Kukan kurciya jawabine mai hankali yakeganewa

  • Home
  • Kukan kurciya jawabine mai hankali yakeganewa

Kukan kurciya jawabine mai hankali yakeganewa Nabude wannan group domin tataunawa akan abunda yashigema duhu

30/04/2024

𝐀𝐋𝐀𝐌𝐎𝐌𝐈 5 𝐃𝐀 𝐙𝐀𝐊𝐀 𝐆𝐔𝐉𝐈 𝐒𝐎𝐘𝐀𝐘𝐘𝐀 𝐃𝐀 𝐌𝐀𝐂𝐄 𝐌𝐀𝐈 𝐒𝐔..

Wa dan nan Wasu Alamomi Ne Da Ya Kamata Ace Ka Kula Dasu Yayin Da Kake Cikin Soyayya, Domin Tabbas Zasu Taimake Ka Wajen Gina Soyayar ka Cikn Farin Ciki Da Kuma Samun Macen Data Dace Da Rayuwarka...

1. Kada Ka So Macen Da Ke Yawan Tambayarka Kudi, 💰 Ko Wasu Kayan Kyale Kyale Na Rayuwa.Domin Wannan Macen Kasuwanci Take Dakai Tana Kwasan Riba Ba Soyayya da kai.

2.Ka Kiyaye Soyayya Da Mace Mai Girman Kai Ko Nuna Isa, Gami Da Jiji Da Kai Domin Mace Mai Wannan Dabi'ah, Koda Ka Aureta Ba Zata Taba Bin Umurnin ka Ko Sarrafuwa Agareka Ba 🙅‍♂️🙅‍♂️

3-Ka Guji Soyayya Da Mace Dake Katange Ka Daga Abokanka, Ko Nesan Taka Da Ahalinka, Domin Duk Macen Dake Maka Haka War Gaje Maka Rayuwa Zatayi.

4-Kayi Nesa Da Mace Mai Karyata Ka Ko Yawan Jayayyah Dakai Domin Wannan Macen Bazata Taba Girmamaka Ba, Kana Kuma Zatayi Kokarin Kauda Duk Wani Farin Ciki Dake Tare Dakai ba🙅‍♂️🙅‍♂️

5-Ka Kiyaye Soyaya Da Macen Dake Kewaye Da Maza Wadda Take Kiransu Da Abokan Ta🤔🤔 Domin Wadannan Mazaje Zasu Maye Gurbinka Agareta Sanan Kuma Tsakaninka Da Ita Babu Sirri Duk Wani Abu Inka Gaya Mata Koya Faru A Tsakninku, To Kadauka Kaman Kayi Magana ne A Kunnen Su

NOTE::- Matukar Zaka Kiyaye Wannan Tabbas Zaka Samu Abokiyar Zama Wadda Zaku Zauna Cike Da Farin Ciki Kana Kuma Da Fahimtar Juna Matukar Kasamu Macen Da Bata Da Dabi'ah Daya Daga Cikin Wadanna To Tabbas Dan Uwa Kayi Dace Kayi Kokarin Riketa Hannun Bibbiyu 🙏🙏

SHAWARI NE KYAUTA.

Ga Abin Da Manzon Allah (S.A.W) Ya Fada.Sahabin Manzon Allah S.A.W Jabir ya rawaito  Manzon Allah S.A.W idan zai yi hudu...
13/09/2023

Ga Abin Da Manzon Allah (S.A.W) Ya Fada.

Sahabin Manzon Allah S.A.W Jabir ya rawaito Manzon Allah S.A.W idan zai yi huduba yana cewa : "Hakika mafi alherin zance shi ne maganar Allah. Mafificiyar shiriya ita ce shiriyar [Annabi] Muhammad. Mafi Sharrin al'amura su ne wadanda aka kirkiro [Bidi'o'i] kuma dukkan abin da aka kirkiro bata ne". Imam Muslim ne ya rawaito wannan hadisi.

Don haka babu wani abin da za a kirkiro a addini ya fi na Manzon Allah S.A.W, duk kuwa yadda mai shi yake ganin kyansa.

Dan uwa rike abin da Manzon Allah S.A.W ya zo da shi, ba za ka yi nadama ba ranar alkiyama.
© Dr.Rabiu Umar Rijiyar lemo

TAYA MUKE BARI ZUCIYAR MU TA LALACE? --"Lalacewar zuciyar mutum yana samo asali ne daga abubuwa shida"-1. Wasu Mutane su...
15/08/2023

TAYA MUKE BARI ZUCIYAR MU TA LALACE?
-
-
"Lalacewar zuciyar mutum yana samo asali ne daga abubuwa shida"
-
1. Wasu Mutane suna aikata zunubi ne da niyyar cewa wai zasu tuba nan gaba.
2. Suna neman ilimi amma basa yin aiki da ilmin nasu.
3. Idan kuma zasuyi aiki, basa yinsa da cikakken ikhlasi.
4. Suna cin arziƙin Allah amma sunƙi nuna godiyarsu ga Allah.
5. Basa yarda da abinda Allah ya basu, (saboda leke-leke).
6. Suna binne Mamatansu amma kuma basa wa'azantuwa daga hakan.
✍️✍️✍️✍️ Kukan kurciya.....

