Musa ibrahim Adam

Musa ibrahim Adam Kano State

MATASAN AREWA SHUWAGABANNIN GOBE KO MABARATAN GOBE?Professor Usman yusuf Katsina mutum ne da a yanzu ya shiga rukunin mu...
02/02/2025

MATASAN AREWA SHUWAGABANNIN GOBE KO MABARATAN GOBE?

Professor Usman yusuf Katsina mutum ne da a yanzu ya shiga rukunin mutanen da za ka kalla ka kira su dattawa.

Sannan dole ka saka shi cikin rukunin dattawan da suke kaunar goben matasan Arewa ta yi kyau,saboda shi dai ya gina rayuwar sa mai inganci.

A shekarar 1982,wanda yayi dai-dai da Shekaru Arba'in da uku (43 years)kenan yau,ya gama digirin sa na farko a matsayin Likita(MBBS)daga Jami'ar Ahmed Bello University a Zaria.

A shekarar 1989 ya zama kwararren likitan yara(Consultant Paediatrician)

Yayi nasarar cin jarrabawar Scholarship a University of Liverpool a London inda yayi Postgraduate course dinsa a Tropical Medicine.

Daga nan ya koma Fred Hutchison Cancer research centre a Washington,US.

A shekarar 2000 ne ya zama Associate Professor.

A shekarar 2008 ne ya zama Full Professor a fannin ilimin halittar jini(Haematology)da kuma ilimin gano da magance cutar cancer(Oncology).

Yayi aiki a nahiyoyi(Continent)guda uku,Afrika,Turai da Arewacin Amurka.

Yanzu mai wannan matakan me yake nema a duniya?
Gida?
Abinci?
Muhalli? Ko
Riga?

Duk Allah ya bashi.

Gwamnatin Nigeria 🇳🇬 ce karkashin mulkin Buhari ta nemi da ya dawo gida ya bayar da gudunmawa a hukumar inshora ta lafiya(NATIONAL HEALTH INSURANCE SCHEME)NHIS.

Bayan dawowar sa ya fara aiki a matsayin Executive secretary na hukumar ta NHIS,sai ya fahimci kudaden da ake rabawa jihohi daga hukumar a matsayin inshora na lafiya ana tura su ne ta asusun wani tsohon Sanata,shi tsohon Sanatan shine zai rarrabawa jihohin da aka bawa wanann kudin bayan ya cire duk abinda s**a tsara shi da wasu azzalumai a kasar.
Da kuma wasu tarun badakala.

Professor Usman yusuf yace ba karkashin office din sa kuma akan idon sa za'ayi wannan ba.

Daga nan ya fara fuskantar barazana daga masu amfana da kudaden na inshora,har ta kai ga an dakatar da shi na tsawon wata goma sha daya,sannan hukumar ta ce ta kafa kwamitin bincike akan sa,bayan ya dawo bakin aiki takaddama taki karewa,daga karshe dai s**a yi nasarar korar sa daga ofishin Ministan lafiya,aka kaiwa Shugaban kasa ya saka hannu✍️.

Bayan korar sa da s**a yi daga hukumar ne ya dawo ya fara kiraye kirayen Nigeria tana cikin wani hali,Arewa mu farka,goben matasan su da ya'yan su ba ta da kyau a hannun mutanen can,a haka har gwamnatin Buhari ta shude.

Wannan gwamnatin ta zo ta jefa mutane cikin halin yunwa da ukuba,bai yi kasa a gwiwa ba ya cigaba da kiran ta cikin ilimintarwa,sai su ka dauke shi a matsayin makiyi wanda dole sai sun saka shi yayi shiru.

Cikin satin da muka yi bankwana da shi sai ga sanarwar cewa hukumar EFCC ta k**a Professor,mun kashe kunne mu ji laifin sa,sai aka ce ya bayar da wata kwangila ne ba bisa ka'ida ba a lokacin yana office din sa a matsayin Executive secretary na hukumar NHIS,kwangilar ta kudi Naira dubu dari bakwai da wasu ya'n kai,ba fa Miliyan dari bakwai ba.

