Freedom Voice Hausa

Freedom Voice Hausa Tashar da zata dinga kawo muku sahin labarai

Ƙungiyar ’Yan Mashal ta mazabar Sheshe ta raba naman sa ga mambobin ƙungiyar, wanda shugaban Hukumar Kula da Asibitoci t...
26/05/2026

Ƙungiyar ’Yan Mashal ta mazabar Sheshe ta raba naman sa ga mambobin ƙungiyar, wanda shugaban Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano, Dr. Mansur Mudi Nagoda, ya bayar domin tallafa wa matasa yayin gudanar da bukukuwan Sallah.

Matasan ƙungiyar sun yabawa Dr. Mansur Mudi Nagoda bisa wannan gudunmawa da ya bayar, suna masu bayyana cewa tallafin zai taimaka wajen rage raɗaɗin halin matsin tattalin arziki da kuma ƙara dankon zumunci a tsakanin al’umma.

Haka kuma sun yi addu’ar Allah ya saka masa da alheri tare da ƙara masa nasara a ayyukansa na hidimtawa jama’a.

21/05/2026

INEC ta bayyana cewa za a gudanar da zaɓen ne domin bai wa al’ummar mazabar damar zaɓar sabon wakilinsu a Majalisar Dattawan Najeriya cikin tsarin dimokuraɗiyya.

21/05/2026

kanin jaridu na yau alhamis 21-5-2026

Wasu ‘yan takarar gwamna uku a jam’iyyar APC mai mulki a jihar Adamawa sun janye daga takarar domin marawa Ahmed Galadim...
21/05/2026

Wasu ‘yan takarar gwamna uku a jam’iyyar APC mai mulki a jihar Adamawa sun janye daga takarar domin marawa Ahmed Galadima Aminu baya gabanin zaɓen fidda gwani na jam’iyyar.

Waɗanda s**a sanar da janyewarsu sun haɗa da Injiniya Diaulhaq Abubakar, Kwamared Mustapha Salihu da Alhaji Ibrahim Thul.

Rahotanni sun ce matakin na zuwa ne kafin gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC da aka shirya gudanarwa a ranar Alhamis a jihar Adamawa.

Masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa janyewar ‘yan takarar na iya ƙara wa Ahmed Galadima Aminu ƙarfi a fafatawar neman tikitin gwamna na jam’iyyar APC a jihar.

Tsohon gwamnan jihar Benue, Sanata Gabriel Suswam, ya bayyana cewa babu wani rabuwar kai tsakanin gwamnan jihar Benue na...
21/05/2026

Tsohon gwamnan jihar Benue, Sanata Gabriel Suswam, ya bayyana cewa babu wani rabuwar kai tsakanin gwamnan jihar Benue na yanzu, Hyacinth Alia, da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, tare da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a jihar.

Suswam ya bayyana hakan ne yayin wata hira da gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce Alia da Akume sun sasanta sabanin da ke tsakaninsu bayan wani babban taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar da ke Makurdi.

Ya ce taron ya taimaka wajen dawo da haɗin kai da fahimtar juna tsakanin shugabannin jam’iyyar a jihar Benue.

Tsohon gwamnan ya kuma jaddada cewa gwamna Alia na ci gaba da mutunta Akume a matsayin uban siyasa, yana mai cewa shugabannin APC a jihar sun himmatu wajen tabbatar da haɗin kai domin ci gaban jam’iyyar da jihar baki ɗaya.

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta nesanta kanta da wani shiri da ake yaɗawa a kafafen sadarwa mai suna AFRIPOL 2026, tana...
21/05/2026

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta nesanta kanta da wani shiri da ake yaɗawa a kafafen sadarwa mai suna AFRIPOL 2026, tana mai gargadin jama’a cewa shirin ba shi da amincewa ko goyon bayan rundunar.

A cikin wata sanarwa da aka fitar daga hedikwatar rundunar da ke Abuja, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Anthony Okon Placid, ya bayyana cewa alaƙanta rundunar da shirin ba tare da izini ba abu ne mai yaudara da kuma rashin gaskiya.

Ya ce rundunar ’yan sandan Najeriya ba ta amince da shirin ba, ba ta goyi bayansa ba, kuma ba ta ba da izinin gudanar da shi ba.

Rundunar ta kuma buƙaci jama’a da su yi taka-tsantsan tare da kaucewa shiga duk wata hulɗa da shirin AFRIPOL 2026, domin gujewa fadawa cikin yaudara ko asarar dukiya.

