KABO Online News

KABO Online News Hausa blog

05/08/2023

Gabacin Sakkwato Na Cikin Mummunar Ukuba Wallahi😭

Anhana Su Noma.
Anhana Su Kasuwanci. Subhanallahi😭

30/07/2023

Kina Durƙusawa Har Ƙass🧎🏾‍♀️ki Gaishe da SAURAYINKI, ko kuwah kemah BARRISTER 👩🏾‍⚖️ ceh Uwar Ƴan Sanin Right🙄😎

07/04/2023

Yaa ALLAH Ka Rintse Idanuwanmu Daga Ganin Aibun Wasu Muga Namu Don Mu Tuba Kuma Mu Gyara.

10/02/2023

KACICI-KACICI: Wane gari ne babban birnin Nigeria 🇳🇬 na farko kafin Abuja ?

Da yawa basu sani ba...

Ya mutu a hatsarin mota kuma dan garin Bichi ne, a taimaka da sharing har makusantansa su gani; yana asibitin Murta. All...
27/12/2022

Ya mutu a hatsarin mota kuma dan garin Bichi ne, a taimaka da sharing har makusantansa su gani; yana asibitin Murta. Allah yaji kansa.

Daga Naynah Salees

KAR KU ZAƁI NNPP - Cewar Kwamishinan yaɗa labaran Kano Malam Muhammad Garba a shafinsa na Facebook.Me zaku ce?
27/12/2022

KAR KU ZAƁI NNPP - Cewar Kwamishinan yaɗa labaran Kano Malam Muhammad Garba a shafinsa na Facebook.

Me zaku ce?

27/12/2022

Maganar da ake yadawa cewar an sace wayar Sen Rabiu Musa Kwankwaso awajen taro ba gaskiya bane.

Na bada kyautar motata idan ka kawo Sunan Dan Talaka Mai Degree a Garin Ganduje mahaifar GwamnaInji Auwal Galadima Jemom...
18/12/2022

Na bada kyautar motata idan ka kawo Sunan Dan Talaka Mai Degree a Garin Ganduje mahaifar Gwamna

Inji Auwal Galadima Jemomi

AN GAMU...Shugabannin jam'iyar APC na karamar hukumar Doguwa dake jihar Kano sun yi tattaki harzuwa Abuja domin bawa Alh...
06/11/2022

AN GAMU...

Shugabannin jam'iyar APC na karamar hukumar Doguwa dake jihar Kano sun yi tattaki harzuwa Abuja domin bawa Alhassan Ado doguwa Hakuri da cewa yayi hakuri ya zauna a jam'iyar ta APC.

Sai anyi rashin sa'a domin kuwa Doguwa Ya tarbi shugabannin jam'iyar da kayan marmari Mai alamar jam'iyar NNPP ta Kwankwaso.

Me hakan ke nufi...

DA ƊUMI-ƊUMI: CBN zai sauya launin takardar kuɗi a DisambaA yau Laraba ne babban bankin Najeriya CBN,  ya sanar da cewa ...
26/10/2022

DA ƊUMI-ƊUMI: CBN zai sauya launin takardar kuɗi a Disamba

A yau Laraba ne babban bankin Najeriya CBN, ya sanar da cewa za a kaddamar da sabbin takardun kudi da a ka sauya musu launi a ranar 15 ga Disamba, 2022.

A cewar Godwin Emefiele, gwamnan bankin, wanda ya bayyana hakan, sabbin kudaden da za a sauya wa launi sun hada da takardar N1,000, N500 da N200.

23/10/2022

Akwai labarai masu zafi

Gwamnati Tayi Waje road Mawaki Daúda Kahutú Rarara daga kwamitin yaƙín neman zaɓèn Bóla Tìnúbú. Inda ta maye gurbin sa D...
22/10/2022

Gwamnati Tayi Waje road Mawaki Daúda Kahutú Rarara daga kwamitin yaƙín neman zaɓèn Bóla Tìnúbú.
Inda ta maye gurbin sa Da Abdul Amat maikwashewa.

-Mé za kúce ?

