Mukhtar Ibrahim Abba FX

Mukhtar Ibrahim Abba FX NEWS ABOUT ISLAMIC MOVEMENT OF NIGERIA
(1)

Ina godiya ga Matar Sheikh Zakzaky wadda tayi magana a wannan wurin, ita din Mahaifiyar Shahidai shida ce, Yayan ta guda...
28/12/2023

Ina godiya ga Matar Sheikh Zakzaky wadda tayi magana a wannan wurin, ita din Mahaifiyar Shahidai shida ce, Yayan ta guda uku a Hadisa(Waki'a) guda, da wasu ukun suma a Hadisa(Waki'a) guda sun yi Shahada, kuma ita wannan Mata ta yi hakuri(ta tsayu kyam) tamkar tsauni, ta jure zaman Kurkuku da wahalhalu na tsawon lokaci.

_Sayyid Ali Khamene’i

25/12/2023

Happy Christmas 🎄

25/12/2023

Happy Christmas 🎁🎄

Today's best photo❤❤❤❤❤❤❤                    • 
19/12/2023

Today's best photo
❤❤❤❤❤❤❤

























A GAGGAUCE......AL'AMARIN GAZA DAKE FALASDINU.....Dakarun Musulunci na Ƙasar Yemen sun hana jiragen ruwan Isr**la da ke ...
15/12/2023

A GAGGAUCE......

AL'AMARIN GAZA DAKE FALASDINU.....

Dakarun Musulunci na Ƙasar Yemen sun hana jiragen ruwan Isr**la da ke wucewa ta mashigin Bab el Mendeb zuwa ƙasar.

Dakarun sun harba makami mai linzami kan wani jirgin ruwan da ke da alaka da Isr**la, "Maersk Gibraltar" (mai tutar Hong Kong).

Asibitin "Soroka" da ke Bir Al-Sabi' ya sanar da cewa sun karɓi wasu sojojin Shaidan guda 35 da s**a samu raunuka a Gaza cikin sa'o'i 24 da s**a gabata.

A wannan Asibitin kadai ya rubuta Sojojin Shaidan 2,148 s**a ji rauni tun ranar 7 ga Oktoba.

A halin da ake ciki, Asibitin "Beilinson" da ke "Tel Aviv" ya ba da rahoton wasu sabbin sojoji uku na Isr**la da s**a jikkata, tare da wasu 19 da ake yi wa jinya a can.

Muhd Bala Afuwa

Taron Tunawa da Waƙi'ar Buhari Ta 12/12/2015 Daga Birnin Karbala/IraqiƳan uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky(H) dake ...
15/12/2023

Taron Tunawa da Waƙi'ar Buhari Ta 12/12/2015 Daga Birnin Karbala/Iraqi

Ƴan uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky(H) dake karatu a ƙasar Iraqi dasu haɗa Najaf da Karbala, sun gabatar da taron tunawa da waƙi'ar Buhari ta 12/13/14 December, 2015 a garin Zaria. Inda a gabatar da taron ɗakin taro na makarantar Ma'ahad Warith Al-Anbiya'i a birnin Karbala dake ƙasar Iraqi.

Da fari Shaikh Mahdy Ɗahiru Sanda Sokoto, shine ya gabatar da maƙala da a rubuta da harshen Larabci, wacce take ɗauke da taƙaitaccen tarihin waƙi'ar Buhari ta 2015 da irin abubuwan dasu gudana har zuwa bayan waki'ar.

Sayyid Ja'afar Azzamiliy, shine ya kasance baƙo na musamman daya gabatar da jawabi a wurin, inda a cikin jawabin nasa ya bayyana yadda addinin musulunci ya yi hani da kisa bisa zulumci. Sannan ya jinjinawa Shahidanmu tare da addu'ar ƙarin kusanci a wurin Allah Ta'ala.

Shaikh Yaseer Alhasan Funtua, shima ya gabatar da taƙaitaccen jawabi na bada labarin yanayin da su samu kansu a waƙi'ar, da irin musibu da tsantsar ta'addancin dasu gani a wannan waƙi'a.

