Garko Reporter's TV

Garko Reporter's TV Muryar Marassa Murya 📚🖊🎤

28/08/2026

BIDIYO:-Yadda Hon Baban Tatu Garko ke bayyana nagartar Abdullahi Mahmud Gaya yake da ita a yankin Kano ta Kudu.

Babantatu ya yi wannan jawabi ne lokacin da ya ja wata tawaga don kai wa Abdullahi Mahmud Gaya ziyara a gidansa.

Me za ku ce?

27/08/2026

Jawabi Daga Wani Ɗan Takarar Kansila A Kano

DA DUMI-DUMI: Ana fargabar mutuwar mutane 40 bayan kwale-kwale ya Kife a SokotoAna fargabar mutuwar mutane kusan 40 baya...
20/08/2026

DA DUMI-DUMI: Ana fargabar mutuwar mutane 40 bayan kwale-kwale ya Kife a Sokoto

Ana fargabar mutuwar mutane kusan 40 bayan wani kwale-kwale da ke dauke da manoma da ma’aikatan gonakin shinkafa ya kife a Gorau, da ke karamar hukumar Goronyo a Jihar Sokoto kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Lamarin ya faru ne lokacin da mutanen ke tsallaka wani rafi domin zuwa gonakinsu, inda rahotanni s**a ce kwale-kwalen ya kife jim kadan bayan ya tashi.

Wani ganau ya ce sama da mutane 70 ne ke cikin kwale-kwalen a lokacin da hatsarin ya afku, ciki har da yara masu shekaru tsakanin 10 zuwa 15.

An kuma ce hakimin kauyen yana cikin wadanda ke cikin kwale-kwalen, sai dai an samu nasarar ceto shi.

Wani dan jaridar yankin, Sharhabilu Yahuza Kiliya, wanda ya kasance a wurin da lamarin ya faru, ya ce zuwa yanzu an gano gawarwaki kusan 40, yayin da aka ceto mutane shida, ciki har da hakimin kauyen.

Ya bayyana cewa wadanda abin ya shafa sun hada da manoma da ma’aikatan da aka dauka domin aikin girbin shinkafa.

A halin yanzu, ana ci gaba da aikin ceto, yayin da masu ruwa na yankin ke neman mutanen da har yanzu ba a gano inda suke ba tare da kuma fitar da gawarwakin wadanda s**a rasu.

CIKIN HOTUNA:-Gwamnatin Jihar Kano ta tura ƙwararrun injiniyoyi zuwa Karamar Hukumar Garko domin gudanar da bincike da t...
19/08/2026

CIKIN HOTUNA:-Gwamnatin Jihar Kano ta tura ƙwararrun injiniyoyi zuwa Karamar Hukumar Garko domin gudanar da bincike da tantance wuraren da zaizayar ƙasa ta shafa a Tsohuwar Kasuwar Garko da Rariyawa.

Ziyarar, da aka gudanar yau Laraba, 19 ga Agusta, 2026, ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru M. Hashim, na daga cikin matakan shirin magance matsalar.

Al’umma na fatan za a gaggauta fara aikin domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

GARKO REPORTER’S TV — Muryar Al’umma.

Hotuna:-Usssini Muhm Garko

17/08/2026

DA DUMI DUMI:-Musa Mai Sana'a Yasha Da ƙyar Lokacin Da Yake Tallata Tinibu A Jihar Katsina.

Allah Ya kiyaye Gaba

16/08/2026

DA ƊUMI ƊUMI:-Jami’in tattara sakamakon zaɓe, Joshua Olalekan Ogunwole, ya bayyana ɗan takarar jam’iyyar Accord, Ademola Adeleke, a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Osun, bayan ya samu ƙuri’u 511,067.
Ya doke ɗan takarar jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, wanda ya samu ƙuri’u 444,815, yayin da ɗan takarar ADC, Najeem Salaan, ya samu ƙuri’u 17,180.

16/08/2026

Yadda Gwamnonin jam'iyyar APC s**a fice daga jihar Osun bayan sun ga rashin nasara a zaben jihar da ya gabata.

INEC Ta Kammala Sanar da Sakamakon Kananun Hukumomi 30 Na Zaɓen Gwamnan jihar Osun, Jam'iyyar Accord ce kan gabaHukumar ...
16/08/2026

INEC Ta Kammala Sanar da Sakamakon Kananun Hukumomi 30 Na Zaɓen Gwamnan jihar Osun, Jam'iyyar Accord ce kan gaba

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta kammala bayyana Sakamakon zaɓen gwamnan Jihar Osun na 2026 daga ƙananan hukumomi 30, inda jam’iyyar Accord ta samu gagarumar nasara a kan APC.

Jimillar kuri’u:

— Accord: 511,067
— APC: 444,815
— ADC: 17,180

Hakan ya sa Accord ke gaban APC da tazarar kuri’u 66,252.

15/08/2026

“Ban taɓa aure don in rabu da mace ba” – Jarumi Adam A Zango bayan an ɗaura, sabon Aurensa a jiya Juma'a.

📷: Kinguzee Uzee

SABON AURE: Adam A. Zango Ya Nemi Addu’ar MasoyaDA DUMI-DUMI: Jarumin fina-finan Hausa, Adam A. Zango, ya sake yin sabon...
15/08/2026

SABON AURE: Adam A. Zango Ya Nemi Addu’ar Masoya

DA DUMI-DUMI: Jarumin fina-finan Hausa, Adam A. Zango, ya sake yin sabon aure a ranar Juma’a, 14 ga Agusta 2026, bayan rabuwar sa da tsohuwar matar sa.

Jarumin ya bayyana cewa bai taba yin aure da niyyar ya rabu da mace ba, yana mai cewa abin da ya faru a baya ƙaddara ce.

A cikin sakonsa ga masoya, Adam A. Zango ya nemi addu’a, inda ya ce yana fatan sabon aurensa ya kasance mai albarka da zaman lafiya.

Ya kuma yi tsokaci kan masu s**ar aurensa, yana mai cewa wasu za su iya cewa: “Kwana nawa ne shi ma zai sake ta?”

Muna roƙon Allah Ya sanya albarka a sabon auren, Ya ba su zaman lafiya, fahimtar juna da tsawon rai, kuma Ya sa alheri ya kasance a tsakaninsu.

Address

Garko
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Garko Reporter's TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Garko Reporter's TV:

Shortcuts

Share