"Mijina Ya Daina Cin Abincin Da Na Girka Tun Bayan Da Naihu, Saboda Yana Kyama Ta"Daga Aliyu Adamu Tsiga Ya yi ƙorafin c...
07/09/2022

"Mijina Ya Daina Cin Abincin Da Na Girka Tun Bayan Da Naihu, Saboda Yana Kyama Ta"

Daga Aliyu Adamu Tsiga

Ya yi ƙorafin cewa ba zan iya haɗa abincinsa ba saboda ya yi iƙirarin ina yin abubuwa marasa kyau da ƙazanta kamar tsafta da kuma jaririn yana yawan yin fitsari, da tumbuɗi kuma ina yin amfani da bakina wajen cirema jaririn majinar da ke cikin hancin shi, kuma a dalilin haka ne yake so mu sami ƴar aikin gida.

Tun daga wannan lokacin, kusan watanni 2 kenan baya cin duk wani abu wanda ni ce nayi tunda daga abinci ko wani abun sha.

Don Allah ku bani shawara domin ban san taya zan ɓullo wa lamarin ba.

'Yan Fim Suna Kokarin Ganin Bayana, Don Sun Maka Ni A Kotu, Saboda Na Ce Suna Bata Tarbiyya, Cewar Dan Jarida Indabawa A...
05/09/2022

'Yan Fim Suna Kokarin Ganin Bayana, Don Sun Maka Ni A Kotu, Saboda Na Ce Suna Bata Tarbiyya, Cewar Dan Jarida Indabawa Aliyu Imam

A daren jiya aka yi sallama da ni bayan na fito ne sai mutumin ya ce daga Kotu ne aka aiko shi waje na da sammaci. Ya ba ni wasu takardu cewa wai wani Mutum mai suna Hamisu Lamido Iyantama ne ya yi kara ta, saboda na yi rubutu kan 'yan fim na ce suna lalata tarbiyya, kuma Iyantama dan fim din ne, sannan na yi rubutu na nuna rashin jin dadina sanda wani Sanata mai suna Barau Jibril ya raba wa 'yan fim motoci, babura, kyamarori, kwamfuyutoci da kudade alhalin mabukata suna mutuwa a asibiti saboda rashin kudin magani, wasu na mutuwa saboda yunwa. Sannan ina goyon bayan Gwamna Ganduje ina adawa da Barau Jibril sanda shi Barau din ke takun saka da Baba Ganduje a kungiyarsu ta G7 Wannan shi ne kadai laifina.

Bin tafarkin Annabi (SAW) na umarni da kyakkyawa da hani da mummuna da yaki da rashin tarbiya ya zama laifin da har ake kokarin a ga bayan mai aikata shi.

Zan bibiyi takardar sammaci insha Allahu, tana da yawa sosai. Zan san matakin da ya dace na dauka.

Allah ya shiga lamuranmu.

05/09/2022

Wait for it........

30/05/2022

Ku kasance damu akoda yaushe

12/05/2022

Kabo online news

20/04/2022

Aslm Yan uwa musulmi Barka da azumi

KUNGIYAR WAR AGAINST INJUSTICE TA BUKACI ALKALIN  ALKALAN KANO MAI SHARI'A  HON. JUSTICE NURA SAGIR UMAR DA YA DAKATAR D...
30/03/2022

KUNGIYAR WAR AGAINST INJUSTICE TA BUKACI ALKALIN ALKALAN KANO MAI SHARI'A HON. JUSTICE NURA SAGIR UMAR DA YA DAKATAR DA MAI SHARI'A AMINU GABARI DA KUMA BINCIKARSA SAKAMAKON ZARGE-ZARGEN DA AKE MASA NA CIN HANCI DA RASHAWA DA KUMA SON KAI NA WADANDA YAKEWA SHARI'A.

Wannan yana cikin wata takardar bukatar yin haka mai dauke da sahannun babban direktan kungiyar Amb. Comr. Umar Ibrahim Umar.