Daga ƙarshe, ƴan uwa ɗalibai sun gabatar da kyauta ta musamman ta girmamawa ga babban baƙo na kyakykyawan hoton su jagora Shaikh Zakzaky(H). Sannan waƙoƙin Azaa (na ambaton mazlumiyar su jagora da Shahidai) su biyo baya daga ƴan uwa, sannan daga bisa a rufe taron da addu'a.

— Abbakar Ibraheem Kudan.
14/12/2023

AFIRKA.....Solomon Kalushi Mahlangu, wadda aka haifa ranar 10 ga Yuli 1956, an kashe ki ta hanyar rataya ranar 6 ga Afri...
11/12/2023

AFIRKA.....

Solomon Kalushi Mahlangu, wadda aka haifa ranar 10 ga Yuli 1956, an kashe ki ta hanyar rataya ranar 6 ga Afrilu 1979, ɗan gwagwarmayar ƴancin Afirka ta Kudu ne, mai fafutuka a jam'iyyar African National Congress (ANC).

Gabadaya Solomon ya fara gwagwarmayar sa zuwa ƙare war rayuwar sa cikin Shekaru 23, Matashi ne mai burin yaga Afirka da ɗan Afirka sun shaƙi iskar ƴanci, daga cikin kalaman sa na ƙarshe dab da za'a rataye shi yana cewa.

"Ku gaya wa mutanena cewa ina son su, kuma dole ne su ci gaba da wannan yaƙin (Na samun ƴancin Afirka daga Mulkin mallakar turawa), jinina zai ciyar da bishiyar da zata ba da ƳaƳan ƴanci."

Waɗannan su ne kalmomin sa na ƙarshe da fitaccen mai fafutukar ƴancin walwala, Solomon Kalushi Mahlangu ya faɗa, kafin gwamnatin wariyar launin fata ta lokacin ta kashe shi.

Yak**ata Afirka da ƴan Afirka ku san gwarazan ku.

Yaushe Afirka zata farka, yaushe talakan nahiyar zai shaƙi iskar ƴanci?.

Muhd Bala Afuwa

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIU'UN 😭Allah ya yiwa Sayyid Muhammad Baƙir Al-Fali rasuwa ɗaya ne daga cikin Malamai masu...
10/12/2023

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIU'UN 😭

Allah ya yiwa Sayyid Muhammad Baƙir Al-Fali rasuwa ɗaya ne daga cikin Malamai masu hidima ga wannan tafiya ta Ahlul Baiti (a.s) , Sayyid Muhammad ya tafi da rayuwar sa wajen hidimar ilmin gidan Annabta da yaɗa shi musamman a fagen Mimbari , za'a yi jana'izar sa da zarar an kammala shirye shirye tare da dawo dashi daga birnin Tehran ɗin Jamhuriyyar Musulunci ta Iran .
Muna roƙon Allah ya jadadda masa rahama da gafara Bihaqqil Hussain (a.s) .

Nice Pic My Holy Dad
09/12/2023

Nice Pic My Holy Dad

YANZU YANZU: Ɗaruruwan matasa ne a birnin Zariya s**a fito domin ƙaddamar da zanga-zangar lumana na kira da ayi adalci k...
06/12/2023

YANZU YANZU: Ɗaruruwan matasa ne a birnin Zariya s**a fito domin ƙaddamar da zanga-zangar lumana na kira da ayi adalci kan musulmi da Sojoji s**a halaka a Kaduna
Da A 2015 Kun hi haka mana Amma saboda Su wa inchan Yan Shia ne su kuma yan shia bah mutane Bah ko kuma bah Musalamine bah Ina da da tambaya Wai shin Kuwa kusan Iya Adadadin mutane da s**a rasa iyayansu kusan iya adadadin da mutanan da s**a rasah yayansu
12 December is loading
Ranar da bana fatah na kara ganin rashin imani da akai A ranar

02/12/2023
CHANJI KO SAUYI? GA MAFITA. Da yawan mutane kowa burin sa shine wannan rayuwar da muke yinta a Doran Duniyar nan, ya sam...
30/11/2023

CHANJI KO SAUYI? GA MAFITA.