03/08/2023

YADDA AKE NEMAN IZININ SOYAYYA GA
MACE!!
Ana neman Izinin soyayya ne a gurin budurwa yayin da mutum
zai yi amfani da wasu 'yan kalamai na shiga zuciya
da kuma yabo
da kodawa.
Misali; "Nayi farin ciki da har ki ka bani damar
ziyartarki har gidanku. Hakika tun lokacin da muka hadu na ji sonki ya
shiga cikin
zuciyata, wannan shi ne dalilin ma da yasa na
bukaci ki bani izini in
same ki har gida domin mu tattauna.
Bayan rabuwarmu dake, na fuskanci ke yarinya ce mai
kyakkyawar halayya da kuma tarbiya mai kyau.
Kina da ilimi da hankali da kuma tunani, sannan kin
iya mutunta
surar jikinki wajen kyautata sa sutura da natsuwa
wajen magana. Wadannan sune abubuwan da s**a fi jan
hankalina, har na ji ina
kwadayin mu kulla soyayya tsakanina da ke, sai
dai kuma ina ta
wasi-wasi a cikin zuciyata, shin ko zan samu shiga
a gurbin zuciyarki? To amma idan na tuna ke wayayyiya ce
mai ilmi, na addini da
kuma na zamani, sai in daina wancan tunanin da
nake.
Da fatan kin fahimci abin da nake magana akai,
kuma za ki karbe ni a matsayin masoyinki mai kaunarki."
IDAN KA SAMU SHIGA ZAKA JI AMSA KAMAR HAKA;
"Na yi farin ciki da zuwanka, na kuma gode da
yabawar da kayi min, Na yarda da kai a matsayin
masoyina, kuma na amince da
soyayyarka. Da fatan ba za ka yi min halin yan maza ma'abota
yaudara ba? Zan kuma soka a zuciyata kamar
yadda ka tabbatar
min da Soyayyata a cikin taka zuciyar.
Allah ya tabbatar mana da alkhairi."
Wannan shi ne amsa mafi kwantar da rai da budurwa zata ba saurayi, yayin da ya furta mata
abin da ke zuciyarshi ko da kuwa
a cikin wasika ne.
To idan kuma aka samu akasin hakan, zai yi wuya
soyayya ta
kullu a wannan wurin. Don haka ya kamata samari da yanmata ma'abota
soyayya su
lura da wannan. MENE NE SHAUKIN SO?
Yadda bege yake, to kusan haka shima shauki
yake, sai dai kuma
ba daya suke ba, kowanne yana da nasa tsarin. Shi shauki, shi ne mutum ya dinga jin wani irin farin
ciki da
annashuwa, da wani yanayi mai faranta rai a duk
lokacin da yaga,
ko ya ji muryar masoyinsa.
Kukan kurciya.....

02/08/2023

Dan Allah a yafeni idan akazo da zancen gaskiya babu maganar kunya Koh boye boye_ Mata ya kamata kusan wanann………

A man do not fall in love through s*x.

Namiji zai iya kwanciya da mata dari, babu daya daga ciki da yake so.

Akwai wacca ba abinda ya tab'a shiga tsakanin su Amma Wlh zai iya mutuwa akanta.

Da yawa matan mu basu iya soyayya ba, idan ka cire gangar jikin su ba bu wata gudunmawa da suke bayarwa a relationship. Shima yawancinsu mazanne ke sarrafasu.

Banda bani-bani ba abinda s**a iya na nazartar abokin rayuwar su.

-Baku iya kiran namiji kuyi masa addu’ar samun nasara ba a rayuwa.

-Baku iya yiwa namiji nasiha akan abinda yake aikatawa akan kuskure ba.

-Babu tausayawa ko taimakawa wajen cimma burinsa na rayuwar ku a nan gaba.

Na rantse da Allah duk bakar zuciyar namiji, Indai zaki tausayawa masa saboda Allah, sai zuciyarsa ta tausasa agare ki.

Zai ringa jin tausayin ki, yadda k**e kula dashi sai ya linka miki fiye da abinda k**e masa.

A yanzu samari wacca zata taimaka musu a rayuwan su suke bukata, ba wacca zata sadaukar da jikinta agare shi ba.

Yana da kyau ku nazarci mutum kafin kubawa wani amanar zuciyar ku.

Kukan kurciya jawabine.

01/08/2023

HUKUNCIN TSOTSA AL'AURA DA BAKI (ORAL S*X)
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Assalamu Alaikum. Allah ya qarawa malam lafiya ameen. Malam, Allah yana cewa a cikin Alqu'ani mai girma:
نِسَاۤؤُكُمۡ حَرۡثࣱ لَّكُمۡ فَأۡتُوا۟ حَرۡثَكُمۡ أَنَّىٰ شِئۡتُمۡۖ
(Mãtanku gõnaki ne a gare ku,bsabõda haka ku je wa gõnakinku yadda kuka so)

Tunda hakane, toh malam meye hukuncin Oral s*x? Saduwar da ake yi ta baki? Malam wannan ya halatta tsakanin ma'aurata?
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Eh haka ne. Allah ya fada haka. Amma ba wai ayar tana nufi cewar kuyi jima'I dasu ta kowacce Qofa bane.