Takardar tace muna kira a gare ka amatsayin ka na alkalin alkalan Kano wanda kai kadai doka tabawa damar ladaftar da duk wani jami'in kotuna da suke jihar Kano amatsayinka na shugaban hukumar da'ar ma'aikatan shari'a ta jihar Kano da ka bincike mai shari'a Aminu Gabari na Kotun majistiret mai lamba 58 dake nomansland a jihar Kano, duba da irin zarge da akeyi masa na karbar cin hanci da kuma duk case din da ya hada da gwamna Ganduje ko kuma makusanta ko yan jam'iyyar APC kotunsa ake turawa, kuma da an tura yake kai mutum kurku da sauran nuna banbance da kuma zargin karbar cin hanci ga makaraya da s**aje gabansa, wanda wannan ya sabawa aikin alkali da dokokin kasar nan.

Amatsayin mu, na masu kare hakkin Dan Adam da bibiya a kan shugabanci nagari gami da yaki da rashin adalci yasaka muke bukatar a dakatar dashi da gudanar da aikinsa da kuma bincikar wadannan zarge-zarge da ake masa.

Wannan abin takaici ne, a zargi alkali da wannan munanan zargen.

A don haka kungiyar take bukatar ayi abinda yakamata kafinta dau mataki na gaba a Kai.

Khalifa Muhammadu Sunusi II. Baida Alaka Labarin Da Ake Yadawa A Yanar Gizo mai Taken (2023 Bola Tinubu and the Cost of ...
23/03/2022

Khalifa Muhammadu Sunusi II. Baida Alaka Labarin Da Ake Yadawa A Yanar Gizo mai Taken (2023 Bola Tinubu and the Cost of Political Misculculation) ~ Dan Buran Kano

Daga Comrade Umar Saleh Zara

Munir Sanusi, Danburam Kano kuma shugaban ma'aikatan fadar mai martaba, Khalifa Muhammad Sanusi II, CON sarkin Kano na 14,
ya karyata labarin da ake yadawa dacewa Sarkin Kano na 14 ne ya rubuta akan Bola Tinubu

Inda ya baiyyana cewa "Muna so mu bayyanawa alumma karara cewa labarin da ke yadawa a kafafen yada labarai na zamani mai suna "2023: Bola Tinubu and the cost of political misculculation" ba mai martaba, Khalifa Muhammad Sanusi II. ne ya rubuta ba kuma baida alaka da lamarin, kamar yadda ake ta yadawa.

Dan Buran yaci gaba da cewa Wannan labarin ya shafe watanni yana yawo a groups na WhatsApp, wanda wani mai suna Sanusi Muhammad ne ya rubuta shi, wanda bashi da alaka da mai martaba, Muhammad Sunusi II.

ya kara da cewa Abin takaici, yawancin mutane sun yi kuskuren gane sunan marubucin a matsayin Mai Martaba. Don haka, idan aka yi la’akari da bukatuwar daidaita bayanan, muna bayyanawa ga wadanda ba su san cewa ba a taba kiran Halifa da Sanusi Muhammad ba, sai dai a ce HH Muhammad Sanusi II.

Har ila yau, muna amfani da wannan damar don ƙarfafa masu karatu su bincika bayanan da s**a samu ta hanyar yanar gizo don gano bayanan karya da yaudara da ake zargin sun fito ne daga manyan mutane da masu tunani. A yayin da muka sake bayyana cewa ba mu da wata alaka da marubuci da ita kanta labarin ta kowace hanya, muna ci gaba da yin imani da dogaro ga Allah (Subhanahu Wa Ta’ala) ya ci gaba da shiryar da Mai Martaba a matsayinsa na dattijo a cikin zamantakewarsa. Tallafin tattalin arziki ga dukkan 'yan Najeriya, 'yan Afirka da kuma bil'adama baki daya".

Daga Umar Zara Comrade

Tunatarwae hausa hazaka
22/03/2022

Tunatarwae hausa hazaka

PROFESSOR YEMI OSINBANJO: BABBAN KALUBALE GA MUSULMIN NIGERIADAGA Datti AssalafiyMataimakin Shugaban Kasarmu Nigeria Pro...
22/03/2022

PROFESSOR YEMI OSINBANJO: BABBAN KALUBALE GA MUSULMIN NIGERIA

DAGA Datti Assalafiy

Mataimakin Shugaban Kasarmu Nigeria Professor Yemi Osibanjo Malamin addinin nasara ne, ya kai matsayin Bishop, babban jigo ne a cikin majalisar kungiyar mabiya addininsu na duniya ba wai a Nigeria kadai ba.

