07/09/2025
Ba kowanne lokaci muke samun abin da muke matuƙar so ba.😥
A lokuta da dama, mukan nace da son abu fiye da kima. Amma a wannan lokacin Allah (SWT) na iya jarabtar mu da rashin samun Wannan abin.
Wannan jarabawa tana iya zuwa ta hanyoyi daban-daban: wataƙila ka rasa damar mallaka, ko kuma mafita ta toshe gaba ɗaya, ko ta shafi lafiya, ilimi, daraja, Badan baka cancanta ba Kuma Bawai Allah yana tauye ka ba ne Saboda Bayason ka Mallaki Abin, a’a, sai dai domin ya nuna maka cewa Shi kaɗai ne Maɓuɗin komai.
Wani lokaci Allah kan sa maka son wani abu, amma ya hana ka ikon samun sa. Wannan nuni ne cewa Ubangiji na iya jarabtar imaninmu ta kowace siga domin ya tsaftace zuciya.
Shiyasa a cikin Alƙur’ani Maigirma, a Suratul Baqarah aya ta 216, Allah (SWT) ya ce:
﴿ كُتِبَ عَلَيْكُمُ الْقِتَالُ وَهُوَ كُرْهٌ لَكُمْ ۖ وَعَسَىٰ أَنْ تَكْرَهُوا شَيْئًا وَهُوَ خَيْرٌ لَكُمْ ۖ وَعَسَىٰ أَنْ تُحِبُّوا شَيْئًا وَهُوَ شَرٌّ لَكُمْ ۗ وَاللَّهُ يَعْلَمُ وَأَنْتُمْ لَا تَعْلَمُونَ ﴾
“An wajabta muku yaƙi, alhali kuna ƙin sa. Amma watakila ku ƙi wani abu, alhali shi ne alheri a gare ku. Kuma watakila ku so wani abu, alhali shi ne sharri a gare ku. Allah ne Ya sani, ku kuma ba ku sani ba.”
Wannan aya tana koyar damu cewa abubuwan da muke ɗauka a matsayin burin rayuwa ba lallai su zama alheri gare mu ba. Sau dayawa abin da muke ƙi ko Bamu so, shine yake zame mana tushen alheri a Rayuwa,
Shawara ga ’yan’uwa
Duk abin da zamuyi, mu roƙi Allah Ya zaba mana mafi alheri. Mu yi istikhara kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya koyar, duk lokacin da wani al’amari ya taso mana wanda muke so amma ba mu da tabbacin sa.
Na rantse da Allah !!
Duk irin son da ka kewa wani abu, idan ka dage da yin istikhara kana miƙa lamarinka ga Allah, Wallahi Allah bazai bari ka mallaki wannan abin ba idan ba alheri bane gare ka.
Zai buɗe maka ƙofa ta mafita cikin sauƙi, kuma zai musanya maka shi da abin da ya fi dacewa da kai na Alkhairi
Allah Kayi mana Zabi Mafi Alkhairi A Dukkan Lamuran mu
Posting na Gaba Zanyi shi ne akan yadda akeyin istikhara Kamar yadda Manzon Allah SAW ya koyar
Please Share
©️Yakubu M Ibrahim ✍️