Freedom Voice Hausa

Freedom Voice Hausa Tashar da zata dinga kawo muku sahin labarai

25/07/2026

Rikicin daba da ya ɓarke da rana tsaka a yankunan Makwarari, Kwalwa da Sheshe da ke Jihar Kano, ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya tare da lalata wasu motoci.

Rahotanni sun bayyana cewa motocin da aka lalata sun haɗa da wasu mallakin Hukumar CRC ta Jihar Kano, inda rikicin ya shafi ƙofar gidan shugaban hukumar, Hon. Shakur Yassar.

An ce an kuma lalata motocin wasu mazauna yankin a lokacin rikicin, lamarin da ya haifar da fargaba da tashin hankali a tsakanin al’ummar yankin.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a samu cikakken bayani daga hukumomin tsaro kan musabbabin rikicin ko k**a waɗanda ake zargi da hannu a lamarin ba.

Gidauniyar Gumel Emirate Foundation ta buƙaci gwamnatin Jihar Jigawa da ta faɗaɗa tare da inganta titin Maigatari zuwa G...
28/06/2026

Gidauniyar Gumel Emirate Foundation ta buƙaci gwamnatin Jihar Jigawa da ta faɗaɗa tare da inganta titin Maigatari zuwa Gumel zuwa hanya mai layuka biyu (dual carriageway), domin karɓar ƙarin zirga-zirgar kasuwanci da ake sa ran za ta ƙaru sak**akon farfaɗo da Kasuwar Export Processing Zone (EPZ) da ke Maigatari.

Shugaban Kwamitin Amintattu na gidauniyar, Alhaji Mohammed Sani Ahmed, Dan Amar na Gumel, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwar manema labarai.

Ya ce farfaɗo da aikin EPZ da Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yi, babban ci gaba ne ga tattalin arzikin jihar.

A cewarsa, aikin wanda ya kwashe sama da shekaru ashirin yana cikin halin dakushewa, yanzu ya zama wani muhimmin mataki na bunƙasa masana’antu, jawo hannun jari da samar da ci gaban tattalin arziki ga al’ummar jihar da yankin baki ɗaya.

Alhaji Mohammed Sani Ahmed ya yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa hangen nesansa da jajircewarsa wajen sauya fasalin tattalin arzikin jihar ta hanyar samar da ingantattun ababen more rayuwa da kuma kyautata yanayin kasuwanci.

Ya kuma bayyana jin daɗin gidauniyar kan yadda masu zuba jari daga ƙasashen waje, ciki har da wasu kamfanoni masu goyon bayan kasar Sin, s**a fara shiga cikin aikin bunƙasa yankin. Ya ce hakan zai taimaka wajen ƙara saka hannun jari, faɗaɗa masana’antu, haɓaka fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje da kuma samar da dubban guraben ayyukan yi ga matasa.

Dan Amar na Gumel ya jaddada cewa al’ummar Masarautar Gumel za su ci gaba da ba gwamnati da masu zuba jari cikakken goyon baya domin tabbatar da tsaro da dorewar aikin, tare da samar da yanayi mai kyau da zai bai wa harkokin kasuwanci damar bunƙasa.

Ya sake bayyana godiyar gidauniyar ga Gwamna Umar Namadi kan wannan gagarumin aiki, yana mai cewa al’ummar Gumel da Jihar Jigawa za su ci gajiyar dimbin alfanun da aikin zai samar nan gaba.

A wani ci gaban kuma, Gidauniyar ta Masarautar ta Gumel ta yabawa gwamnatin Jihar Jigawa kan kafa Cibiyar Kyauta ta Wankin Koda (Dialysis Centre) a Babban Asibitin Gumel.

Alhaji Mohammed Sani Ahmed ya ce wannan mataki shaida ce ta gwamnatin da ke sanya jin daɗin jama’a a gaba, musamman wajen samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga marasa galihu.

Ya bayyana cewa cututtukan koda na daga cikin matsalolin lafiya mafi tsada wajen magani, inda kudin wankin koda ke zama babban ƙalubale ga marasa lafiya da iyalansu. Saboda haka, samar da wannan hidima kyauta ya rage musu nauyin kuɗi tare da dawo musu da fata.

A cewarsa, cibiyar ba wai kawai aikin kiwon lafiya ba ce, har ila yau jari ne na ceton rayuka da bunƙasa albarkatun ɗan Adam. Ya ƙara da cewa tun bayan fara aiki a watan Janairun 2026, mutane 53 sun amfana da cibiyar, yayin da aka gudanar da jimillar zaman wankin koda 383, lamarin da ya nuna muhimmancin cibiyar ga al’umma.