Da yawan mutane kowa burin sa shine wannan rayuwar da muke yinta a Doran Duniyar nan, ya samu sauki aduk lamuran sa na yau da kullun.

Da yawa na furta muna son canji-canji amma kuma a zuciyo yinsu ƙarya suke sanan kuma basu shirya ai chanjin ba.

Allah (S.w.t) yana faɗi cikin littafin sa mai tsarki. "LALLAI ALLAH BAYA KAWO MA WASU MUTANE SAUYI HAR SAI WA YAN NAN MUTANEN SUN SAUYA DA KANSU SAI ALLAH YA TAI MAKE SU"

Tambaya.Tunanin mu wasu ne zasu zo suyi mana komai? Amsa: A a , dole mune zamu tashi muyi da kan mu . In muka yi yanzu ƴaƴan mu da jikokinmu sun huta, amma in ba muyi ba, to har jikokin-jikokin mu zasu taso a kangin wahala harsai an samu wanda zasu tashi tsaye.

Dole mu nuna wa duniya Bamu yarda da tsarin kafirci ba (DEMOCRATIC) Mu tsarin Alqur'ani muke so (ISLAMIC).
Wanan shine ya hau kanmmu, Saboda Da Bara'a Ake Tabbatar Da Wulaya.

Muna kira ga ɗaukacin Musulmai mu tashi mu nuna rashin goyan bayan mu ga kafirci da kuma mulkin kafurci.

MULKIN NIGERIA MULKIN TURAWANE,MULKIN TURAWA MULKIN KAFURCI NE.

SHAHADAR SAYYADA ZAHRA (SA)😭😭muna mika ta'aziyarmu ga manzon allah (saww) muna mika ta'aziyarmu ga imam ali (as) muna mi...
29/11/2023

SHAHADAR SAYYADA ZAHRA (SA)😭😭
muna mika ta'aziyarmu ga manzon allah (saww) muna mika ta'aziyarmu ga imam ali (as) muna mika ta'aziyarmu ga imam hassan da hussain (as) da sauran imamai (as) gaba daya muna mika ta'aziyarmu ga sahibuz asr wazzaman (AJFT) muna mika ta'aziyarmu ga maulaya sayyid zakzaky (h) na rashin kakarshi sayyada zahra (as) muna mika ta'aziyarmu ga sauran muminai na duniya baki daya wa maulaty😭💔

Sheikh Dr Ibraheem Zakzaky tare da Syed Hassan Ahmad Khomeini, Jikan Imam Khomeini kenan.Allah ya ƙara tsawaita mana kwa...
24/11/2023

Sheikh Dr Ibraheem Zakzaky tare da Syed Hassan Ahmad Khomeini, Jikan Imam Khomeini kenan.

Allah ya ƙara tsawaita mana kwananku taurarin gwagwarmayar Addinin Musulunci.

MUNA TAYA MANZON ALLAH DA SAYYIDI ALI DA NANA FADIMATU MURNA.....A irin wannan Rana, Shekara ta 5 ko ta 6 bayan Hijira a...
20/11/2023

MUNA TAYA MANZON ALLAH DA SAYYIDI ALI DA NANA FADIMATU MURNA.....

A irin wannan Rana, Shekara ta 5 ko ta 6 bayan Hijira aka haifi Jarumar Karbala, As-Sayyida Zainabul Kubra (S.A), Ƴar Shugabar Muminai Imamu Ali (as), kuma Ƴar Shugabar Matan Duniya da Lahira Sayyida Az-Zahra (S.A) Ƴar Manzon Allah (Saww), kuma Ƴar uwar Imamu Hasan da Imam Husain (as) Shugabannin Ƴan Aljannah. Kuma An haife ta ne a Garin Madina mai haske.

ALKUNYAR TA: Ana yi mata Alkunya da Ummu Kulthuum, Ummu Abdillah, da kuma Ummu Hasan.

ALLAH SWT NE DA KANSA YA SA MATA SUNA ZAINAB...

