Kobo Da Kobo

Kobo Da Kobo Jaridar Kobo Da Kobo - Za ta ringa kawo muku labarai da rahotanni da dumi dumi.

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya karɓi bakuncin Janar T.Y. Danjuma a wata ziyarar girmamawa da ya kai masa a fadar s...
28/02/2026

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya karɓi bakuncin Janar T.Y. Danjuma a wata ziyarar girmamawa da ya kai masa a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

An kaddamar da wata sabuwar doka mai suna “Dokar Vinicius” domin yaki da wariyar launin fata a harkar kwallon kafa.Hukum...
28/02/2026

An kaddamar da wata sabuwar doka mai suna “Dokar Vinicius” domin yaki da wariyar launin fata a harkar kwallon kafa.

Hukumar tsara dokokin kwallon kafa ta duniya, International Football Association Board (IFAB), tare da FIFA, sun amince da wasu sabbin matakai da nufin dakile wariyar launin fata.

Daya daga cikin matakan shi ne haramta wa ‘yan wasa rufe baki yayin da suke magana da abokin hamayya a filin wasa.

Ana sa ran za a amince da wannan doka gaba daya kafin fara gasar cin kofin duniya ta 2026.

Shugaba Tinubu Ya Sabunta Wa'adin Aikin Abubakar Audi A Matsayin Kwamanda Janar Na NSCDCShugaba Bola Ahmad Tinubu ya sak...
28/02/2026

Shugaba Tinubu Ya Sabunta Wa'adin Aikin Abubakar Audi A Matsayin Kwamanda Janar Na NSCDC

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya sake nada Dr. Ahmad Abubakar Audi a matsayin Kwamanda-Janar na Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC) na wani sabon wa’adi na shekaru biyar, daga 27 ga Fabrairu, 2026.

An fara nada shi ne a 2021 ta hannun tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, kuma wa’adinsa na farko ya kare ne a makon da ya gabata.

Shugaba Tinubu ya umurce shi da ya kara inganta aikin hukumar domin ta taka rawa sosai wajen inganta tsaron kasa.

Dr. Audi, haifaffen jihar Nasarawa, ya shiga aiki da NSCDC a 1996 kuma ya rike muk**ai daban-daban kafin ya zama Kwamanda-Janar.

Barau FC ta nemi afuwa kan sabanin fahimta tsakanin kocinta da dan jarida a KanoDaga Nazir Bashir TsamiyaKungiyar kwallo...
28/02/2026

Barau FC ta nemi afuwa kan sabanin fahimta tsakanin kocinta da dan jarida a Kano

Daga Nazir Bashir Tsamiya

Kungiyar kwallon kafa ta Barau FC da ke Kano ta nemi afuwar abin da ya faru tsakanin mai horas da ‘yan wasanta, Eugene Agbabe, da mamban kungiyar marubuta labaran wasanni ta SWAN kuma ma’aikacin Freedom Radio, Aminu Halilu Tudun Wada, inda ta bayyana lamarin a matsayin sabanin fahimta.

Manajan gudanarwar kungiyar, Mista Dominic Lorfa, ne ya bayyana hakan yayin wani zaman sulhu da aka gudanar tsakanin Barau FC da SWAN a safiyar Asabar a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano.

Lorfa ya ce tun farko sabanin ya samo asali ne daga rashin fahimtar juna tsakanin bangarorin biyu, yana mai cewa ya k**ata tun a wancan lokaci su kwantar da hankalinsu domin kauce wa rikicin.

Ya kuma jaddada kyakkyawar alakar da ke tsakanin kungiyar da ‘yan jarida, musamman SWAN, yana mai cewa kungiyar ta dauki mataki kan lamarin tare da alkawarin cewa hakan ba zai sake faruwa ba.

Har ila yau, ya yabawa shugabannin SWAN karkashin jagorancin Zahraddeen Saleh bisa jajircewarsu wajen sasanta rikicin.

Tun da fari dai, Aminu Halilu Tudun Wada ya zargi kocin Barau FC, Eugene Agbabe, da cin zarafinsa da kuma yunkurin dukansa a bainar jama’a, lamarin da ya kira rashin mutunta dan Adam.

WASANNI:Daga Mukhtar S Yahuza Hukumar tsara dokokin wasan kwallon kafa ta Duniya (IFAB) na shirin tattauna sabbin dokoki...
28/02/2026

WASANNI:

Daga Mukhtar S Yahuza

Hukumar tsara dokokin wasan kwallon kafa ta Duniya (IFAB) na shirin tattauna sabbin dokoki da za su kawo sauyi a wasan ƙwallon ƙafa domin rage ɓata lokaci da inganta kallo.

