Fasaha Hausa Media

Fasaha Hausa Media Ilimantarwa
Nishaɗantarwa
faɗakarwa

Ingantattun Labarai Na Ciki Da Wajen Kasa A Koda Wanne Lokaci.

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Fatima Rabi'u Lawal Ta Rãșu Sakamakøɲ Haihuwa'Yan uwanta sun bukaci jama'a da su yi...
14/08/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Fatima Rabi'u Lawal Ta Rãșu Sakamakøɲ Haihuwa

'Yan uwanta sun bukaci jama'a da su yi mata addu'ar samun rahama.

Ku cire ni daga cikin masu fafutukar neman hakkokin mata.Idan neman hakkokin mata yana nufin watsar da dabi’u na gari da...
13/08/2025

Ku cire ni daga cikin masu fafutukar neman hakkokin mata.

Idan neman hakkokin mata yana nufin watsar da dabi’u na gari da raina maza.

Idan yana nufin kawo rarrabuwar kawuna tsakanin miji da mata, to ni ba zan kasance a cikinsa ba.

Na yarda da mutunta juna, ba yaƙin jinsi ba.

Na yarda da gina aure, ba rushe shi ba.

Ku ji ni da kyau, KU CIRE NI DAGA CIKIN MASU NEMAN HAKKOKIN MATA.

Aurenmu dole ne ya yi nasara.

~Cewar Stella Justice Esq.

13/08/2025

Mene ne Ma'anar 'MU JE MAHAA' Da Ake Yawan Faɗi a Comment Section?

Majalissar Matasa Ta Kasa Reshen Jihar Katsina NYCN Sun Gudanar Da Bikin Ranar Matasa Ta Duniya (International Youth Day...
12/08/2025

Majalissar Matasa Ta Kasa Reshen Jihar Katsina NYCN Sun Gudanar Da Bikin Ranar Matasa Ta Duniya (International Youth Day).

Majalisar Matasa ta Kasa (NYCN) reshen jihar Katsina ta shirya taron musamman domin bikin Ranar Matasa ta Duniya, wanda ake gudanarwa a duk shekara domin kara wayar da kan matasa kan rawar da suke takawa wajen ci gaban kasa.

Taron ya samu halartar manya manyan mutane na fadin jihar katsina, shugabannin matasa daga sassa daban-daban na jihar, kungiyoyin fararen hula, dalibai da wakilan hukumomin Gwamnati.

An gudanar da jawabai da dama masu karfafa gwiwa, inda aka tattauna kan muhimmancin matasa a harkokin siyasa, ilimi, sana’o’i da kuma ci gaban tattalin arziki.

Da yake jawabi a lokacin taron, shugaban majalisar Hon. Yusuf Abubakar Papa, ya yi kira ga matasa da su rungumi zaman lafiya, hadin kai da kuma yin amfani da damammakin da suke da shi wajen inganta rayuwarsu da ta al’umma baki daya.

Ya kuma gode wa duk masu ruwa da tsaki da s**a tallafa wajen ganin taron ya yi nasara.

Gwamnan jihar Katsina wanda ya samu wakilcin Mataimakinsa Hon. Faruk Lawal Jobe ya bayyana cewa ranar Matasa ta Duniya tana tuna mana muhimmancin matasa a matsayin ginshiƙin ci gaban kowace al’umma da ƙasa.

Ya kara da cewa, Gwamnatin jihar na da niyyar ci gaba da tallafawa shirye-shiryen da ke rage rashin aikin yi da bunkasa ƙwarewar matasa.

Sauran mutanen da s**a yi jawabai na kwarin gwiwa da cigaban matasa a wajen taron sun hada da; Kwamishinar mata ta jihar Katsina Hajiya Hadiza Yar’adua, shugaban hukumar cigaban jihar Katsina Dr. Mustapha Shehu, shugaban hukumar KATDICT Alhaji Naufal Ahmad, Sadaukin Kasar Hausa Dr. Haruna Maiwada da sauaransu.