Ya zo a cikin Littafin Rayahinus-Sahari'ati cewa: A lokacin da aka haife ta Ma'aiki (Saww) yana halin Tafiya ne, sai Mahaifinta Amirul Mu'uminina (as) ya ce: "Ba zan rigayi Manzon Allah (Saww) ba a wajen saka mata Suna".

A lokacin da Ma'aiki (Saww) ya dawo, ya kasance yana jiran saukar Wahayi, sai Jibril (as) ya sauko yace da Shi: Allah yana karanta Sallama a gare Ka, ya ce da Kai: "Ka saka mata suna Zainab, haƙiƙa mun rubuta wannan Sunan a cikin Lauhul Mahfuz".

Sannan Ma'aiki ya sa aka zo da ita ya sumbace ta sannan ya ce: "Ina yin Wasiyya ga Mahalarta da kuma waɗanda ba su halarta ba a nan kan cewa Su kiyaye wannan Ƴar saboda Ni, ita mak**anciyar Khadijatul Kubrah ce".

Nutsuwar ta da Sakinarta ta yi k**a da Khadijatul kubrah. Ismarta da Kunyarta ta yi k**a da Fadumatuz-Zahrah (S.a). Fasaharta da Balagarta kuwa ta yi k**a da Aliyyul Murtadha (as). Hakurinta da Dauriyarta kuwa irin na Hasan Almujtaba (as) ne. Jaruntarta da Sadaukantakar ta kuwa ta yi k**a da Sayyidus-Shuhadah (as).

Madogara; Littafin Rayahinus-Shari'ati Juzu'i na 3 Shafi na 38.

DARAJOJINTA DA MARTABOBINTA DA KUMA ILMOMINTA....

Ibnu Hajar a cikin Littafinsa na Al-Isaabah, da kuma Ibnu Athir a cikin Usudul gaba, sun tabbatar a cikin Tarjamar da s**a yi mata suna cewa: Zainab (S.A) ta kasance Mace ce mai kaifin Hankali, kuma mai zurfin hankali, Jaruma... Shahararriyar Maganar ta ga Yazidu Dan Mu'awiyya yana nuna irin kaifin Hankalin ta da k

A GAGGAUCE.....Dakarun Musulunci tsagin Lebanon sun kakkabo jirgin saman Dakarun Shaidan ta hanyar amfani da makami mai ...
18/11/2023

A GAGGAUCE.....

Dakarun Musulunci tsagin Lebanon sun kakkabo jirgin saman Dakarun Shaidan ta hanyar amfani da makami mai linzami a yankin Al-Jalil.

Akalla Falasdinawa 150 ne aka kashe a harin da Dakarun Shaidan s**a kai jiya cikin dare a Gaza.

Dakarun Shaidan sun umarci mutanen da ke cikin Asibitin Al-Shifa da su fice cikin sa'a ɗaya, Umarnin ya jefa tsoro tsakanin marasa lafiya, ma'aikatan lafiya, da Iyalan marasa lafiyan bayan ance su fice nan da sa'a guda.

An bar mutane kimanin 120 a Asibitin saboda basa iya tafiya, kuma babu abinda za'a iya musu na tallafi.

Muhd Bala Afuwa

A Hukumance; Dakarun Musulunci tsagin Falasdinu sun lalata tankokin yaƙin Rundunar Shaidan guda 160, daga Ranar 7 ga wat...
12/11/2023

A Hukumance; Dakarun Musulunci tsagin Falasdinu sun lalata tankokin yaƙin Rundunar Shaidan guda 160, daga Ranar 7 ga watan Oktoba zuwa yau 12 ga Nuwamba.

Wadannan tankokin, da mutum zai samu kuɗin guda 1 daga cikin su tabbas da kakarsa ta yanke saƙa, shi da Talauci saide in a C**a ya sanya kuɗin aka masa bugu 1 aka kwace, wannan kenan, ba mu kai ga jin lissafin jimillar nawa Dakarun Musulunci tsagin Lebanon s**a lalata ba.

