24/07/2026
DA DUMI-DUMI: Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga likitoci da sauran ƙwararrun ma'aikatan lafiya 'yan Najeriya da ke zaune a ƙasashen waje da su dawo gida domin bayar da gudunmawarsu wajen bunƙasa harkar lafiya da ci gaban ƙasa.
Tinubu ya bayyana cewa babu inda ya fi gida, yana mai jaddada cewa ƙwarewa da ilimin da 'yan Najeriya s**a samu a ƙetare za su taimaka matuƙa wajen inganta tsarin kiwon lafiya da ci gaban Najeriya.