Binul Mustapha

Binul Mustapha we seek Allah's protection and guidance

06/06/2025

Nigeria in the future

*WAJABCIN ƘANƘAN DA KAI GA MUTANE* Manzon Allah (Sallallahu Alaihi wa sallama) ya ce:*"Allah Ya yi min wahayi cewa ku ƙa...
06/06/2025

*WAJABCIN ƘANƘAN DA KAI GA MUTANE*

Manzon Allah (Sallallahu Alaihi wa sallama) ya ce:

*"Allah Ya yi min wahayi cewa ku ƙanƙan da kawunanku ga junanku; kada wani ya dinga (alfahari) jin fifiko akan wani, kuma kada wani ya zalunci wani."*

Imamu Muslim

Hadisin ya na koyar da mu wajabcin tawadu'u (ƙanƙan da kai), ta hanyar rashin jin cewa mun fi kowa ballantana ma mu zalunci mutane. والله أعلم

23/05/2025
23/04/2025

Da ana haka da tuni an kawo karshen daba da kwacen waya

MAGANA TA ADALCI GAME DA ƊAN BELLODa farko dai ya kamata mu sani cewa Ɗan Bello da Sheikh Balalau ƴan Adam ne ba ma'asum...
02/04/2025

MAGANA TA ADALCI GAME DA ƊAN BELLO

Da farko dai ya kamata mu sani cewa Ɗan Bello da Sheikh Balalau ƴan Adam ne ba ma'asumai bane zasu iya dai-dai zasu iyayin kuskure

Sheikh Balalau kamar yadda aka sani Shahararren malamin Addinin ne Wanda ya samu shaidar nagarta daga manyan MALAMAI na ƙasar nan kuma sannan jimawar da yayi Yana riƙon shugabancin ƙungiyar izala ya tabbatar da haka domin asanina ba'a taɓa samin wata ɓaraka ba tun daga lokacin daya karɓi shugabancin har zuwa yanzu hakan yake tabbatar da nagartar sa da kuma kirkinsa da riƙon amanarsa, lallai Sheikh Balalau mutumin ƙirkiri ne da wahala ace wai an haɗa baki dashi an cuci Al'ummar Musulmai wannan kenan

Shi kuma Ɗan Bello mutum ne matashi ɗan Boko kuma ɗan gwagwarmaya mai kishin ƙasa da son ganin anyi gyara game da yadda alamuran ƙasar nan Ke tafiya Mai son ganin an magance matsalar cin hanci da rashawa a kasar nan, akwai matasa ire-irensa da muke dasu a ƙasar nan kamar irin su Barr. Abba Hikima da Barr. Bulama Bukarti irin su Jafar Jafar da sauransu da wasu da dama da ban ambata ba

Ire-iren mutanen nan lallai a yanayin yadda ƙasar nan take tafiya lallai muna bukatar ƴan gwagwarmaya ire-irensu waƴanda zasu yi amfani da ilimin su da matsayinsu wajen ganin an kawo gyara a kasar nan don haka su ɗin ba ƙashin yadawa bane, domin suma ɗin suna da amfani garemu mu Musulmi, Mu ƴan Arewa, lallai muna buƙatar su Sai dai kuma yakamata Kai Mai karatu kasan cewa:-

(1) Su Ba ma'asumai bane s**anyi dai-dai s**anyi kuskure
(2) Su ƴan boko ne, shi kuma ɗan Boko idan bai koshi da addini ba tinaninshi ba abin dogaro bane 100% , akan samu zamiya da sauka daga shoulder
(3) Su s**an dogara ne da abinda ya bayyana agaresu ko kuma abinda bincikensu ya haifar
(4) Su ba karnukan ya hudawa bane kamar yadda wasu suke musu kallan haka kawai don suna zaune a kasashen waje ko dan ƴan boko ne, a fahimtata mutane ne masu son kawo gyara wannan kenan

Lallai Malamammu na Addini ba ƙaramin gudummawa suke bawa zamantakewar rayuwarmu ba, amfaninsu garemu bazai misaltuna bai kuma baidace ba wani ya ɗauki layin cutar dasu ko cin mutuncinsu ba, domin su kaɗai s**a rage mana a kasar nan da suke sadaukar da rayuwarsu akanmu, Allah ya ƙarfafesu Allah ya tai makesu duniya da lahira Ameen

Kai tsaye zan kutsa cikin magana game da abinda yake trending a yanzu na tuhuma da ɗan Bello yayi ga Sheikh Balalau da kuma Jibwis

Ɗan Bello acikin maganganun dayi game da Balalau akwai rashin ADALCI da baiyi Mai ba domin ya tuhumesa kamar haka:-

(1) Ya tuhumesa da mallakar account sama da Talatin, Wanda wannan ba laifi bane ɗan ƙasa ya mallaki account 100 ma ko sama da haka da BVN number ɗaya.