Ba shakka Professor Yemi Osibanjo yana da tsananin kishin addininsa, kuma baya wasa akan kishin addininsa, idan kuna bibiyar kafofinsa na sada zumunta zaku shaida hakan, a cikin program da yake watsawa a shafinsa na Facebook duk karshen sati sai an nunoshi a dakin bautarsu yana wa'azi, samun matsayin da yayi a Gwamnati bai hanashi watsi da kuma kyamar addininsa ba.

Kamar yadda Malam Adam Baba ya fada ne, shi dai Pastor Yemi Osinbanjo tunda ya zama mataimakin Shugaban kasa, addinin sa ne a gaban sa, kullun lalube ya ke don samun salun habbaka akidar sa ta RCCG da addininsu na nasara ba tsoro ba kunya, wannan aka rasa a tare da Musulmai.

Idan Osinbanjo ya zama Shugaban Kasar Nigeria, sai ya tabbatar da addininsu na nasara ya samu ginda zama cikin salon mulkin Nigeria, in kana ja, ka je ka yi binciken yaya ya raba kudin TraderMoney, ta yaya ya kasance akwai layin waya na (Airtel RCCG line) wanda a fakaice Kristoci kawai aka sayar wa layin?, me yasa ba Musulmai a cikin ayarin sa duk da shi Vice-President ne?

Abokan zaman mu wadanda ba Musulmai ba basa wasa da addininsu, kuma basa shakkar bayyana addininsu, idan sun samu dama a Gwamnati kokari suke su kawo 'yan uwansu masu kaifin kishin addini su dasa su, wannan aka rasa a tare da 'yan uwa Musulmai.

Kuma kamar yadda Professor Farooq yayi bayani a cikin dalilansa na hudu yace: Osinbajo mutun ne mai fara'a amma mai guba, mai kiyayyar Islama wanda yake tufatar da son zuciya da baka, Yana cudanya da musulmi ne kawai saboda manufarsa ta siyasa. Shiyasa fa a kaf cikin masu tsaron lafiyarsa babu Musulmi ko guda daya, duk wani sensitive guri dake ofishinsa babu Musulmi.

Abokan zaman mu wadanda ba Musulmai ba basu taba yadda su fif

Shekaru 7 cikin jiran tsammani...Yau fiye da shekaru 7 Kenan muna uziri cikin jiran tsammanin warabbuka,na Samun kyautat...
20/03/2022

Shekaru 7 cikin jiran tsammani...
Yau fiye da shekaru 7 Kenan muna uziri cikin jiran tsammanin warabbuka,na Samun kyautatuwar lamura a Nigeria.
Kafin zuwan me Gaskiya, zaton mu shine komai zai daidaita,tun daga farashin Mai da cin hanci da rashawa da matsalar wutar lantarki da sauran matsalolin dake addabar talaka musamman ma uwa uba matsalar tsaro,a zaton mu idan ya karbi sitiyari komai yazo karshe amma abin mamaki har ya fara tattara kayansa babu abin da ya sauya,sai ma tabarbarewar lamura.

Wallahi kafin ya hau idan nayi mafarki cewar zai shekara 7 talaka bai GA sauyi ba,zance mafarkin shaidan ne,amma sai gashi muna gani a zahiri.Allah mun tuba da muka dora wilaya GA waninka,Allah Ka karbi tuban mu.

Ni dai a ra'ayi na,matsayi na na Dan Nigeria Mai hakki,idan Zan bayar da maki a cikin wadannan shekaru 7 da akayi,sai nace na bayar da maki 6 cikin dari,shima Dan kar ace ina da kwauron maki ne.

