Daula Online Radio

Daula Online Radio Kafar yada labarai mai zaman kanta da take yada shirye-shirye a yanar gizo cikin harshen Hausa.
(1)

Za ku iya tuntuɓarmu kai tsaye a lambar mu ta kira ko WhatsApp 07016740034

Buratai ya bukaci 'yan Nijeriya su yi watsi da tsoma bakin kasashen waje kan zarge-zargen shekaru 33 da s**a gabata kan ...
23/08/2026

Buratai ya bukaci 'yan Nijeriya su yi watsi da tsoma bakin kasashen waje kan zarge-zargen shekaru 33 da s**a gabata kan Tinubu

Tsohon babban hafsan rundunar sojin kasa ta Nijeriya, Laftanar Janar Tukur Buratai (mai ritaya), ya bukaci ’yan Nijeriya da su yi watsi da abin da ya bayyana a matsayin tsoma bakin kasashen waje a cikin harkokin cikin gida na kasar, sakamakon yunkurin fitar da wasu takardu da ake zargin suna da alaka da binciken safarar miyagun kwayoyi da ya shafi shugaba Bola Tinubu sama da shekaru 30 da s**a gabata.

Buratai ya yi wannan kira ne a cikin wata takardar matsaya da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Lahadi.

Tsohon shugaban sojin ya ce bai kamata a bar cece-kucen da ya dabaibaye shugaban kasa ya janyo illa ga martabar Nijeriya a idon duniya ko kuma ya raunana ikon mulkin kasar ba, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Dino Melaye ya yi barazanar maka shugaban hukumar haraji a kotu saboda samun gurbi a kwamitin  kamfen na TinubuTsohon Sa...
23/08/2026

Dino Melaye ya yi barazanar maka shugaban hukumar haraji a kotu saboda samun gurbi a kwamitin kamfen na Tinubu

Tsohon Sanatan Kogi ta Yamma, Dino Melaye, ya ce zai maka Shugaban Hukumar Harajin Najeriya (NRS), Zacch Adedeji, a kotu kan mukamin da aka ba shi a Kwamitin Kamfen na Shugaban Ƙasa na APC na zaɓen 2027.

Melaye, wanda ke cikin shugabannin jam’iyyar ADC a Kogi, ya ce akwai yiwuwar samun rikicin muradun aiki, ganin cewa Adedeji ma’aikacin gwamnati ne kuma aka nada shi Mataimakin Daraktan tara kudaden kamfen Tinubu.

Ya kuma soki matakin da Shugaba Bola Tinubu ya dauka na jagorantar kwamitin kamfen dinsa da kansa, yana mai cewa hakan na nuna rashin amincewa da wasu shugabannin APC.

Melaye ya ce zai garzaya kotu domin a tantance ko nadin Adedeji ya dace da dokokin aikin gwamnati da ka’idojin da’a na ma’aikatan gwamnati.

A jerin kwamitin kamfen da APC ta fitar, Tinubu ne Shugaban Kwamitin, yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima da Shugaban APC na ƙasa Nentawe Yilwatda s**a kasance Mataimakan Shugaban Kwamitin. An nada tsohon Gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari, Darakta-Janar, yayin da Gwamnan Imo, Hope Uzodimma, ya zama Sakatare.

Gwamnan Ogun, Dapo Abiodun, shi ne Daraktan Tara Kudaden Kamfen, yayin da Zacch Adedeji aka nada Mataimakinsa.

Wanene zaɓinku a 2027?
21/08/2026

Wanene zaɓinku a 2027?

Cikin Shekaru bakwai na mulki na, kashi 70 na kasafin kuɗin jihar Borno akan tsaro yake tafiya - ZulumGwamnan Jihar Born...
20/08/2026

Cikin Shekaru bakwai na mulki na, kashi 70 na kasafin kuɗin jihar Borno akan tsaro yake tafiya - Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya ce tsaro da sauran ayyukan jin kai sun cinye kashi 70 cikin 100 na kasafin kuɗin jiharsa a cikin shekaru bakwai da s**a gabata.

Zulum ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, yayin taron kwamitin gudanarwa karo na huɗu na shirin majalisar ɗinkin duniya.

