26/09/2023
LABARI MAI FARANTA RAI DAGA KASAR NIJAR
Kasar Faransa ta bada sanarwan kawo karshen yarjejeniyar tsaro da Jamhuriyar Nijar kuma zata kwashe duk sojojinta dake Kasar, sannan ta janye jakadanta dake Kasar Nijar
Bayan haka Faransa tace tana duba yiwuwar kulle ofishin jakadancinta dake babban birnin Kasar Nijar Nyamey, tace ta dauki wadannan matakai ne saboda yanzu babu Demokaradiyya a Nijar (oho dai, aje a hakan 😂)
Kuma a taron Majalisar dinkin duniya da ya gabata Ministan harkokin waje na Kasar Nijar ya halarci taron, hakan na nufin har Majalisar dinkin duniya ta amince da Gwamnatin Soji na Kasar Nijar
Don haka yanzu borin kunya ya rage wa kungiyar ECOWAS ta cire dukkan takunkumin zalunci da rashin imani na karya tattalin arziki da ta kakaba wa Kasar Nijar, tunda uwargijiyarta Faransa ta hakura don dole, kuma masu yunkurin shan jinin Musulmai a Nijar da Arewa sun ji kunya
Yanzu Nijar ta samu 'yancin kai cikin ruwan sanyi ba tare da zubar da jinin mutun daya ba, Nijar zata karbe dukkan ragama na juya tattalin arzikinta daga Faransa
Masana suna cewa nan gaba Nijar sai ta zama wata kasa da 'yan Afirka zasu dinga rububin shiga cikinta domin cin moriyar arziki, saboda suna da tsarin Shûgabanci mai cike da adalci, hatta tsaro a yankin Sahel sai ya inganta
AlhamdulilLah 'Yanci mai dorewa yazo Kasar Nijar, 'Yan uwa na Kasar Nijar muna tayaku murnan samun 'yanci
Ba zamu manta da gudunmawar da Shugaban Izala na duniya Sheikh Abdullahi Bala Lau da tawagarsa s**a bayar ba wajen kawar da fitinar yaki a Nijar, Allah Ya biyasu da Aljannah
AlhamdulilLah 🙏