28/02/2026
LABARAI.
Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya ce s**ar da yake fuskanta daga wasu mutane ba za ta hana shi ci gaba da aiwatar da ayyukan bunkasa jihar ba.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin taron bude-baki da shugabannin kungiyar ’yan kasuwa ta jihar a ranar Alhamis.
Ya ce gwamnatinsa ta kammala shirye-shiryen bayar da rance ga ’yan kasuwa, da zarar an gama gyaran wani bangare na kasuwar Sokoto da gobara ta lalata.
A cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a, Abubakar Bawa, ya fitar, Gwamna Aliyu ya bayyana cewa ci gaban da aka samu a jihar a bayyane yake, yana mai cewa ana kokarin mayar da birnin Sokoto cibiyar yawon bude ido.
Ya kara da cewa gwamnatinsa na maraba da s**a mai ma’ana daga masu fatan alheri, domin inganta ayyukan gwamnati.