"A siyasance Hon. Kabiru Adam Abdullahi kofar ruwa yayi Expire Irinta siyasa tunda yabar tsarin kwankwasiyya tsarin da y...
19/08/2026

"A siyasance Hon. Kabiru Adam Abdullahi kofar ruwa yayi Expire Irinta siyasa tunda yabar tsarin kwankwasiyya tsarin da yayi masa suttura irinta siyasa"

- CMRD MUSTAPHA UMAR DALA, Ɗan jam'iyyar NDC Kwankwasiyya

Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta tura kwamishinonin ’yan sanda kimanin 30 domin sa ido da jagorantar ayyukan tsaro yayin...
14/08/2026

Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta tura kwamishinonin ’yan sanda kimanin 30 domin sa ido da jagorantar ayyukan tsaro yayin zaɓen gwamnan jihar Osun da za a gudanar gobe Asabar.

Kakakin rundunar ’yan sandan Nijeriya, CSP Anietie Iniedu, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani a birnin Osogbo.

Ya ce sama da jami’an ’yan sanda 15,000 ne za su gudanar da ayyukan tsaro a faɗin jihar, inda aka ware kwamishina guda ga kowace ƙaramar hukuma cikin 30 ɗin jihar.

A cewar Iniedu, an kuma tura jirgin sama mai saukar ungulu da jirage marasa matuƙa domin gudanar da sa ido ta sama kafin zaɓen, yayin da rundunar ’yan sandan kwantar da tarzoma ta samu wakilci a kowace ƙaramar hukuma.

A halin yanzu, Gwamna Ademola Adeleke na jam’iyyar Accord, Bola Oyebamiji na APC da kuma ɗan takarar ADC, Najeem Salaam, na cikin manyan ‘yan takarar da ke fafutukar neman kujerar gwamnan jihar Osun a zaɓen.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa ma’aikatan man fetur na ƙasar cewa matatun man Nijeriya za su dawo aiki y...
14/08/2026

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa ma’aikatan man fetur na ƙasar cewa matatun man Nijeriya za su dawo aiki yadda ya kamata, bayan an kammala matakan sake fasalin yadda ake tafiyar da su.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Tinubu ya bayyana hakan ne jiya Alhamis, yayin da ya karɓi bakuncin shugabannin Ƙungiyar Ma’aikatan Man Fetur ta kasa, NUPENG a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Tinubu ya ce gwamnati ba za ta bari manyan kuɗaɗen da aka zuba wajen kafa da gyaran matatun man ƙasar su tafi a banza ba, inda ya jaddada cewa za a yi gyare-gyare da sake fasalin tsarin gudanar da su domin su samar da riba mai ɗorewa.

Allah ne ya nuna ikonsa kan Pantami, ya saka shi shiga jam'iyyar da ya la'anta, cewar Sanata Rabi'u Musa KwankwasoMe za ...
11/08/2026

Allah ne ya nuna ikonsa kan Pantami, ya saka shi shiga jam'iyyar da ya la'anta, cewar Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso

Me za ku ce?

Tinubu ya bayyana hakan ta bakin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, a wani taron tsaro da haɗin kan ƙa...
11/08/2026

Tinubu ya bayyana hakan ta bakin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, a wani taron tsaro da haɗin kan ƙasa da JIBWIS da Muslim World League s**a shirya.

Me za ku ce?

Ministan lafiya da walwalar jama’a na Nijeriya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya ce gwamnatin Tinubu ta ƙuduri aniyar kawo ...
09/08/2026

Ministan lafiya da walwalar jama’a na Nijeriya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya ce gwamnatin Tinubu ta ƙuduri aniyar kawo ƙarshen zazzabin cizon sauro tare da ƙara zuba kuɗaɗe a fannin kiwon lafiya, domin rage dogaro da tallafin ƙasashen waje.

Gidan talabijin na NTA ya ruwaito Pate ya bayyana hakan ne a Abuja yayin da yake karɓar tawagar kwamitin amintattu na Malaria Consortium, wadda ta kai ziyara ma’aikatar domin taya Nijeriya murnar raguwar yawan yara masu ɗauke da kwayar cutar daga kashi 42 cikin 100 a shekarar 2010 zuwa kashi 15 cikin 100 a 2025.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daula Online Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share