Ina la'akari da irin dadin bakin da aka yi mana lokacin yakin neman Zabe,cewar wuta zata samu kaKaraka,man fetur ma za'a rage kudin sa,matsalar tsaro zata zama tarihi,talaka zai sha jar miya blablabla,amma wallahi babu fus duk alkawarin da akayi an mance dashi an kara tura mutane cikin masifar da tafi ta Baya.
Mai daukar albashin dubu 100 idan har ba cuwa cuwa zai yi ba,ko kuma Yana da wata sana'ar Mai kawo masa income ,Bai isa ya mallaki gida ba,idan ma yayi sa'a su ishe shi cefane, domin shinkafar da yake saya buhu naira dubu 8 a zamanin marasa gaskiya yanzu a zamanin me gaskiya ta Zama naira dubu 25, taliyar dubu 1500 yanzu dubu 4500,jarkar mai naira dubu 6 yanzu naira dubu 30. Ina gaskiyar?

Mun gaji da gafara sa alhalin bamu ga kaho ba,.an sha mu basulla an mana dadin baki an kaimu an baro mu.Allah ya kiyaye gaba.nadama dai mun yi ta,kuma ni a ganina mun tafka asara munyo zaben tumun dare.Allah mun tuba Allah Ka kawo mana chanji na gaskiya ba irin chanjin cigaban me hakar rijiya ba.
Na mance Ashe fa dala ma an yi alkawarin Zata daidaita da naira.ko nawace dalar yanzu?

Shekaunsa goma sha takwas  an daura aurensa yau bayan sallar juma'a a garin tilden fulani dake jahar bauchiDaga comr abb...
18/03/2022

Shekaunsa goma sha takwas an daura aurensa yau bayan sallar juma'a a garin tilden fulani dake jahar bauchi

Daga comr abba sani pantami

kotu a kano ta sake bada umarnin a kamo muazu magaji (ɗan sarauniya) bisa kin halartar zaman kotu har karo biyu
14/03/2022

kotu a kano ta sake bada umarnin a kamo muazu magaji (ɗan sarauniya) bisa kin halartar zaman kotu har karo biyu

yadda minister isa ali pantami ya ɗana motar da aka ƙera a nigeria mai amfani da lantarki , jelani aliyu ne shugaban huk...
07/03/2022

yadda minister isa ali pantami ya ɗana motar da aka ƙera a nigeria mai amfani da lantarki , jelani aliyu ne shugaban hukumar NDCCD

Daga Comr Mustapha Safyan Abdullahi

YANZU YANZU :Kwankwaso yana shirin ficewa daga PDP zuwa NNPPTsohon gwamnan engr rabiu kwankwaso yana shirin ficewa daga ...
01/03/2022

YANZU YANZU :Kwankwaso yana shirin ficewa daga PDP zuwa NNPP

Tsohon gwamnan engr rabiu kwankwaso yana shirin ficewa daga babbar jam'iyya adawa ta PDP zuwa wata sabuwar jam'iyya mai suna NNPP.

01/03/2022

Zanyi gwamnan Kano nayi aiki kamar kwankwaso ,, shaa'aban Ibrahim sharada"

21/02/2022

Kungiyar daliban nigeria tabawa ASUU da gwamnati mako Daya akan susasanta kansu

  Chairman na local government shine babban mutum na farko da ya dace ace yasan matsalonin da Al ummar da yake mulka ama...
20/02/2022



Chairman na local government shine babban mutum na farko da ya dace ace yasan matsalonin da Al ummar da yake mulka amatsayinsa na shugaban karamar hukuma domin ance Mai daki shiyasan inda yake masa zuba duba da yanayin da abubuwa suke faruwa ..

