Yakubu M Ibrahim

Yakubu M Ibrahim Journalism // Current Affairs // Media Consultant // Digital Skill and Islamic Videos update
(8)

(Minhaj al-Muslim) wanda Sheikh Abu Bakr Jabir Al-Jazairi ya rubutaShekara 12 da s**a wuce Baban mu Allah yagafarta masa...
01/11/2025

(Minhaj al-Muslim) wanda Sheikh Abu Bakr Jabir Al-Jazairi ya rubuta
Shekara 12 da s**a wuce Baban mu Allah yagafarta masa ya bani shi Yana Daga Cikin muhimman litattafa da Mahaifina ya Dauka ya bani dakansa

Littafin Minhaj-Muslim yana koyar da cikakken tsarin rayuwa na Musulmi daga dukkan fannoni — addini, zamantakewa, da ɗabi’a.

1. Aƙeeda (I'tiqad) – Yana koyar da imani da Allah, mala’iku, littattafai, annabawa, ranar lahira, da kaddara.
2. ‘Ibadat (Ibada) – Yana bayyana sallah, zakka, azumi, hajji, da sauran ibadodi cikin sauƙi.

3. Akhlaq (Hali da ɗabi’u) – Yana koyar da kyawawan halaye, kamar gaskiya, tawali’u, haƙuri, da adalci.

4. Mu’amalat (Mu’amala) – Yana bayani kan mu’amalar yau da kullum, kamar kasuwanci, aure, ma’amala da mutane, da adalci.

5. Adab (Ladabi da Hanyoyin Zamani) – Yana nuna yadda musulmi zai rayu da mutane cikin ladabi da hikima a duk inda yake.

Manufar Littafin:
Sheikh Al-Jazairi ya rubuta shi ne domin ya zama jagora mai sauƙin fahimta ga duk musulmi — ko malami ne, ko ɗalibi, ko talaka — domin ya san yadda zai yi rayuwa bisa tafarkin Musulunci na gaskiya.
Sannan Wannan Littafi yayi Cikakken Bayani akan Zamantakewar Aure

A takaice:
Minhaj al-Muslim” yana koyar da cikakken tsarin rayuwa na musulmi daga akida har zuwa mu’amala, yana mai da hankali sosai wajen tarbiyya da tsaftar zuciya tare da fahimtar shari’a cikin sauƙi.

'Yan'uwa na Matasa mu Nemi Ilimi na Gaske
Mu Koma gun Malaman mu na gida Masu Sahihiyar Karantawa Ilimin ka Shine ke doraka Akan akidar da ta Dace
Allah Yajikan iyayen mu
Allah yasa mu wanye Lafiya.

Yakubu M Ibrahim ✍️

Zan Shiga Kungiyar Masu kwaikwayon Manyan Mutane Amma Ni Zan dauki role din kwaikwayon Mentor Namu Professor Isa Ali Pan...
31/10/2025

Zan Shiga Kungiyar Masu kwaikwayon Manyan Mutane
Amma Ni Zan dauki role din kwaikwayon Mentor Namu Professor Isa Ali Pantami
Ya kuke Gani 😄?

31/10/2025
Ministan Abuja, Nyesom Wike, Tare Da Ƙaramar Ministar Harkokin Haɗin Gwiwa Na Ƙasashen Duniya Ta Hadaddiyar Daular Larab...
30/10/2025

Ministan Abuja, Nyesom Wike, Tare Da Ƙaramar Ministar Harkokin Haɗin Gwiwa Na Ƙasashen Duniya Ta Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Reem bint Ebrahim Al Hashimy, Yayin Taron Biranen Asiya Dake Maƙwabtaka Da Tekun Pasifik Na 2025 da aka gudanar a birnin Dubai.

Hotunan taron Manchester na Convention wanda Professor Isa Ali Pantami  Ya zama Jeynote Speaker akan topic: Ethical Digi...
27/10/2025

Hotunan taron Manchester na Convention wanda Professor Isa Ali Pantami Ya zama Jeynote Speaker akan topic: Ethical Digital Economy: The Future of Community-Centred Islamic Digital Banking.
Taron an gabatar da shi ne a jiya.
Muna rokon Allah Ya karbi ayyukan mu.



Abokaina Mukhtar Ambazonia Abba Rigasa  Ya Kasuwa 🤣 Laminu yau ba market
26/10/2025

Abokaina Mukhtar Ambazonia Abba Rigasa Ya Kasuwa 🤣
Laminu yau ba market

Anci Jakaianci Jakaiiaaanci Jakaiiiii 😃🙅🤸🤸🤸
26/10/2025

Anci Jakai
anci Jakaii
aaanci Jakaiiiii 😃🙅🤸🤸🤸

Makabartar Barcelona 🤍💙
26/10/2025

Makabartar Barcelona 🤍💙

Bari mu ga suwaye tsofaffin ƴan IZALA a gidannan.Wa kagane a hotonnan.? Kuma wace Shekara ce.?
25/10/2025

Bari mu ga suwaye tsofaffin ƴan IZALA a gidannan.

Wa kagane a hotonnan.? Kuma wace Shekara ce.?

Mutan Makka sun bawa HASSAN BN THABIT kuɗi akan ya aibata Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a cikin waƙa, irin aibatawa...
25/10/2025

Mutan Makka sun bawa HASSAN BN THABIT kuɗi akan ya aibata Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama a cikin waƙa, irin aibatawar da tarihi zai daɗe yana ambatonta.

Hassan ya tsaya a hanyar da Ma'aiki yake wucewa, yana hango shi, sai ya kasa ƙura masa idanu b***e ya ga aibunsa, saboda kyawun hasken fuskarsa da kuma kwarjininsa.

Hassan ya koma ya basu dukiyarsu ya ce: Ya Allah! Ka zama sheda lalle n shaida Muhammad Manzon Allah ne.

Ƙuraishawa s**a ce masa: wannan ba shi ne aikin da muka saka ka ba.

Sai y ce: Tun da nake ba taɓa ganin kyawun halitta ba irin halittarsa (Sallallahu Alaihi Wasallama).

Da na ƙura masa Ido domn aibata shi; kau da idona na yi saboda tsananin hasken fuskarsa kar in makance.

Tsira d Aminci su tabbata a gareka y wanda duniya ta yi haske da haskensa.

s**airaj Hafiz Imam

Malami Bafaden Allah
23/10/2025

Malami Bafaden Allah

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yakubu M Ibrahim posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Yakubu M Ibrahim:

Share

Category