30/05/2026
A gurina Barmani Choge ta fiye mani Nana Asma’u ’yar Maulana shehu usman ɗan Fodio sau milyan dubu. Domin kuwa ta ba wa Hausawa gudummawa ta ban mamaki, sannan cikin hikimar waƙe ta na koyar da mata darussan zaman aure da kuma muhimmancin sana’o’i.
Ta yi wakoki barkatai ga sunan kullin a gidajen TV da rediyo ana buga misali da su wajen fadakarwa.
Ni dai duk littattafan da ake ta shararo karyar cewar Nana Asma’u ta yi sun fi dari wallahi ko 10 ban samu ba, sai dai guntayen wakokin da ba su fi page ɗai ɗai ba.
Na karanta "The Caliph’s Sisters", na karanta "One Woman of Jihad", sannan na karanta "The Collected Works of Nana Asma’u"
Kuma duk wakokinta yawanci da Fulfulde da zqbaramci da Larabci ta yi ba da Hausa ba.
Kawai ana zuzutata ne saboda ’yar sarki ce, mahaifinta ya yi kwacen sarauta. Amma babu wani abin kai gida.
Har yau ba wani shahararren littafin nata da ake amfani da shi a ƙasar Hausa,to da ma fa daga ita har ’yan jihadin kaf littattafansu na kare abunda s**a yi ne..... to ba rami me ya kawo rami?🙄
Kuskurene ma da rage kimar Barmani Choge a haɗa da Nana Asma’u.
Ita sdai Hajiya Sa’adatu Aliyu, wadda daga baya ta fi shahara da suna Barmani Choge, an haife ta a shekarar 1943 a tsohuwar lardin Kaduna, yankin da yanzu ya kasance cikin Jihar Katsina. Ta girma kuma ta zama ɗaya daga cikin fitattun mawaƙan mata a ƙasar Hausa da sauran sassan Arewacin Najeriya.
Tana da shekara ashirin da bakwai ta shiga harkar waƙa cikin girmamawa.
Barmani Choge ta yi fice wajen raya Amada, wani nau’in kiɗa da mata manya Hausawa ke matuƙar so. Salon Amada ana amfani da tsagin kora guda biyar a juye a cikin ruwa, inda dattawan mata ke buga kiɗi da tafin hannayensu. Wannan sauƙaƙƙen tsarin yana samar da sauti da ke ratsa rai.
Tana tabo batutuwan da mata da yawa ke tsoron faɗi. Wakokinta suna ƙarfafa mata wajen neman ilimi, shiga sana’o’in hannu, da fahimtar matsayinsu a cikin al’umma.
Haka kuma an santa da wakokin barkwanci, wasu lokuta masu jan hankali, musamman game da kishiyoyi, kyau, da halin rayuwar gida. Duk da haka, saƙonta na asali ya kasance ɗaya: mata su tashi tsaye, su yi ilimi da sana'a.
Ta rasu a shekarar 2013 tana da shekara saba’in, ta bar ’ya’ya shida da jikoki sittin.
Ita kuwa Nana Asma’u an haifeta a shekarar 1793 a garin Degel shekaru goma sha ɗaya (11) kafin fara Jihadin tawaye wa daulolin musulunci na Hausawa.
Su biyu aka haifa a lokaci ɗaya wato tagwaye da ɗayan namiji mai suna Hassan.
Bayan shekara biyu da haihuwarta mahaifiyarta ta rasu a 1795. Ta girma a hannun kishiyoyin mahaifiyarta Aisha da Hauwa wadda ita ce mahaifiyar Muhammad Bello.
Tana da shekara sha ɓiyar ta auri Gidado ɗan Laima a shekarar 1807. Sun tashi daga ƙauyen Degel s**a koma Sokoto a 1809. Likafarta ta ci gaba; mijinta ya zama Waziri a Daular Sakkwato a zamanin Muhammadu Bello da Abu Bakr Atiku.
Ta haifi ’ya’ya uku: babban mai suna AbdulKadir, da Sambo da Tukur.
Mahaifiyar Asma’u, sunanta Maimuna. Ita Maimuna ta kasance ’yar uwar Shehu.
A cikin littafin "One Woman of Jihad" Mack da Boyd sun riwayato cewa mahaifiyar Maimuna da mahaifin ɗan Fodio ’yan’uwa ne na kusa.
Nana Asma’u dai ta shahara a fagen waƙa saboda a lokacin sune su ke mulki bayan tawayen da aka yi wa daulolin musulunci na Hausawa.
To da yake ’yar sarki ce sai ta shahara wajen jagorantar koyar da mata a zamanin.
