
07/09/2025
ASALIN RIKICIN GARIN JOS
Bazamu Taɓa Mance Ranar 7 September 2001 Ba A Jos Jihar Filato, Yau Kimanin Shekaru 24 Kenan.
A wannan ranar aka fara rikicin addini tsakanin mabiya addinai 2 mazauna kuma ƴan asalin jihar Filato, Wannan ranar ta kasance baƙar rana agaremu ƴan jihar filato masoya zaman lafiya, A wanann ranar aka yi sanadiyyar mutuwar mutanen da basuji ba basu gani ba aka lalata dukiyoyi aka ɗaidaita mana al'umma aka wargaza zaman lafiyar mu, Kai Innalillahi 😭 Ya Allah Kar Ka Sake Maimaita mana irin wannan rana, Allah ya ƙara mana zaman lafiya a jihar Filato, Allah yaƙara haɗa kawunanmu, Allah yaƙara mana so da ƙaunar juna a jiharmu mai albarka.
Allah Ya Dauwamar Mana Da Zaman Lafiya A Jihar Filato! 🙏🥹
✍️ Faisal Muh'd Sadauki