A'a ayar tana nufin "KUYI JIMA'I DASU AKWANCE, KO AZAUNE, KO ATSAYE, KO DURKUSHE, KO TA-GABA, KO TA-BAYA".

Wannan shi ake nufin "أَنَّىٰ شِئۡتُمۡۖ" ɗin.

Dangane da KOFAR SADUWAR kuwa, idan ka koma ayar da take kafin wannan wacce ka kawo, ai zakaga wajen da Allah yake cewa:..فَأْتُوهُنَّ مِنْ حَيْثُ أَمَرَكُمُ اللَّهُ ۚ ...
Wato: "Kuzo musu (ku sadu dasu) ta wajen da Allah ya umurceku".

To idan kayi nazari, ai zaka ga cewar FARJINSU shine wajen da Allah yayi umurni ɗin. Ba wai dubura ba, ba kuma baki ba.

Da akace MATAYENKU GONAKINKU NE, ai farjinsu shine gonar. Maniyyin mazajensu kuma shine abin shukawar (seeds) kenan.
Don haka idan kazo da seeds ɗinka, awanne waje ya kamata ka shuka?
ABAKI??- a'a shi baki anyishi ne domin zikiri da karatun Alqur'ani da salatin Annabi ﷺ dakuma cin abinci, da furuci.

Don haka bai kamata wajen ambaton Allah kuma ya koma ya zama wajen yin Jima'I ba.

Acikin littafin FATAWAL HINDIYYAH juzu'I na 5 shafi na 372, marubucin yana cewa: Malamai sun kasu gida 2 akan mas'alar ta kowacce fuska.

Idan sumbartar al'aurar juna kawai kake nufi, ba tare da fitar Maziyyi ko Maniyyi ba, to wasu Malaman sunce ya halatta. Amma mafiya yawan Malamai sunce MAKRUHI NE.
(Aduba Tafsirin Qurtubee juzu'I na 12 shafi na 231 da kuma AL-INSAF juzu'I na 8 shafi na 33)

Amma idan kana nufin tsotsa sosai harda fitar maniyyi da maziyyi, to wannan Mafiya yawan Malamai sun tafi akan rashin halaccin yinsa. Saboda wadancan d

01/05/2023

SALAM YAN UWA DA ABOKAN ARZIKA DA FATAN ANYI SALLAH LPY
Kwana 2 shiru.
Mun dawo bakin aiki. Allah yasa mudace

26/12/2022

Manzo Allah saw Yana cewa ku tsayar da duk abinda kuke lokacin da ake Kiran sallah Koda kuwa karatun alqurani Mai girma ne domin saboda duk mutumin da yake zance ko magana alokacin Kiran sallah to bazai Sami damar furta kalmar shahada ba alokacin mutuwarsa Allah kasa mudace.
KUKAN KURCIYA....

25/12/2022

MUTANE IRI HUDU(4) NE A DUNIYA.

1) wani yanada rabo aduniya amma bayada rabo a Lahira.

2)wani yanada rabo a Lahira amma bayada rabo a Duniya.

3)wani yanada rabo a Duniya kuma yanada rabo a Lahira.

4) wani bayada rabo Aduniya kuma bayada rabo a lahira.

Ya ubangiji kasa munada rabo a Duniya da kuma Lahira.🙏🙏🙏

Akwai Wata Addu'a Da Manzon Allah Yayi Mai Zafi Game Da Shugabanni, Inji Marigayi Sheikh Ja'afarYa ɗaga hannu a ɗakin Mu...
23/12/2022

Akwai Wata Addu'a Da Manzon Allah Yayi Mai Zafi Game Da Shugabanni, Inji Marigayi Sheikh Ja'afar

Ya ɗaga hannu a ɗakin Mumina A'isha Ya ce;

"Ya Ubangiji duk wanda ya jiɓinci lamarin al'ummata, ya shugabance su, in yayi musu sauƙi sunji daɗin gudanar da mulkinsa bai zaluncesu ba, ya Ubangiji ka sauƙaƙa masa! Ka sauƙaƙa masa!! Ka sauƙaƙa masa!!!"

Sannan kuma ya ce;

"Ya Ubangiji duk wanda ya shugabanci al'ummata, kuma ya jefa su cikin ƙunci, cikin halin ƙaƙa-nikayi, ya Ubangiji ka ƙuntata masa! Ka ƙuntata masa!! Ka ƙuntata masa!!!"

Duk mai ƙaunar Annabi S.A.W ya amsa da AMEEN.

Address


Telephone

+2348165519997

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kukan kurciya jawabine mai hankali yakeganewa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share