A wajen shekarar 1830, har ta kafa wata ƙungiyar mata da ake kira “Yan Taru” wacce aikinsu shine suna zagayawa ƙauyuka suna koyar da mata tare da rera wakoki.
Sanadiyyar waƙarta ta zama ɗaya daga cikin fitattun ’ya’yan mahaifinta da aka fi sani bayan Bello da Abdullahi.
Galibin rubuce-rubucenta na wakoki, ta yi su ne cikin harshen Fulfulde da harshen Larabci.
Ta yi wakokin alhini na rashin Fulani da s**a jagoranci tawayen jihadi.
Wasu wakoki kuma takan yi idan ta rasa wani a wajen yaƙi.
Yawanci wakokinta na magana ne akan Daular da mahaifinta wanda ya jagoranci tawayen da aka yi wa daulolin musulunci na Hausawa.
Tana yin wakoki don ƙarfafa ɗaukacin sojojin tawaye.
Wasu wakokinta ta yi su ga ɗan’uwanta Bello wanda ya jagoranci tawayen kisar kiyashi na malaman Yan Doto, wata babbar jami’ar Hausawa ta biyu mafi girma a West Africa bayan jami’ar Timbuktu.
Sannan tana yi wa ɗan’uwanta Atiku da kuma nuna bajintar da ’yan’uwanta s**a yi wajen ruguje daulolin musulunci na Hausawa.
Wani masani tarihi ya ce ba a bar ta a baya ba, domin kuwa ta halarci yaƙe-yaƙe da dama da aka yi akan musulman Hausawa.
Wannan ne ma ya sa ta rubuta wata waƙa mai suna ‘Wakar Gewaye’ don bayyana farin ciki da yadda aka ci masarautun Hausawa.
Bayan mutuwar mahaifinta Asma’u ta zama mataimakiya ta musamman ga Bello wanda ya hau karagar mulki.
Kuma Asma’u tana daga cikin masu rubuta takardu da ake aikawa sauran sarakunan garuruwa da aka kashe sarakunan Hausawa aka maye gurbinsu da Fulani.
Ta rubuta wasu wakoki a harshen Fulfulde irinsu *Mantore Arande*, *Sannore Gidado Waziri* da *Ɓegore*.
Na harshen Hausa kuma akwai “Kiran Ahmada da Murna Kan Nasarar Yaƙi”.
Na Larabci kuma akwai “Mursalat Al-Sha’ar” da “Qasida Min Asma’u”.
A cikin littafin *The Caliph’s Sisters* na Jean Boyd ya riwayato cewa Asma’u tana bai wa mayaƙan tawaye gudummawa na abubuwan yaƙi, tana halarta tarurruka don tattauna dabarun yaƙi da yadda za a kwace mulki.
Sanannen marubucin ya riwayato Asma’u tana wanke takubba ta tsabtace su bayan sun yi da jinin Hausawa.
Sannan tana shirya abincin sojoji sannan tana gina sansanonin mayaƙan tawayen jihadi.
Asma’u ita ce ke karɓar ganima dukiyar yaƙi da bayi wato musulman Hausawa da aka mayar bayi.
Daga 1845 zuwa 1884, Asma’u ta kasance ta musamman ta shahara duk da ta tsufa amma tana daga cikin masu fada a ji.
Jean Boyd da Beverly Mack a littattafansu sun ce ta yi Waƙar tunawa da Sa’ad – ɗan Shehu da Waƙar tunawa da sauran ’yan jihadin da s**a mutu.
Tana yin wakokin tunatar da abubuwan da s**a faru a lokacin tawayen mahaifinta, da bayar da labarin yaƙe-yaƙe, da yadda s**a shirya da tsare-tsaren da s**a yi, da kamabama jarumai da s**a taka rawa wajen murkushe sarakunan Hausawa.
Akwai wasu baitoci na Nana Asma’u da ta yi don murna da sunyi nasara ƙwace mulkin Hausawa yanzu zasu shiga cikin manyan gidajen sarautar Hausawa su fantama su wala.
Ta ce:
“Yunfa ya gudu daga makiyaya da ba su da ko arziƙin takalman sawa (ƙafa tsirara).
Mu (Fulani) da a da ake farauta kamar zomaye,
Yanzu za mu yi rayuwa cikin manyan gidajen ku cikin taƙama.”
Nana Asma’u dai ta rasu a shekarar 1864, tana da shekaru 71 (wani tarihi ya nuna a shekarar 1863) dai-dai da 1280 A.H.
Sources:
The Caliph’s Sisters
One Woman of Jihad
The Collected Works of Nana Asma’u