(2) Ya ɗora masa laifin da shi kansa Ɗan Bello n bai kawo hujja ba ƙarara wacce take nuna Balalau Yana ciki tsamo-tsamo.

(3) Ya zargi ƙungiyar da Balalau yake jagoranta wato JIBWIS da karɓar kuɗi daga wajan gomnati hakan ya nuna kenan ana Kashi muraba dasu tare da Azzaluman ƴan Siyasa.

Kuma dalilin da ya bada ya nuna cewa ƙungiyar Izala Jibwis nada Alaƙa da Kamfanin dake karɓar kuɗin daga gomnati Wanda yake zargin ba'a gudanar da aikin, Sai kuma ga hujjoji suna yawo a social media na ayyukan an kamamala, hakan yake nufin Ɗan Bello yayi kuskure wajan rashin tabbatar da ingancin bincikensa kafin ya yaɗashi kuma zargin daya jefa zuwa ga Jibwis bayyi Mata Adalci ba domin ba ita gomnati ta sawa kuɗi a account ba, don haka tuhumarta Zalinci ne

SHAWARA GAREKA ƊAN BELLO
Ni a shawarce shawarar da zan ba Ɗan Bello itace kamar haka:-

(1) Karinƙa tabbatar da dukkan binciken ka kafin ka yaɗashi don kudun kada ka kwana aikin

(2) Masu baka rahoto suma sai ka tabbatar Baza suyi Maka ƙarya ba kuma sannan su kansu suna tabbatar da ingancin bayanai kafin su baka

(3) Sannan ka rinƙa tuhumar wa'ƴanda bincikenka yabaka hujja, ba'a wa'ƴanda baka da hujja akan su ba walau ƴan Siyasa ne ko malaman Addini ne Kai koma wani irin mutum ne katabbatar kana da hujja akanshi, domin kasan cewa akwai kotu

(4) Sannan kasani Kai ba kotu bane abinda zaka iyayi shine zargi ba hukunci ba, kotu ce kaɗai take iya yin hukunci cewa wane ankama shi da laifin kaza ko kaza, Kai naka zargi binciken kotu shi zai tabbatar

(5) Fatan alkhairi kare ka da duk sauran ƴan gwagwarmaya ire-irenka musamman Barr. Abba Hikima da Barr. Bulama da sauransu

SHAWARA ZUWA GA USTAZAI DA ƊALIBAN ILIMI
A shawarce shawarar da zan Bamu anan shine muji tsoron Allah, kada murinƙa Fasiƙantar da mutum ko Yi masa ƙazafi ko ɓatashi (total condemnation) saboda yayi kuskure ko kuma saboda muna tuhumarsa da Zalinci, ya kamata musani cewa a baya dayake ɓan kaɗo ire-iren wayannan bayanai Yaba masa muke muna jinɗaɗi muna masa kirari da kwarzon shekara kamar yadda wani naga postin na wani matashi dake karatu a waje Mai suna Alhassan Mai lafia saboda abin bai shafemu ba ƴan Siyasa yake tonawa asiri.

To kaga irin hakan ba Adalci bane idan ana tuhumar wasu muna jin daɗi to kuma don tazo akanmu bai kamata kuma mu koma ɓata mutum ba, idan mukai haka me kenan? mun zama ƴan Bid'a kenan!!? Allah ya tsare kuma ya kamata musani cewa shi Mai girma Sheikh Balalau ba ma'asumin bane idan an tuhumeshi akan wani abu Gaskiyarsa itace zata kuɓutar dashi Wanda Bama shakkar Gaskiyar sa da nagartar sa

Abinda ƴan uwa s**ayi na zaƙulo ajujuwan da aka Gina cewa ba cinye kuɗin a kaiba wannan shine abinda ya dace ba zage-zage ba da cin mutuncin mutum manya-manyan MALAMAI na da ma da wasu daga cikin sahabbai an humcesu Gaskiyar su ta kuɓutar dasu ballantana na yanxu

Don haka masu zagi da cema Masa Ai dama maƙaryaci ne ko kuma ai Karen farautar ya hudawa ne su yake wa aikin don yaɓata MALAMAI kongila aka bashi kuji tsoron Allah wannan abu da kuke tafarkin ƴan Bid'a NE ba na ahlus Sunnah, ba zayyuba muna Kiran kanmu Ahlus Sunnah kuma munayi Abinda Allah subhanahu wata'ala ya Hana nayin ƙazafi ga mutum kuma munsan ba haka bane, kawai saboda ya fusata mu