Ko yanzu kasuwa ta watse, ɗan koli yaci riba, Shahidai tasu tayi kyau, ko ba komi muna da tabbacin suna cikin yardar Allah. Kuma yankin Falasdinu da Dakarun Shaidan s**a mamaye wuraren shekaru 75, da Iznin ubangijin Ka'abah sai an ƴanta wuraren.

Muhd Bala Afuwa

🛑 DA ƊUMI-ƊUMI | IRAN ta sanar da fara shirin haɗa rundunar soja gobe juma'a, a wani shiri na zaman ko ta kwana.Ministan...
26/10/2023

🛑 DA ƊUMI-ƊUMI |

IRAN ta sanar da fara shirin haɗa rundunar soja gobe juma'a, a wani shiri na zaman ko ta kwana.
Ministan tsaron ƙasar IRAN ya ƙara da cewa: “ matuƙar sojojin is'''raa''ila s**a yi gangancin shiga zirin gaza, to su tabbatar sun kai kansu ne a maƙabarta”.

SHUKAR BUHARI MUKE GIRBA A WANNAN MULKINWato tarihin Ƙasar nan ba zai taɓa cika ba har sai an ambaci Buhari a matsayin m...
26/10/2023

SHUKAR BUHARI MUKE GIRBA A WANNAN MULKIN

Wato tarihin Ƙasar nan ba zai taɓa cika ba har sai an ambaci Buhari a matsayin mutumin da yafi kowani mai mulki rashin iya mulki da kuma cutar al'ummar Ƙasar nan.

A ƙarƙashin mulkin Buhari NNPC da CBN s**a zamanto mallakar wasu tsirarun mutane da sai yadda suke so ne zai faru a Ƙasar nan. Su ne kuma mahangar tattalin arziƙin Ƙasar nan.

A ƙarƙashin mulkin Buhari hukumar EFCC ta bankaɗo kwagilolin fiye da Naira Tiriliyan 2 wanda an fitar da kuɗaɗen, ba a aiwatar da ayyukan ba. Babu kuma wanda aka nuna da yatsa ballantana a tsangwama.

A ƙarƙashin mulkin Buhari harkar tsaro ta koma kasuwanci mafi riba tsakanin jami'an tsaron Ƙasar nan.

Tsakanin al'ummar Ƙasar nan da Buhari sai dai mu yi fatan Allah ya masa irin ruƙon da ya yiwa Ƙasar nan, dan alfarmar Annabi Muhammadu (SAW).

26/10/2023

Mene ne laifi idan ka dangwalawa ɗan’uwanka ‘Like’ da niyyar ƙarfafa shi a Facebook.

Muna da marubuta masu tasowa a wannan kafa ta “Facebook” ta yaya zamu ƙarfafesu,? Suna yin rubututtuka masu amfanin gaske, amma haka za ka ga an barshi ba mai kulawa ballantana ya yi musu ‘Like ko comments,’ Irin wannan rashin ko na kula ɗin yana sare ma da yawa daga cikin su gwiwa, kuma haka na sabbaba mu rasa su, na san akwai wani Mentality na ƴan’uwa a wannan soshiyal midiya ɗin na ganin idan s**a yi maka "Like ko Comments" k**ar sun taimaka maka ne.

Kada kace: “Idan har don Allah suke yi baza su damu da like ko comments ɗin kowa ba.”

Mun san da wannan amma komai yana buƙatar ƙarfafa ai, akwai waɗanda muke tare da su ake musu ganin manyan marubuta ne a wannan kafa da ace za su ƙarfafi irin waɗannan da like ɗin su ko comments, kai idan ya rubuta abu mai kyau sosai ma kayi "Sharing" hakan zai ƙarfafeshi wajen dagewa sosai.

Dalilin irin waɗannan abubuwan dake faruwa a tsakaninmu yasa wasu ba'adin ƴan’uwa s**a koma rubuta shirme saboda an fi mayar da hankali kan shi, misali k**ar haka: “Da ace zaka rubuta abu kan Jawabin Sayyid (H), ba a cika mayar da hankali kan sa ba. Amma idan a kan soyayya ka rubuta sai kaga an yi ɗuuu a kan sa sama da wancan.”