Ga muhimman abubuwan da ake shirin dubawa:

1- Gololi za su samu sakan 8 kacal domin sakin ƙwallo (goal kick ko throwing).
👉Idan s**a wuce lokaci, abokin hamayya zai samu corner kick ko a juya musu throwing ɗin.

2- Duk ɗan wasan da ya bukaci kulawa fiye da sakan 8, dole ne ya fita daga fili na sakan 60.
👉 Idan foul ne ya jawo masa rauni kuma aka bayar da yellow ko red card, dokar ba za ta shafe shi ba.
👉 Wannan dokar ba ta shafi gololi ba.

3- A lokacin sauyi, ɗan wasa zai samu sakan 10 daga ɗaga lamba har zuwa fita daga fili.
👉 Idan ya wuce, ƙungiyarsa za ta ci gaba da wasa da ƴan wasa 10 har sai an samu dakatarwa ta gaba.

4- VAR za ta iya shiga idan an bayar da corner ba daidai ba da ya kai ga cin ƙwallo, ko domin gyara yellow card na biyu da aka bayar ba bisa ƙa’ida ba.

Game da “Wenger Law” (sabuwar shawarar offside da ke cewa ɗan wasa zai zama offside ne kawai idan duk jikinsa ya wuce na defender), har yanzu ana kan tattaunawa.

Ana sa ran duk dokar da aka amince da ita za ta fara aiki daga 1 ga Yuni 2026, kafin fara gasar Kofin Duniya 2026.

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya fice daga jam'iyyar PDP zuwa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya tare da dukkan ...
27/02/2026

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya fice daga jam'iyyar PDP zuwa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya tare da dukkan yan majalisar zartarwarsa da jami’an jam’iyya.

Ya ce matakin ya biyo bayan shawarwari kuma an ɗauke shi ne domin ci gaban Adamawa da daidaita siyasar jihar da gwamnatin tarayya, domin cin gajiyar manufofin shugaba Bola Ahmad Tinubu.

Kafin hakan, mambobi 15 na majalisar dokokin jihar da kakakin majalisa sun riga sun koma APC.

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa umarnin da ta bayar na mayar da motocin hukuma daga hannun wasu jami’an da s**a yi ...
26/02/2026

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa umarnin da ta bayar na mayar da motocin hukuma daga hannun wasu jami’an da s**a yi murabus ya dace da doka kuma tsari ne na yau da kullum a aikin gwamnati.

Ta ce motocin mallakin gwamnati ne, an ba su ne domin gudanar da ayyukan hukuma, ba kyauta ko hakkinsu na kashin kai ba, domin a bisa ka’ida, duk jami’in da ya sauka daga mukami wajibi ne ya mika dukiyar gwamnati da ke hannunsa.

Gwamnatin ta jaddada cewa matakin ba hukunci ba ne, illa bin doka da rikon amana wajen kula da dukiyar jama’a, kuma za a sake amfani da motocin ne wajen bai wa sabbin jami’an da za a nada nan gaba.

Gwamnatin karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta bukaci jama’a su yi watsi da jita-jita, tana mai cewa za ta ci gaba da mai da hankali kan kawo cigaba ga al’ummar Kano.

Yadda Gwamnatin Kano ta kawata dakin taro na Africa House dake gidan Gwamnati.
26/02/2026

Yadda Gwamnatin Kano ta kawata dakin taro na Africa House dake gidan Gwamnati.

Wasu tsofaffin kwamishinoni a jihar Kano sun kai ƙarar gwamnatin jihar kotu, suna neman a biya su haƙƙokinsu da s**a ce ...
26/02/2026

Wasu tsofaffin kwamishinoni a jihar Kano sun kai ƙarar gwamnatin jihar kotu, suna neman a biya su haƙƙokinsu da s**a ce ba a biya su ba tun bayan saukarsu daga muk**ansu.

Sun bayyana cewa sun fara tuntubar ofishin sakataren Gwamnatin jiha domin warware matsalar cikin lumana, amma ba su samu amsa ba, a cewarsu, ana bin su kuɗaɗen amfani da motocinsu na kashin kai da s**a yi amfani da su wajen aiki na tsawon sama da shekara biyu.