Taron wanda ya gudana a ranar Talata 12/8/2025 a dakin taro na Bello Kofar Bai ya gudana cikin yanayi na nishadi, tare da gudanar da wasu wasanni da nuni na al’adu domin kara hadin kai tsakanin matasa.

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Bayyana Kisan Ɓarayin Daji Da Dama A Jihar Zamfara...A wani harin sama da rundunar ta kai g...
12/08/2025

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Bayyana Kisan Ɓarayin Daji Da Dama A Jihar Zamfara...

A wani harin sama da rundunar ta kai ga ɓarayin dajin a dajin Makakkari da ya ratsa ƙananan hukumomin Anka da Bukuyum jihar Zamfara yayi sanadiyyar mutuwar ɓarayin sama da Ɗari.

Wasu hotunan basu da daɗin gani kuma ba zasu sanyu nan ba.

Muhammad Aminu Kaber

TIRƘASHI:Wannan itace budurwar da tasha fiya-fiya ta mvtu saboda za'a yi mata Auran dole, a karamar hukumar Bakori, jiha...
30/07/2025

TIRƘASHI:Wannan itace budurwar da tasha fiya-fiya ta mvtu saboda za'a yi mata Auran dole, a karamar hukumar Bakori, jihar Katsina.

ALLAHU AKBAR:Ambaliyar Ruwa Ya cinye Makabartu a Maiduguri. Allah ubangiji ya kare na gaba Amin.
30/07/2025

ALLAHU AKBAR:Ambaliyar Ruwa Ya cinye Makabartu a Maiduguri.

Allah ubangiji ya kare na gaba Amin.

DA ƊUMI-ƊUMI: Yadda ruwan sama ya mamaye wasu unguwanni a birnin Maiduguri da ke jihar Borno, bayan kwashe kimanin awann...
30/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Yadda ruwan sama ya mamaye wasu unguwanni a birnin Maiduguri da ke jihar Borno, bayan kwashe kimanin awanni biyar ana sheƙa ruwa sama.

CIKIN HOTUNA:Uwargidan Gwamnan Bauchi, Hajiya Aishatu Bala Mohanmed Kenan, A Cikin Kicin Tana Dafawa Mijinta Abinci.
30/07/2025

CIKIN HOTUNA:Uwargidan Gwamnan Bauchi, Hajiya Aishatu Bala Mohanmed Kenan, A Cikin Kicin Tana Dafawa Mijinta Abinci.

INNALILLAHI WAINNA'ILAHI RAJI'UN: Allah ya yiwa Jarumin Masana'antar fina-finai na Nupe a Jihar Neja, Prince Ahmed Tsado...
29/07/2025

INNALILLAHI WAINNA'ILAHI RAJI'UN: Allah ya yiwa Jarumin Masana'antar fina-finai na Nupe a Jihar Neja, Prince Ahmed Tsado rasuwa.

ALLAHU AKBAR: Jiya Akayi Jana'izar Matasa 7 ƴan Asalin Garin Ɗanbatta Da S**a Rasu Asanadin hatsarin mota yayin da wasu ...
28/07/2025

ALLAHU AKBAR: Jiya Akayi Jana'izar Matasa 7 ƴan Asalin Garin Ɗanbatta Da S**a Rasu Asanadin hatsarin mota yayin da wasu mutum 7 ke kwance a asibitti.

Allah Yajikan Su Da Rahama 🤲🏿

CIKIN HOTUNA:shugaban ƙasar Gambiya Adama Barrow ya kai ziyarar ta'aziyya ga iyalan tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhar...
25/07/2025

CIKIN HOTUNA:shugaban ƙasar Gambiya Adama Barrow ya kai ziyarar ta'aziyya ga iyalan tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura jihar Katsina.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fasaha Hausa Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fasaha Hausa Media:

Share