Yanzu abin da yake gudana kenan a tsakanin mu, kuma yana da kyau mu gane ya k**ata mu canza wannan abin, a wannan ɓangaren wallahi amawa sun fi mu haɗin kai, ka shiga Pages ɗin su kaga yadda suke ƙarfafa junan su, sai kana da abokai Amawa za ka gane mai nake faɗa, idan kuma kana tunanin ba haka bane abin da nake faɗa, ka shiga (Timelines) ɗin wasu ƴan’uwa, sannan sai ka koma na amawa mutanen gari, anan zaka fahimci abin da nake faɗa.

Amma sai ka rasa irin waɗannan ƴan’uwan da za ka dinga ganin su a shafukan wasu Jaridun Online da wasu shafukan wasu sanannu a wannan kafar suna yi musu comments da likes mai suke yi a lokacin da ɗan’uwansu shi ma yake baza fikirarsa wajen yin rubutu. Sai na rasa shin neman suna ya k**ata mu kira shi, ko neman wajen zama, ko shishshigi, kai ko nace wulaƙanta kai. Zaka ga da za a samu saɓanin fahimta ya soki abin da suke so, sai su koma faɗar ba muyi tunanin haka daga gare ka ba. Bayan tun farko su s**a yi kuskuren bashi wannan amincin.

Tabbas wannan gaskiya ce mai ɗaci, amma buri na shi ne mu fi ƙarfin zuciyoyinmu mu amshi wannan gaskiyar. Tabbas muna aiki saboda Allah ne a wannan kafar ta Fesbuk, amma akwai abubuwan da zasu ƙarfafemu wajen Inganta ayyukanmu a waɗannan kafafen da muka bayyana.

Idan mutum yana yin rubutu, mu kuma muna daure wa mu fi ƙarfin zuciyoyinmu muna yi mishi ‘like da Comments’, wallahi hakan zai ƙarfafe shi.

Ƙiri-ƙiri mutum yana jin daɗin Posting ɗin ka a duk lokacin da kayi, amma ɗan like ɗin da zai danna maka, shi ne bazai yi ba, sai dai yayi Scrolling down ya wuce. Wasu a tunaninsu ma idan s**a yi maka Like ko Comment taimaka maka s**a yi. Musamman ƴan'uwa da muke tarayya da su a wannan kafar, sai kaga mutum yana kyashin yi maka Like ko Comment. Kuma yana jin daɗin Posting ɗin ka.

Amma tsabar neman suna, sai ka tsince su can shafukan Celebrities ko kuma manya-manyan Jaridu suna yin Comment da Liking, Amma nan sun ƙi tsayawa su mayar da shafin ɗan'uwansu Shahararre. Wallahi idan kaga shafin ɗan'uwa a wannan sahar yana da yawan Likers da Commenters, to wallahi amawa (mutanen gari) ya tara a shafin shi da yawa. Sun fi ƴan'uwa yawa a shafin nashi. Saboda su basa kyashin yi maka liking. Ban ce kada ayi musu like ko Comments ba waɗanda ake cewa Celebrities.

Ni wallahi ina sane wata rana nake rubuta kuskure nayi Posting, don na gane masu bibiya ta. Amma ba zaka gansu suna yi maka Like ko Comment ba a duk Posting ɗin ka.

To idan ma ba zaka yi hakan don Allah ba, to akwai tsarin da Fesbuk s**a yi yanzu akan ‘Like da Comment’ a wannan kafa ta Fesbuk. Kuma tsakani da Allah ni abin yayi matuƙar burge ni, ganin yadda wasu ke rayuwa a wannan kafa ta Fesbuk ɗin. Duk da wannan tsarin ya ɗan jima, amma wasu na ɗan tambaya akan Malam wane mun dena ganin Posting ɗin ka a fesbuk, ko ka dena ne.? Sai nace musu: Idan ka dena ganin Posting ɗin ɗaya daga cikin abokanka na Fesbuk, yana da alaƙa da rashin “Like ko Comment ”ɗin ka a duk Posting ɗin da yayi.