Daga cikin masu ƙarar akwai Ibrahim Umar (Tsaro), Mustapha Rabiu Kwankwaso (Matasa), Yusuf Ibrahim Kofar Mata (Kimiyya da Fasaha), Adamu Aliyu Kibiya (Jin Kai), da Nasiru Sani Garo (Ayyuka na Musamman).

Sun ce sun tafi kotu ne domin tilasta wa gwamnati biyan haƙƙokinsu na kuɗaɗen motoci da sauran alawus-alawus k**ar yadda dokar RMAFC 2023 ta tanada.

A yammacin ranar Alhamis ne dai hukumar karɓar korafe-korafe da yaƙi da cin hanci ta Kano ta gudanar da aikin kwato motocin gwamnati daga hannun wadannan tsofaffin kwamishinonin a gidajensu, lamarin da ya jawo muhawara a fagen siyasar jihar.

Me ye ra'ayin ku?

Yanzu-Yanzu: Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta a Najeriya (INEC) ta tsayar da ranar 16 ga Janairu, 2027, a matsayin ranar ...
26/02/2026

Yanzu-Yanzu:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta a Najeriya (INEC) ta tsayar da ranar 16 ga Janairu, 2027, a matsayin ranar gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisun tarayya a kasar.

Haka kuma, hukumar ta ayyana ranar 6 ga Fabrairu, 2027, domin gudanar da zaɓen gwamnoni da na ƴan majalisun dokokin jihohi a faɗin ƙasar, k**ar yadda jaridar The Cable ta ruwaito.

Umahi Ya Musanta Zargin Amfani da ‘Yansanda Wajen Tsoratar da Wata MataMinistan ayyuka kuma tsohon Gwamnan jihar Ebonyi,...
26/02/2026

Umahi Ya Musanta Zargin Amfani da ‘Yansanda Wajen Tsoratar da Wata Mata

Ministan ayyuka kuma tsohon Gwamnan jihar Ebonyi, Sanata David Umahi, ya musanta zargin cewa ya yi amfani da ‘yan sanda domin tsoratar da wata mata mai suna Tracy Ohiri kan wani sabani da ya shafi bashin yakin neman zaɓe.

A wata sanarwa da mataimakinsa na musamman kan harkokin watsa labarai, Francis Nwaze, ya fitar a ranar Alhamis, Umahi ya bayyana cewa ‘yan sanda sun gudanar da aikinsu ne bisa ƙa’idojin kundin tsarin mulki, bayan wani ƙorafi da lauya ya gabatar musu.

Sanarwar ta ƙara da cewa jami’an tsaron sun k**a Ohiri ne bisa tsarin doka, tare da gayyatar ministan domin ya bayar da nasa bayani, k**ar yadda doka ta tanada.

Ofishin ministan ya kuma yi zargin cewa wani bidiyo da Omoyele Sowore ke yadawa a kafafen sada zumunta na ƙoƙarin bata masa suna ne kan wani lamari da tuni yake hannun hukumomin da s**a dace.

Tun da farko, PUNCH Online ta rawaito cewa a wani bidiyo da ya yadu a ranar Laraba, Tracy Ohiri ta zargi ministan da duka da kuma kin biyan kuɗin wasu kayan yakin neman zaɓe.

ADC Da NNPP Sun Yi Watsi Da Sabuwar Dokar ZabeJam’iyyun adawa na ADC da NNPP sun yi watsi da sabuwar dokar gyaran zaɓe t...
26/02/2026

ADC Da NNPP Sun Yi Watsi Da Sabuwar Dokar Zabe

Jam’iyyun adawa na ADC da NNPP sun yi watsi da sabuwar dokar gyaran zaɓe ta 2026 da shugaba Bola Ahmad Tinubu ya sanya wa hannu, suna zargin cewa dokar na barazana ga dimokraɗiyya tare da yunƙurin karkatar da ƙasar zuwa tsarin jam’iyya ɗaya.

Shugaban NNPP na ƙasa, Ajuji Ahmad, ya bayyana hakan a Abuja a madadin jam’iyyun adawa, inda ya ce za su bi duk hanyoyin doka domin kalubalantar dokar tare da hana aiwatar da wasu tanade-tanaden da s**a ce ba su dace ba.

Jam’iyyun sun kuma bukaci majalisar dokoki ta tarayya ta sake nazarin dokar domin gyara sassan da ake takaddama a kai, tare da tabbatar da sahihin zaɓe mai ‘yanci, gaskiya da adalci a Najeriya.

Address

No. 179 Durumin Iya
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kobo Da Kobo posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share