Sai dai ya buƙaci gwamnatin jihar da ta samar da tsarin hasken rana (Solar Power System) a cibiyar domin tabbatar da wadataccen wutar lantarki ba tare da katsewa ba, tare da rage kuɗaɗen gudanarwa domin cibiyar ta ci gaba da sauke nauyin da aka ɗora mata yadda ya k**ata.

Jami’an tsaro a Libya sun k**a wasu ’yan Najeriya biyu a garin Qarabouli bisa zargin yada bidiyo da wasu saƙonni a kafaf...
18/06/2026

Jami’an tsaro a Libya sun k**a wasu ’yan Najeriya biyu a garin Qarabouli bisa zargin yada bidiyo da wasu saƙonni a kafafen sada zumunta da hukumomi s**a ce suna ƙarfafa tashin hankali da aikata laifuka.

Rahotanni sun ce hukumomin Libya sun ɗauki abubuwan da aka wallafa a matsayin barazana ga tsaron jama’a da zaman lafiyar ƙasa. An kuma ce saƙonnin sun saɓa wa dokokin ƙasar.

Tuni aka gurfanar da mutanen biyu tare da miƙa shari’arsu ga ofishin masu gabatar da ƙara domin ci gaba da bincike da yiwuwar gurfanar da su a kotu.

Sai dai ba a bayyana sunayen waɗanda ake zargin ba, haka kuma ba a fayyace ainihin abubuwan da s**a wallafa ba.

A cikin ’yan shekarun nan, hukumomin Libya sun ƙara tsaurara matakan sa ido kan abubuwan da ake yadawa a yanar gizo da suke ganin na iya yin barazana ga tsaron ƙasa.

18/06/2026

Get smarter res

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Legas, ta k**a wani likita, ungozoma da kuma wasu masoya bisa zargin sayar da jariri sabon ka...
17/06/2026

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Legas, ta k**a wani likita, ungozoma da kuma wasu masoya bisa zargin sayar da jariri sabon kan kuɗi Naira miliyan 2.5.

A cewar majiyoyin ’yan sanda, mahaifiyar jaririn mai shekaru 28 da saurayinta sun yanke shawarar ba za su riƙe jaririn ba, inda s**a fara neman waɗanda za su saya tun kafin a haife shi.

Rundunar Sojin Najeriya ta bayyana cewa dakarunta sun kwato manyan mak**ai da kuma abubuwan fashewa na gida (IEDs) daga ...
16/06/2026

Rundunar Sojin Najeriya ta bayyana cewa dakarunta sun kwato manyan mak**ai da kuma abubuwan fashewa na gida (IEDs) daga hannun 'yan ta'addan Lakurawa bayan wata arangama da s**a yi a Jihar Kebbi.
A cikin wata sanarwa da Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulda da Jama'a na Rundunar Sojin Najeriya ta 8 Division, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya fitar a ranar Litinin, ya ce farmakin ya gudana ne a ranar 14 ga watan Yuni a yankin Dogon Daji da ke Karamar Hukumar Dandi ta jihar.
Sanarwar ta ce dakarun sojin sun yi artabu da 'yan ta'addan ne bayan samun bayanan sirri kan motsinsu a yankin. Bayan musayar wuta, maharan sun tsere daga wurin tare da barin wasu manyan mak**ai da na'urorin fashewa da sojojin s**a kwato.
Rundunar ta ce nasarar wani bangare ne na ci gaba da kokarin da jami'an tsaro ke yi na kawar da ayyukan ta'addanci da tabbatar da zaman lafiya a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro.
Sojojin sun kuma jaddada kudurinsu na ci gaba da gudanar da hare-hare kan kungiyoyin masu aikata laifuka tare da kira ga al'umma da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro hadin kai ta hanyar samar da sahihan bayanan sirri.

Tsohon Ministan Kuɗin ƙasar Ken Ofori-Atta, wanda hukumomin Ghana ke nema ruwa a jallo bisa wasu zarge-zargen da ake bin...
16/06/2026

Tsohon Ministan Kuɗin ƙasar Ken Ofori-Atta, wanda hukumomin Ghana ke nema ruwa a jallo bisa wasu zarge-zargen da ake bincike a kansu, ya samu izinin zama na dindindin (Permanent Residency) a ƙasar United States.

Lauyan Ofori-Atta ne ya tabbatar da hakan, yana mai cewa kotu a Amurka ta yi nazarin lamarin tare da duba zarge-zargen da gwamnatin Ghana ke yi masa kafin yanke hukuncin ba shi wannan matsayi.