Abin kuma da yafi kona min zuciya har nake wannan rubutun shine,matasan da Professor yake wannan rigimar a kansu,a cikin satin da aka k**a shi,a satin ne wani abin banza da sunan Tik toker wanda ni Wallahi summa tallahi ban ta6a sanin sa ko ganin hoton sa ba sai satin nan,shine matasan s**a shagala da batun wai yayi aure.

Prof yana can tsare a Kuje prison a dalilin halin da kuke ciki.
Duk Azabar nan dai mune da iyayen mu ake ganawa ita,babu wanda a gidan su zai bigi kirji yace kasar nan ana cikin kwanciyar hankali,amma ko a jikin ku.

Wannan ce ta sa nake kaunar mutanen kudu,domin yau da ace irin wannan mutumin na su ne aka k**a,to duk wata hukumar kula da hakkin dan Adam,hukumomin walwala da jin kai,International communities duk sai sun ji hakin da ake ciki.

Goben mu a hannun mutanen nan ba mai kyau ba ce,ni dai da ace Arewa riga ce,da tuni na cire ta na jefar na fara yawo tsirara tunda yanzun ma tsirara ake kallon mu.

🤦‍♂️✍️.

MATASAN AREWA SHUWAGABANNIN GOBE KO MABARATAN GOBE?Professor Usman yusuf Katsina mutum ne da a yanzu ya shiga rukunin mu...
02/02/2025

MATASAN AREWA SHUWAGABANNIN GOBE KO MABARATAN GOBE?

Professor Usman yusuf Katsina mutum ne da a yanzu ya shiga rukunin mutanen da za ka kalla ka kira su dattawa.

Sannan dole ka saka shi cikin rukunin dattawan da suke kaunar goben matasan Arewa ta yi kyau,saboda shi dai ya gina rayuwar sa mai inganci.

A shekarar 1982,wanda yayi dai-dai da Shekaru Arba'in da uku (43 years)kenan yau,ya gama digirin sa na farko a matsayin Likita(MBBS)daga Jami'ar Ahmed Bello University a Zaria.

A shekarar 1989 ya zama kwararren likitan yara(Consultant Paediatrician)

Yayi nasarar cin jarrabawar Scholarship a University of Liverpool a London inda yayi Postgraduate course dinsa a Tropical Medicine.

Daga nan ya koma Fred Hutchison Cancer research centre a Washington,US.

A shekarar 2000 ne ya zama Associate Professor.

A shekarar 2008 ne ya zama Full Professor a fannin ilimin halittar jini(Haematology)da kuma ilimin gano da magance cutar cancer(Oncology).

Yayi aiki a nahiyoyi(Continent)guda uku,Afrika,Turai da Arewacin Amurka.

Yanzu mai wannan matakan me yake nema a duniya?
Gida?
Abinci?
Muhalli? Ko
Riga?

Duk Allah ya bashi.

Gwamnatin Nigeria 🇳🇬 ce karkashin mulkin Buhari ta nemi da ya dawo gida ya bayar da gudunmawa a hukumar inshora ta lafiya(NATIONAL HEALTH INSURANCE SCHEME)NHIS.

Bayan dawowar sa ya fara aiki a matsayin Executive secretary na hukumar ta NHIS,sai ya fahimci kudaden da ake rabawa jihohi daga hukumar a matsayin inshora na lafiya ana tura su ne ta asusun wani tsohon Sanata,shi tsohon Sanatan shine zai rarrabawa jihohin da aka bawa wanann kudin bayan ya cire duk abinda s**a tsara shi da wasu azzalumai a kasar.
Da kuma wasu tarun badakala.

Professor Usman yusuf yace ba karkashin office din sa kuma akan idon sa za'ayi wannan ba.

Daga nan ya fara fuskantar barazana daga masu amfana da kudaden na inshora,har ta kai ga an dakatar da shi na tsawon wata goma sha daya,sannan hukumar ta ce ta kafa kwamitin bincike akan sa,bayan ya dawo bakin aiki takaddama taki karewa,daga karshe dai s**a yi nasarar korar sa daga ofishin Ministan lafiya,aka kaiwa Shugaban kasa ya saka hannu✍️.

Bayan korar sa da s**a yi daga hukumar ne ya dawo ya fara kiraye kirayen Nigeria tana cikin wani hali,Arewa mu farka,goben matasan su da ya'yan su ba ta da kyau a hannun mutanen can,a haka har gwamnatin Buhari ta shude.

