "Allah ne kaɗai zai iya kawo ƙarshen matsalar tsaro a Najeriya", Ya ce.
Ministan ya kuma ƙara da cewa gwamnati tana ci gaba da ɗaukar matakai domin inganta tsro da walwalar jami’an tsaro, ciki har da ƙarin albashi, inganta fansho da giratuti, da kuma biyan alawus-alawus a kan lokaci, "mun ba wa jami'an tsaro umarni duk inda s**a ga ɗan'ta'adda su hallaka shi". In ji shi.