Hukumomin Ghana dai suna zargin tsohon ministan da hannu a wasu batutuwan da s**a shafi gudanar da harkokin kuɗi a lokacin da yake kan mulki. Sai dai lauyoyinsa sun musanta zarge-zargen, suna masu cewa babu isassun hujjojin da ke tabbatar da aikata wani laifi.

Wannan mataki na Amurka na iya ƙara jawo muhawara tsakanin kasashen biyu, musamman kan batun yiwuwar dawo da shi Ghana domin fuskantar bincike ko shari'a.

Masu sa ido na ganin cewa batun zai iya shafar dangantakar diflomasiyya da kuma ƙoƙarin gwamnatin Ghana na yaƙi da cin hanci da rashawa.

Ministan Tsaro na Ƙasa, Bello Matawalle, ya bayyana cewa nasarorin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta samu a fann...
16/06/2026

Ministan Tsaro na Ƙasa, Bello Matawalle, ya bayyana cewa nasarorin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta samu a fannoni daban-daban za su sanya masu s**ar gwamnati da masu yaɗa farfaganda yin shiru kafin babban zaɓen shekarar 2027.

Matawalle ya ce gwamnatin Tinubu na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen ci gaba da s**a haɗa da inganta tattalin arziki, tsaro da samar da ababen more rayuwa, waɗanda a cewarsa al’umma za su ci gaba da amfana da su.

Ya jaddada cewa duk da s**a da kalubalen da gwamnati ke fuskanta, sak**akon ayyukan da ake gudanarwa zai bayyana a fili, kuma hakan zai ƙara wa shugaban ƙasa karɓuwa a tsakanin ‘yan Najeriya.

Ministan ya kuma yi kira ga magoya bayan jam’iyyar APC da su ci gaba da mara wa gwamnatin baya, yana mai cewa nasarorin da aka samu za su taimaka wajen tabbatar da nasarar Shugaba Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Sai dai masu adawa da gwamnati na ci gaba da bayyana ra’ayoyinsu kan yadda ake tafiyar da harkokin ƙasa, musamman a bangarorin tattalin arziki da walwalar jama'a.

Masanin tattalin arziki, Lekan Olayiwola, ya bayyana cewa yarjejeniyar zaman lafiya da ake dangantawa tsakanin Amurka da...
16/06/2026

Masanin tattalin arziki, Lekan Olayiwola, ya bayyana cewa yarjejeniyar zaman lafiya da ake dangantawa tsakanin Amurka da Iran na iya haifar da sauye-sauye a harkokin tattalin arzikin duniya, fiye da batun farashin mai kaɗai.

Ya ce shekaru ashirin da s**a gabata sun nuna cewa duk abin da ke faruwa a sassa daban-daban na duniya na iya shafar rayuwar yau da kullum a gida, musamman ta hanyar rikicin kuɗi, faduwar kasuwannin mai, da kuma annobar COVID-19.

Olayiwola ya ƙara da cewa irin waɗannan manyan sauye-sauye na duniya suna shigowa kai tsaye cikin kasuwannin gida, kasafin kuɗin gwamnati da kuma rayuwar iyalai, ko da kuwa suna faruwa ne nesa da ƙasa.

Ya yi kira da a riƙa lura da al’amuran duniya domin fahimtar yadda suke tasiri ga tattalin arzikin ƙasa.

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta ƙasa, National Drug Law Enforcement Agency (NDLEA), ta ce ta cafke tarin...
08/06/2026

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta ƙasa, National Drug Law Enforcement Agency (NDLEA), ta ce ta cafke tarin kwayoyin Tramadol guda 320,840 da aka ɓoye a cikin wata mota da ke ɗauke da kayan gini a jihar Taraba.

Hukumar ta kuma bayyana cewa ta k**a wani tsoho mai shekaru 75 a jihar Ebonyi, tare da wasu mata huɗu da ake zargi da harkar miyagun ƙwayoyi a wasu jihohi daban-daban ciki har da Edo, Imo, Kano da Gombe.

NDLEA ta ce waɗannan kamen sun biyo bayan samamen da ta kai a sassa daban-daban na ƙasar, inda aka gano miyagun ƙwayoyi da aka ɓoye cikin kayayyaki domin kauce wa binciken jami’an tsaro.

Hukumar ta ce tana ci gaba da ƙoƙarin daƙile yaduwar miyagun ƙwayoyi a fadin Najeriya, tare da gargadin masu aikata laifi da su daina wannan dabi’a ko su fuskanci hukunci daga doka.

NDLEA ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da gudanar da farmaki a duk fadin ƙasar domin kare matasa da al’umma daga illolin miyagun ƙwayoyi.

Address

Makwarari Street 137
Kano
700234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Freedom Voice Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share