Wannan gwamnatin ta zo ta jefa mutane cikin halin yunwa da ukuba,bai yi kasa a gwiwa ba ya cigaba da kiran ta cikin ilimintarwa,sai su ka dauke shi a matsayin makiyi wanda dole sai sun saka shi yayi shiru.

Cikin satin da muka yi bankwana da shi sai ga sanarwar cewa hukumar EFCC ta k**a Professor,mun kashe kunne mu ji laifin sa,sai aka ce ya bayar da wata kwangila ne ba bisa ka'ida ba a lokacin yana office din sa a matsayin Executive secretary na hukumar NHIS,kwangilar ta kudi Naira dubu dari bakwai da wasu ya'n kai,ba fa Miliyan dari bakwai ba.

Abin kuma da yafi kona min zuciya har nake wannan rubutun shine,matasan da Professor yake wannan rigimar a kansu,a cikin satin da aka k**a shi,a satin ne wani abin banza da sunan Tik toker wanda ni Wallahi summa tallahi ban ta6a sanin sa ko ganin hoton sa ba sai satin nan,shine matasan s**a shagala da batun wai yayi aure.

Prof yana can tsare a Kuje prison a dalilin halin da kuke ciki.
Duk Azabar nan dai mune da iyayen mu ake ganawa ita,babu wanda a gidan su zai bigi kirji yace kasar nan ana cikin kwanciyar hankali,amma ko a jikin ku.

Wannan ce ta sa nake kaunar mutanen kudu,domin yau da ace irin wannan mutumin na su ne aka k**a,to duk wata hukumar kula da hakkin dan Adam,hukumomin walwala da jin kai,International communities duk sai sun ji hakin da ake ciki.

Goben mu a hannun mutanen nan ba mai kyau ba ce,ni dai da ace Arewa riga ce,da tuni na cire ta na jefar na fara yawo tsirara tunda yanzun ma tsirara ake kallon mu.

🤦‍♂️✍️.

Happy Friday
24/01/2025

Happy Friday

Gwamnonin Nigeria kaf (gaba dayan su) sun hadu yau a fadar shugaban kasa sun amince da kudirin karin haraji na shugaba T...
17/01/2025

Gwamnonin Nigeria kaf (gaba dayan su) sun hadu yau a fadar shugaban kasa sun amince da kudirin karin haraji na shugaba Tinubu.
~ Gaba ɗaya gwamnonin kasar sun je, sun sa hannu sun amince, wadanda basu je sun aike da wakilai, sun sa hannu a madadin su.

Dama Tinubu ya fada babu gudu babu ja da baya sai an kara haraji a kasar, ya fadi haka ne saboda yasan yadda zai fito wa duk wadanda suke adawa da manufar sa akan Harajin.
~ Ai kuwa gashi ya shawo kansu, har da wani gwamna da muka ji shi yana nasiha ma wani Malami wai yana jin zafin halin da Tinubu yaje talaka a ciki.

Mun ganku, kun je, kun sa hannu.
Saura muji wani yazo yana ce mana basu tare da manufofin Tinubu na karin haraji.

~ Talakawa sai ku duba da kyau ku ga wakilan ku.

The governor's Forum endorsed a revised Value Added Tax (VAT) sharing formula to ensure equitable distribution of resources:

Existing VAT sharing formular is:

1. Derivation 20%
2. Equality 50%
3. Population 30%

The proposed tax reforms formular:

1. Derivation 60%
2. Equality 20%
3. Population 20%

Governors' Forum Proposal:
1. Derivation 30%
2. Equality 50%
3. Population 20%

11/08/2024
Da Dumi-Dumi Gwamantin Tarayya Ce Za ta Ke Biyan Ma'aikatan Kananan Hukumomi da na Jihohi AlbashiMa'aikatan Ƙananan huku...
07/04/2024

Da Dumi-Dumi

Gwamantin Tarayya Ce Za ta Ke Biyan Ma'aikatan Kananan Hukumomi da na Jihohi Albashi

Ma'aikatan Ƙananan hukumomi da na Jihohi za su dawo karkashin Gwamnatin Tarayya.