Idan mutum yayi Maka ƙazafi ko yayi Maka sharri to Kai amatsayin Ahlus Sunnah kaima ba ƙazafi ko sharri zakai maiba, sai kuza ma ɗaya Allah ya tsare

A ƙarshe nake cewa USTAZAI da Ɗaliban ilimi da ƴan ƙungiyar Izala Allah ya huci zuciyar ku lallai Ɗan Bello yayi kuskure babba Allah ya gafarta Mana baki ɗaya ameen

✍️Usaimeen Mustapha
wed, 2 April. 2025

ƘALU BALENKA SARKIN KANO GAME DA TA'ADDANCIN DA AKA YIWA MUSULMI A EDO STATE?Ko Mai karatu zai iya tunawa da YUNUSU YELL...
30/03/2025

ƘALU BALENKA SARKIN KANO GAME DA TA'ADDANCIN DA AKA YIWA MUSULMI A EDO STATE?

Ko Mai karatu zai iya tunawa da YUNUSU YELLOW?

Kamar yadda kowa yasani wasu ƴan shekaru da s**a wuce anyi wani case na wani yaro YUSUF YELLOW Wanda wata yarinya daga KUDU ta musulunta a raɗin Kanta ta Biyu shi nan Arewa da Kanta

A lokacin ne ƴan KUDU s**ayi cah akai wai ya tirsasata ya gudo da ita Wanda Sarkin Kano a lokacin ya shiga case ɗin ta yadda ya damƙa YUSUF YELLOW wa ƴan KUDU don su hukuntashi haka abin nan ya faru a kasar nan

Ko yanzu a wani hali YUSUF YELLOW yake?
ko an sake shi yanzu? Allah shine masani

A cikin satin nan an samu wani TÁ'ÁDDÁNCĪ da aka yiwa ƴan uwanmu Musulmai Mafarauta Wanda s**a taho daga Elele Portacourt zuwa Kano inda akasamu wasu ƴan TÁ'ÁDDÁ da sunan vigilant s**a yi musu kisan wulaƙanci s**a Kona wasu da ransu inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un

Haka s**a riƙa bidiyo suna ɗauka suna duka da jifa da wulaƙanci iri-iri da sunan wai kidnappers ne, Wanda a dai-dai lokacin da hakan yafaru wannan Sarkin da ya miƙa YUSUF YELLOW a waccan lokacin yanzu ma shine Sarki, sai dai kash!!! ba muji wani yunƙuri daga wajansa

Ko ƙoƙarin ganin an ƙwatowa bayin Allahn nan hakkinsu an biya iyalansu diyyan rayukansu da aka salwartar, Wanda a case ɗin YUSUF YELLOW rai bai salwanta ba amma kayi ruwa da tsaki wajan miƙamusu shi don su hukuntashi sai gashi ba muga haka daga gareka ba a wannan case ɗin

Wanda tuni Allah subhanahu wata'ala ya yanke Maka hanzari na ƙara baka sarautar Kanon don tayyu a iya cewa ai yanzu ba Sarki bane sai Allah ya yanke wannan hanzarin don haka lallai akwai haƙƙi Mai girma da ka ɗorawa kanka Wanda Allah subhanahu wata'ala zai tambayeka game da rashin sauke shi

Lallai Mai martaba Sarkin Kano rashin yin hakan zai zubar Maka da ƙima a idon Musulmai da kuma ƴan Arewa da kuma ƴan jahar Kano, Sa'annan Ina jiyemaka tsoron kada a fassaraka da ɗan daɗi Arna, Wanda Bama fatan haka ta faru

Shin wai Arewa Babu wani jajirtaccen ɗan Siyasa ko basarake da zai zama wakilin Arewa?

Shin Arewa Bamu da jagorori Tsayayyu ne?