Saboda haka idan kana son ganin Posting ɗin ɗaya daga cikin abokanka na Fesbuk kana buƙatar ka dinga bibiyar abubuwan da ya rubuta ta hanyar yi mishi “Liking ko Comment”. Hakan ne zai baka damar ganin duk Post ɗin da yayi sabo, idan kuma ba za kayi hakan ba, idan ka dena ganin Posting ɗin shi kar ka tambayi mutum ka dena ganin shi.

To ka sani idan baka yi hakan ba, hukumar da ke gudanar da Fesbuk suna ganin k**ar ma baka buƙatar shine. Shi yasa suke ɓoyeshi daga gare ka, daga ƙarshe ma su cire maka shi ta hanyar Unfriending ɗin shi daga Friend list ɗin ka.

Yana dakyau mu gane hakan. Ayi min Afuwa.

-Aba Sajjadi.

26/10/2023

Isr**la ta kwashe wasu mutanan ta da suke iyaka da Lebanon kimanin dubu ɗari da Ashirin da biyar 125,000, saboda yadda Hez**llah suke ƙara kusantar wurin.

Da yammacin nan, sun tashi da Sunan Allah zuwa ga Qiryat Shemona ta Isr**la, Dakarun Allah tsagin Lebanon ne s**a tura s...
25/10/2023

Da yammacin nan, sun tashi da Sunan Allah zuwa ga Qiryat Shemona ta Isr**la, Dakarun Allah tsagin Lebanon ne s**a tura saƙon.

25/10/2023

Bayan Saudiyya ta koka dangane da kisan Mata da yara da Isra**la keyi a Falasdinu, daga ƙarshe ta kwashe Ma'aikatan ta dake Lebanon sun fece, bayan hare-haren Hez**llah sun yawaita a Isr**lan.

AKWAI ƘURA FA, DON ZAKUNAN LARABAWA SUN GANA A TSAKANIN SU.....Yau Laraba, 25 ga Oktoba 2023, Babban sakataren Ƙungiyar ...
25/10/2023

AKWAI ƘURA FA, DON ZAKUNAN LARABAWA SUN GANA A TSAKANIN SU.....

Yau Laraba, 25 ga Oktoba 2023, Babban sakataren Ƙungiyar Hizbullah, Sayyid Hassan Nasrallah, ya karɓi bakuncin Mr. Ziad Nakhala, babban sakataren kungiyar Islamic Jihad a Falasdinu, da Sheikh Saleh Al-Arouri, mataimakin shugaban hukumar siyasa ta Hamas. Sun yi nazarin abubuwan da s**a faru na baya-bayan nan a Zirin Gaza tun bayan fara aikin farmakar Isra'ila da Hamas s**ayi a ranar 7 ga Oktoba, wadda s**a sanya masa suna 'Ambaliyar ruwa ta Al-Aqsa' da kuma ci gaban da aka samu a dukkan matakai, da kuma tashe-tashen hankulan da aka samu a kan iyakokin Lebanon da Falasdinu da Isra'ila ta mamaye.

Sun tattauna akan abinda ya shafi dokokin ƙasa da ƙasa da na shiyya-shiyya da abin da ya k**ata ɓangarorin gwagwarmayar su yi a cikin wannan yanayi mai matukar muhimmanci, don samun nasara ta haƙiƙa da tsayin daka a Gaza da Falasdinu, da kuma dakatar da ha'inci da zalunci kan al'ummarmu da ake zalunta a Gaza da kuma West Bank.

Sun amince da ci gaba da daidaitawa da kuma bin diddigin abubuwan da ke faruwa a yankunan.

Muhd Bala Afuwa

25/10/2023

China ta soki rahoton Amurka kan faɗaɗa ayyukan sojinta inda ta mayarwa Amurkan martani da cewa ita ce take taimakon Isra'ila da Ukraine da kuma kafa sansanonin soji a fadin duniya.

Address

Miltara
Kano

Telephone

+2348108210531

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mukhtar Ibrahim Abba FX posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mukhtar Ibrahim Abba FX:

Videos

Share