Fadar Shugaban Ƙasa ta mayar da martani bayan wasu ‘yan Najeriya sun mamaye shafukan sada zumunta na Bankin Duniya suna ...
21/05/2026

Fadar Shugaban Ƙasa ta mayar da martani bayan wasu ‘yan Najeriya sun mamaye shafukan sada zumunta na Bankin Duniya suna roƙon ƙungiyar da ta daina bai wa Najeriya rance.

Jaridar Daily Post ta rawaito cewa mutane da dama sun yi kira ga Bankin Duniyar da ya hana Najeriya samun karin bashin kuɗi, saboda yadda ake nuna damuwa kan yawaitar bashin ƙasar.

Da yake magana a gidan talabijin na Arise a ranar Alhamis, mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan sadarwa da manufofi, Daniel Bwala, ya ce yana da wahala a tantance ko waɗanda s**a yi wannan kira mambobin jam’iyyun adawa ne ko kuma talakawan ƙasa na gari.

A cewarsa, kasancewar ana gab da shiga yanayin siyasar zaɓe, akwai yiwuwar wasu daga cikin masu irin waɗannan kiraye-kiraye suna da manufar siyasa.

Daniel Bwala ya ce gwamnati na ci gaba da kokarin aiwatar da manufofin tattalin arziki da za su taimaka wajen farfaɗo da tattalin arzikin Najeriya tare da rage matsin rayuwa da jama’a ke ciki.

Wasu ’yan takarar jam’iyyar APC biyu sun bayyana kansu a matsayin sahihan masu tikitin takarar kujerar Ibadan North West...
18/05/2026

Wasu ’yan takarar jam’iyyar APC biyu sun bayyana kansu a matsayin sahihan masu tikitin takarar kujerar Ibadan North West/South West gabanin zaɓen cike gurbi da ke tafe.

Rahotanni sun ce kowanne daga cikin ’yan takarar na ikirarin cewa shi ne ya samu amincewar shugabannin jam’iyyar da kuma nasara a tsarin zaɓen fidda gwani da aka gudanar.

Lamarin ya haifar da ruɗani a cikin jam’iyyar APC a yankin, inda magoya bayan ɓangarorin biyu ke ci gaba da nuna goyon baya ga ’yan takararsu.

Sai dai shugabannin jam’iyyar a jihar Oyo sun ce suna ƙoƙarin sasanta rikicin domin tabbatar da haɗin kai kafin zaɓen.

Wata babbar kotun tarayya ta bai wa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, beli kan kuɗi naira miliyan ɗari tare d...
18/05/2026

Wata babbar kotun tarayya ta bai wa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, beli kan kuɗi naira miliyan ɗari tare da tsauraran sharudda bayan gurfanar da shi bisa zargin karya dokokin tsaron ƙasa.

Kotun ta umarci El-Rufai da ya gabatar da mutane biyu da za su tsaya masa, inda dole ne su kasance manyan ma’aikatan gwamnati masu matsayi, tare da mallakar kadarori a Abuja.

Haka kuma kotun ta hana shi yin wata magana a bainar jama’a da ka iya shafar binciken da ake ci gaba da yi, tare da umartar sa da ya miƙa fasfo ɗinsa ga kotu har sai an kammala shari’ar.

An dage sauraron karar zuwa wani lokaci domin ci gaba da gabatar da hujjoji daga bangarorin da ke shari’a.

Rahotanni sun ce shirin ya haɗa da wayar da kan jama’a kan hanyoyin kare rayuka da dukiyoyi, tsaftace magudanan ruwa, da...
17/05/2026

Rahotanni sun ce shirin ya haɗa da wayar da kan jama’a kan hanyoyin kare rayuka da dukiyoyi, tsaftace magudanan ruwa, da kuma tanadin wuraren da za a kwashe mutane idan buƙatar hakan ta taso.
Jami’ai da shugabannin al’umma a yankunan sun bayyana cewa an ɗauki matakan ne bayan hasashen samun ruwan sama mai yawa a bana, wanda ka iya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.
Haka kuma, sun buƙaci mazauna yankunan da su riƙa bin umarnin hukumomi tare da kaucewa gina gidaje a hanyoyin ruwa domin rage haɗarin ambaliya.

Address

Makwarari Street 137
Kano
700234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Freedom Voice Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share