Amma Kash nidai banyi saar wannan kujera ta chairman ba domin shekara ta biyar yake da Hawa akan kujera Amma ba lailai bane ya iya nuna Wani muhimmin aiki wanda Al umma suke amfanuwa dashi , zan iya cewa wallahi ko Yan barandar siyasa basa samu daga gurinshi b***e wasu Al umma ,, Koda yake ba wannan ake bukata ba

Amma yanzu ahaka ake cewa za abawa kananan hukumomi yanci a Ina ta wanne guri wallahi Basu samu wannan cancanta ba domin yar yanzu Banga Wani Abu dasukeyiwa ba ,,
Abun bakin cikin ma saikaje LOCAL government secteria zaka hirme da rashin chanchanta ta bangaren myatanen da suke aiki a wannan guri zakasamu mutum Bai iya karatun hausa ba b***e turanci amma shine yake da office
Domin Wani ko secondary bayyi ba am zakaga Yana takama akan wai shi ma aikaicin gwamnati

Nasan a Kabo L. G. A akwai matasa Wanda zuka cancanta a kowanne bangaren na fannin ilmi Amma sai kaga mutum ya buge da post na Wani katon mayaudari a social media yaan wai azabeshi sabida shirme shida yakamata ace Yana school kowani ministry , ki wata hukuma dai ko Kuma Yana business

*****

Ya Mai girma chairman a gaskiya ka sauya Shirin tafiyarka domin gobenka tayi kyau duba da yanin yanza zamanin ya sauya
Ya kamata ace A kabo local government munada wadanan abubuwa ko Ian akwai mutum kamar Sha biyar
1. Sojoji
2.lauyoyi
3.civil defence
4.lecture
5.professor
6. Manyan likitoci
7.Dr PhD

Manyan jamian gwamnati

Amma. Kash 😭😭😭

Gamu da manyan Yan siyasa
Har bila adadin
Gamu da manyan Yan kasuwa
Gamu da manyan dalibai
Gamuda manyan Yan Sara s**a😂😂

Zamuci gaba
✍️✍️✍️✍️
Comr Comr Mustapha

,                  *ZUMUNCI*Wani halattaccen mu'amala ce daya samo asali tun halittun farko.Yana da mahimmanci da alkhai...
18/02/2022

, *ZUMUNCI*

Wani halattaccen mu'amala ce daya samo asali tun halittun farko.
Yana da mahimmanci da alkhairi a cikin sa. Saboda mahimmancin sa Allah SWT Yace "Ya yanke Rahamar sa ga duk wanda ya yanke zumunci".

*SU* *WAYE* *KE* *ZUMUNCI* ?
Ana zumunci da dan'uwa na jini, da Makwabci, da duk musulmi, kamar fadar Manzo SAW "musulmi dan'uwan musulmi ne".

Ana hada zumunci a auratayya da zama na wurin kasuwanci da karatu. Akwai hanyoyi da dama na zamantakewa da ake hada zumunci.

*YAYA* *AKE* *ZUMUNCI* ?

Ana yin zumunci domin *ALLAH* *SWT.*
Ana taimakon Juna.
Ana Rufawa Juna asiri.
Ana Tausayawa Juna.
Ana Kyautatawa Juna
Ana Auratayya wa Juna
Ana Ilimantar da Juna.
Ana Ziyartar Juna.
Ana yin Nasiha wa Juna. Al'ummar da tayi Zumunci yadda ya kamata tafi kowacce samun Arziki.

Tsawon Rai, Zaman Lafiya da cigaba.

Don haka mu rike *ZUMUNCI* kamar yadda yake!

Ya Allah Ka hada kan mu Ka sada Zumunci a tsakanin mu kuma Ka bamu Ladan Zumunci a duniya da lahira. Ameeen summa Ameeen

13/02/2022

Muhammad rasulilah

Wata dalibar obafemi awolowo Mai suna haritage ta rasa ranta bayan fadawa sokawe Dake rukunin dakunan dalibanDaga arewa ...
09/02/2022

Wata dalibar obafemi awolowo Mai suna haritage ta rasa ranta bayan fadawa sokawe Dake rukunin dakunan daliban

Daga arewa radio

07/02/2022

Kotu a kano ta yankewa safiya haruna hukuncin daurin wata shida a gidan gyaran hali ba tare da zabin Tara ba.

05/02/2022
02/02/2022

Gobara ya tashi a F. C. E Kano kusada theater olside

Address

, 233 Nnamdi . Opposite Wutsawa Islamiyya
Kano
MULTIMEDIA

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KABO Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category


Other Newspapers in Kano

Show All