Gwamantin Tarayya zata sauyawa dukkannin ma'aikatan Kananan hukumomi da na jihohi suna zuwa ma'aikatan gwamantin tarayya.

Za kuma a tilastawa dukkanin ma'aikatan fara yin amfani da tsarin biyan albashi na bai ɗaya wato IPPIS.

Hakan zai dakile gwamnoni daga wawure kuɗaɗen kananan hukumomi.

Gwamnoni zasu ke amfani da kuɗin da gwamnatin tarayya ta ke turawa kowacce jiha a wata-wata ne wajen bunkasa jihar su.

Wannan shi ne manufar gwamantin Tinubu na sabunta fata (Renewed hoped)

Wannan tsarin zai kawo karshen wawure kudaden kananan hukumomi da waɗannan “Shugabannin dole” suke yi, wajen naɗa kansu mulki.

Hakan na nufin al'ummar jihohi za su iya bincikar gwamnoninsu.

Wannan sabon tsari ne da ƴan Nijeriya za su ji daɗinsa.

Allah Ya sa Shugaba Tinubu ya yi nasara Allah ya taimaki Nigeria. ©️

KUNCE KUNA ROƘON ALLAH AMMAH BAYA AMSA MUKU, EH SABODA KUNA DA CUTUKA GUDA GOMA(10)NE.Shaykh Muhammad Bin Uthman Cuta ta...
12/03/2024

KUNCE KUNA ROƘON ALLAH AMMAH BAYA AMSA MUKU, EH SABODA KUNA DA CUTUKA GUDA GOMA(10)NE.

Shaykh Muhammad Bin Uthman

Cuta ta Farko;

(1)Kunce kuna son Allah amma bakwa bashi hakkinSa.

(2)Kunce kunason Manzon Allah amma bakwa bin sunnar shi.

(3)Kuna karatun Qur'ani amma bashine tsarin mulkinku ba.

(4)Kunce sheɗan makiyinku ne amma kuna biye mashi.

(5)Kunsan Mutuwa gaskiya ne amma baku shirya mataba.

(6)Kunsan Aljana gaskiya ce amma bakwa nemanta da gaske.

(7)Kunsan Jahannamah gaskiya ce amma bakwa Guje mata.

(8)Kunacin Arzikin Allah kuna masa butulci bakwa gode masa.

(9)Sai ku tsaya kunayi da mutane kuna shagala da aibin mutane kumance da aibin kanku.

(10)Kullum kuna binne mamata,kullum kuna kai gawa kabari,
ammah bakwa Wa'aztuwa.

Allah yasa mu wanye lafiya.

SHAWARA CE MAI MUHIMMANCIMasu karin magana s**ace gyara kayanka bai taba zama sauke mu raba baIna hadu da Girman Allah j...
12/03/2024

SHAWARA CE MAI MUHIMMANCI

Masu karin magana s**ace gyara kayanka bai taba zama sauke mu raba ba

Ina hadu da Girman Allah jama'a ku yi taka tsantsan sosai wajen sayan waya second hand, kuma musamman idan baku san wadanda s**ayi amfani da wayar ba

Akwai manyan Criminals, suna zuwa shago su sayi waya sabuwa, babba ko karama, sai su je su aikata laifi, suna kammala aikata laifin sai su sayar da wayar tareda kwalinta ko ma su jefar da ita

Kai a tsammaninka ba matsala bane don kaje ka sayi waya second hand da kwalinta kayi amfani da ita, amma fa baka san irin mummunan laifin da aka aikata da ita ba, idan bincike ya tashi zai shafeka

Kafin gaskiyarka ta kubutar da kai kasha wahala, idan kuma ka fada hannun azzaluman masu bincike shikenan sai yadda rayuwa ta kasance da kai

Ku sani cewa da zaran ka sayi waya ka saka simcard a ciki to ko kona wayar akayi akwai hanyoyin da ake gano duk wanda ya taba amfani da wayar abisu daya bayan daya a k**a

Kuma kar a rena girma ko karancin wayar, indai ana iya daurawa waya SIM card.

Address

NASIRIYYA G R A
Kano

Telephone

+2349066085935

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Musa ibrahim Adam posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Musa ibrahim Adam:

Share