Arewa Pulse

Arewa Pulse Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Arewa Pulse, Digital creator, Kano.

📰 Labarai Masu Zafi
⚽ Wasanni
🎬 Entertainment
🌍 Trending Stories
📢 Sahihan Labarai Cikin Gaggawa
💬 Mu na son jin ra'ayinku a kowane labari.
❤️ Follow Domin Kada Ka Rasa Sabbin Updates!

Jama'a A Kula 😢
04/08/2026

Jama'a A Kula 😢

JAMA'A A YI HATTARA DA SABUWAR DABARAR BARAYIN BABURA!

Ana samun rahotannin cewa wasu barayin babura sun bullo da wata sabuwar hanya ta yaudarar mutane.

Daga misalin 10:00 na dare zuwa tsakar dare, s**an je tsakiyar hanya su zubar da kuɗi k**ar N10,000 ko fiye domin su ja hankalin masu wucewa.

Da zarar mutum ya tsaya domin ɗaukar kuɗin, sai su fito ba-zata su kai masa hari da sara, duka ko kwace dukiyarsa. A wasu lokuta ma lamarin kan kai ga rasa rai.

⚠️ Idan ka ga kuɗi a tsakar hanya musamman cikin dare, ka guji tsayawa domin ɗauka. Rayuwarka ta fi kowace dukiya muhimmanci.

📢 A taimaka a yaɗa wannan saƙo domin wayar da kan jama'a. Idan ka ga wani abu mai k**a da haka, ka sanar da jami'an tsaro mafi kusa.

An Hango Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II Tare da Abokan Karatunsa na Makarantar Lauya Yayin da Suke Jiran Fara Darasi a ...
04/08/2026

An Hango Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II Tare da Abokan Karatunsa na Makarantar Lauya Yayin da Suke Jiran Fara Darasi a Jami'ar Northwest

An hangi Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, tare da abokan karatunsa na Makarantar Lauya yayin da suke jiran fara darasi a Jami'ar Northwest.

Lamarin ya ja hankalin mutane da dama, inda wasu s**a yaba da yadda Sarkin ya kasance cikin sauƙi da tawali'u, yana zama tare da sauran ɗalibai ba tare da nuna bambanci ba.

💬 Me kake gani a wannan hoto? Shin wannan alama ce ta tawali'u da ƙarfafa ilimi?

🚨 Direban Adaidaita Sahu Ya Buge K**aye Na Dadin Kowa, Ya Tsere Daga Wurin HatsarinAn shiga jimami bayan da wani direban...
03/08/2026

🚨 Direban Adaidaita Sahu Ya Buge K**aye Na Dadin Kowa, Ya Tsere Daga Wurin Hatsarin

An shiga jimami bayan da wani direban Adaidaita Sahu ya buge K**aye Na Dadin Kowa, lamarin da ya yi sanadin karyewar ƙafarsa.

Rahotanni sun ce direban ya tsere daga wurin bayan hatsarin. K**aye ya bayyana cewa ba zai yafe masa ba har sai ya zo da kansa ya nemi afuwa.

Iyalan K**aye sun roƙi al'umma da su yi masa addu'ar samun lafiya, tare da neman duk mai bayani kan direban ya sanar da hukumomin da abin ya shafa.

💬 Me kake ganin ya k**ata a yi wa direban da ya gudu bayan haddasa hatsari?

🚨 Adam A. Zango Ya Kafa Tarihi A Zauren Jita? Ko Akwai Wani Sirri A Bayan Lamarin? 🤯Kasa da kwanaki uku kacal, hirar da ...
02/08/2026

🚨 Adam A. Zango Ya Kafa Tarihi A Zauren Jita? Ko Akwai Wani Sirri A Bayan Lamarin? 🤯

Kasa da kwanaki uku kacal, hirar da aka yi da Adam A. Zango a shirin Zauren Jita ta kai views 146,000, abin da ya sa ta zama hirar da aka fi kallo a tashar tun bayan da Ali Jita ya ƙaddamar da ita shekaru 6 da s**a gabata.

Abin mamaki shi ne, duk da cewa tashar Zauren Jita TV ba ta kai mabiya 40,000 ba, bidiyon ya samu wannan gagarumin yawan kallo cikin ɗan lokaci.

Wannan ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin masu bibiyar Kannywood, inda wasu ke cewa sunan Adam A. Zango ne ya ja hankalin jama'a, yayin da wasu ke ganin batutuwan da aka tattauna ne s**a sa mutane s**a yi tururuwa domin kallon hirar.

🔥 Shin Adam A. Zango ne kaɗai jarumin da zai iya karya duk wani tarihi a Kannywood, ko kuwa akwai wani dalili daban?

29/07/2026

Abar Zugani 🤣.

Gibin Gidajen Najeriya Ya Kai Miliyan 15Abuja – Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa gibin gidaje a Najeriya ya kai kimanin...
28/07/2026

Gibin Gidajen Najeriya Ya Kai Miliyan 15

Abuja – Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa gibin gidaje a Najeriya ya kai kimanin miliyan 15, tare da amincewa da sabbin ƙa'idojin duniya domin jagorantar manufofin samar da gidaje masu araha.

Gwamnatin ta ce sabon tsarin zai taimaka wajen inganta shirye-shiryen samar da gidaje da kuma sauƙaƙa wa 'yan Najeriya samun matsuguni masu sauƙin biya.Shin gwamnati za ta iya magance ƙarancin gidaje? 🤔👇

Jihar Oyo Ta Karɓi Jiragen Sa Ido BiyuIbadan – Gwamnatin Jihar Oyo ta karɓi jiragen sa ido guda biyu domin ƙarfafa sa id...
28/07/2026

Jihar Oyo Ta Karɓi Jiragen Sa Ido Biyu

Ibadan – Gwamnatin Jihar Oyo ta karɓi jiragen sa ido guda biyu domin ƙarfafa sa ido ta sama, tattara bayanan sirri da kuma inganta saurin mayar da martani kan matsalolin tsaro.

