23/06/2026
"Na fito takarar Sanatan Kano ta Arewa ne, biyo bayan tabarbarwar Al'amura, a wannan yanki namu, Kuma duk Wanda ya sanni a lokacinda nake Shugabancin D-Tofa, yasan idan na fada saina cika."
Barr. Saleh Shehu kwuidawa
'Dan takarar Sanatan Kano ta Arewa, Tsohon shugaban karamar Hukumar D-Tofa.
...
Barr Saleh Shehu kwuidawa ya bayyana haka ne cikin wata tattauna da yayi da kafafen yada labarai da dama anan Kano.
Yace: "Ya lura da yadda matsalar tsaro taki ci taki cinyewa a Nigeria, Kuma 'yan Majalisa sune suke da cikakkiyar dama wajen matsawa Gwamnati har sai ta dauki matakinda ya k**ata".
Ya Kuma tabbatar da cewa: "Bazasuje Majalisa su zama 'yan Amshin shata ba, zasu tashi ne suyi gwagwarma har sai an samu Nasara da yardar Allah".
Da yake magana akan siyasa, Barr Saleh Shehu kwuidawa yace: "Gwamnatice take da hannu wajen kunnawa jamiyyun siyasa matsala, domin bata son hamayya, Wanda Hakan shine babban koma bayan da ake son haifarwa da 'yan Nigeria, Kuma Talaka shine zaifi Shan wahala da wannan mataki".
"Dole duk masu neman cigaba su kaucewa wannan tsari na APC domin ceto Nigeria daga mawuyacin halinda ta shiga".