26/05/2026
Ƙungiyar ’Yan Mashal ta mazabar Sheshe ta raba naman sa ga mambobin ƙungiyar, wanda shugaban Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano, Dr. Mansur Mudi Nagoda, ya bayar domin tallafa wa matasa yayin gudanar da bukukuwan Sallah.
Matasan ƙungiyar sun yabawa Dr. Mansur Mudi Nagoda bisa wannan gudunmawa da ya bayar, suna masu bayyana cewa tallafin zai taimaka wajen rage raɗaɗin halin matsin tattalin arziki da kuma ƙara dankon zumunci a tsakanin al’umma.
Haka kuma sun yi addu’ar Allah ya saka masa da alheri tare da ƙara masa nasara a ayyukansa na hidimtawa jama’a.