An bayyana cewa jiragen za su taimaka wa hukumomin tsaro wajen inganta ayyukan tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al'umma a faɗin jihar.

Shin jiragen sa ido za su magance matsalar tsaro? 🤔👇

RUNDUNAR SOJIN RUWA TA K**A JIRGIN DA KE ƊAUKE DA DANYEN MAI NA SAMA DA NAIRA MILIYAN 660 DA AKE ZARGIN AN SATAAbuja – R...
28/07/2026

RUNDUNAR SOJIN RUWA TA K**A JIRGIN DA KE ƊAUKE DA DANYEN MAI NA SAMA DA NAIRA MILIYAN 660 DA AKE ZARGIN AN SATA

Abuja – Rundunar Sojin Ruwan Najeriya ta sanar da k**a wani jirgin ruwa da ake zargin yana ɗauke da danyen mai da aka sace, wanda darajarsa ta haura Naira miliyan 660.

A cewar rundunar, an kuma k**a ma'aikatan jirgin guda 12 da ake zargi da hannu a safarar danyen man.

Hukumomin tsaro sun ce ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano yadda aka samu danyen man da kuma cafke duk wasu da ke da hannu a lamarin.

Rundunar ta jaddada kudirinta na ci gaba da yaƙi da satar danyen mai da sauran ayyukan haramtattu a yankunan ruwa na.

A ra'ayinka, me ya sa har yanzu ana ci gaba da satar danyen mai duk da tsauraran matakan tsaro? Wa kake ganin ya k**ata a ɗora wa alhakin wannan matsala? 🤔👇

RAHOTO: Najeriya Ta Zama Ta Huɗu a Afirka Wajen Yawan Attajiran Dala Miliyan ƊayaAbuja – Wani rahoto ya nuna cewa Najeri...
28/07/2026

RAHOTO: Najeriya Ta Zama Ta Huɗu a Afirka Wajen Yawan Attajiran Dala Miliyan Ɗaya

Abuja – Wani rahoto ya nuna cewa Najeriya ce ta huɗu a nahiyar Afirka wajen yawan mutanen da darajar dukiyarsu ta kai akalla dala miliyan ɗaya.

Rahoton ya bayyana cewa akwai kimanin mutane 7,200 a Najeriya da kadarorinsu s**a kai ko s**a haura dala miliyan ɗaya, lamarin da ya sanya ƙasar ta kasance ta huɗu a jerin ƙasashen Afirka masu yawan attajiran dala.

Bayanan sun nuna cewa duk da ƙalubalen tattalin arzikin da ƙasar ke fuskanta, Najeriya na ci gaba da kasancewa cikin manyan ƙasashen da ke da attajirai masu tarin dukiya a nahiyar Afirka.

A ra'ayinka, me ya sa duk da yawan attajirai a Najeriya, har yanzu talauci ke ci gaba da ƙaruwa? Shin matsalar rabon arziki ce ko kuma tsarin tattalin arziki? 🤔👇

Daga Sani Muhammad ✍️

SHARI'AR KISAN MATA DA ƳAƳANTA SHIDA A ƊORAYI: Wanda Ake Tuhuma Ya Amince Da Wani Kisan, Ya Nemi A K**a Boka ThomasKano ...
28/07/2026

SHARI'AR KISAN MATA DA ƳAƳANTA SHIDA A ƊORAYI: Wanda Ake Tuhuma Ya Amince Da Wani Kisan, Ya Nemi A K**a Boka Thomas

Kano – An ci gaba da sauraron shari'ar kisan matar aure da 'ya'yanta shida a unguwar Ɗorayi da ke Jihar Kano, inda wanda ake tuhuma, Umar Auwalu, ya gabatar da bayanansa a gaban kotu.

Yayin da yake kare kansa, Umar ya shaida wa kotu cewa wani boka mai suna Thomas ne ya rinjaye tunaninsa har ya aikata laifukan da ake zarginsa da su.

A cewarsa, tun farko ya je wajen bokan ne domin neman taimako kan harkokin sana'arsa da kuma rayuwarsa, amma daga baya ya fara shiga ƙarƙashin tasirin bokan.

Umar ya kuma roƙi kotu da ta bayar da umarnin kamo Boka Thomas domin gudanar da bincike tare da hukunta shi idan aka same shi da laifi. Ya ce, a fahimtarsa, hukunta bokan na da muhimmanci wajen dakile aukuwar irin waɗannan laifuka a nan gaba.

Har ila yau, wanda ake tuhumar ya yi ikirarin alaƙanta kansa da wani kisan da ya faru a Tudun Yola, inda ya ce Hauwa'u da Zahra'u s**a rasa rayukansu.

A cewarsa, Hauwa'u ƙanwar mahaifiyarsa ce. Ya bayyana cewa bayan ta buɗe masa ƙofa, wani yanayi ya sauya masa tunani, lamarin da ya kai ga kai hari kan mutanen da ke cikin gidan.

Ya kuma shaida wa kotu cewa daga bisani ya banka wa gidan wuta, tare da ɗaukar waya, kuɗi da ya ce sun kai naira dubu ɗari uku, da wasu kayayyaki kafin ya bar wurin.

Ana ci gaba da sauraron shari'ar, kuma kotu ce za ta tantance hujjoji da dukkan bayanan da aka gabatar kafin yanke hukunci.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Pulse posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share