Allah yasa mudace, Ameen

Wannan AI hauka ne daga 20 zuwa hamsin kawai don tafi kowace jaha karɓar kasafi náwa legas take? to kaga Kano sai ƙara d...
27/03/2025

Wannan AI hauka ne daga 20 zuwa hamsin kawai don tafi kowace jaha karɓar kasafi náwa legas take? to kaga Kano sai ƙara daga 44 zuwa 100 kenan kawai

21/05/2023

Dr Zakir Naik

31/10/2022

Sharrin su ojuku da mulkin Obasanjo

19/07/2022

❝𝗔 𝗚𝗿𝗼𝘂𝗽 𝗼𝗳 𝗙𝗿𝗶𝗲𝗻𝗱𝘀 𝗔𝗿𝗲 𝗔𝗹𝗹 𝗟𝗶𝗸𝗲 𝗘𝗮𝗰𝗵 𝗢𝘁𝗵𝗲𝗿, 𝗮𝗻𝗱 𝘁𝗵𝗲 𝗟𝗼𝗻𝗴𝗲𝗿 𝘁𝗵𝗲 𝗙𝗿𝗶𝗲𝗻𝗱𝘀𝗵𝗶𝗽 𝗟𝗮𝘀𝘁𝘀, 𝘁𝗵𝗲 𝗖𝗹𝗼𝘀𝗲𝗿 𝘁𝗵𝗲 𝗖𝗵𝗮𝗿𝗮𝗰𝘁𝗲𝗿 𝗮𝗻𝗱 𝗠𝗮𝗻𝗻𝗲𝗿𝘀 𝗼𝗳 𝗘𝗮𝗰𝗵 𝗣𝗲𝗿𝘀𝗼𝗻 𝗶𝗻 𝘁𝗵𝗲 𝗚𝗿𝗼𝘂𝗽 𝗪𝗶𝗹𝗹 𝗕𝗲 𝘁𝗼 𝘁𝗵𝗲 𝗢𝘁𝗵𝗲𝗿𝘀. 𝗗𝗼 𝗡𝗼𝘁 𝗕𝗲𝗹𝗶𝗲𝘃𝗲 𝗧𝗵𝗮𝘁 𝗮 𝗚𝗼𝗼𝗱 𝗣𝗲𝗿𝘀𝗼𝗻 𝗖𝗮𝗻 𝗟𝗶𝘃𝗲 𝗳𝗼𝗿 𝗟𝗼𝗻𝗴 𝗪𝗶𝘁𝗵 𝗮 𝗖𝗼𝗿𝗿𝘂𝗽𝘁 𝗣𝗲𝗿𝘀𝗼𝗻, 𝗨𝗻𝗹𝗲𝘀𝘀 𝘁𝗵𝗲 𝗖𝗼𝗿𝗿𝘂𝗽𝘁 𝗣𝗲𝗿𝘀𝗼𝗻 𝗜𝗺𝗽𝗿𝗼𝘃𝗲𝘀 𝗮𝗻𝗱 𝗙𝗼𝗹𝗹𝗼𝘄𝘀 𝘁𝗵𝗲 𝗘𝘅𝗮𝗺𝗽𝗹𝗲 𝗼𝗳 𝘁𝗵𝗲 𝗚𝗼𝗼𝗱 𝗣𝗲𝗿𝘀𝗼𝗻.

𝗧𝗵𝗶𝘀 𝗶𝘀 𝗪𝗵𝘆 𝗬𝗼𝘂 𝗦𝗵𝗼𝘂𝗹𝗱 𝗟𝗼𝗼𝗸 𝗳𝗼𝗿 𝘁𝗵𝗲 𝗚𝗼𝗼𝗱 𝗣𝗲𝗼𝗽𝗹𝗲, 𝗮𝗻𝗱 𝗮 𝗙𝗿𝗶𝗲𝗻𝗱 𝗶𝘀 𝗟𝗶𝗸𝗲 𝗮 𝗖𝗵𝗮𝗶𝗻: 𝗛𝗲 𝗪𝗶𝗹𝗹 𝗘𝗶𝘁𝗵𝗲𝗿 𝗗𝗿𝗮𝗴 𝗬𝗼𝘂 𝗜𝗻𝘁𝗼 𝗣𝗮𝗿𝗮𝗱𝗶𝘀𝗲, 𝗼𝗿 𝗗𝗿𝗮𝗴 𝗬𝗼𝘂 𝗜𝗻𝘁𝗼 𝗛𝗲𝗹𝗹. 𝗛𝗲 𝗪𝗶𝗹𝗹 𝗘𝗶𝘁𝗵𝗲𝗿 𝗖𝗮𝘂𝘀𝗲 𝗬𝗼𝘂 𝗣𝗿𝗼𝗯𝗹𝗲𝗺𝘀 𝗼𝗿 𝗛𝗲 𝗪𝗶𝗹𝗹 𝗛𝗲𝗹𝗽 𝗬𝗼𝘂 𝗦𝗼𝗹𝘃𝗲 𝗬𝗼𝘂𝗿 𝗣𝗿𝗼𝗯𝗹𝗲𝗺𝘀.❞

Dr Zakir Naik

Address

Nassarawa L. G, Brigade
Kano

Telephone

+2348060174141

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Binul Mustapha posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category