22/08/2026
Tinubu ya kafa kwamitin shirye-shiryen yakin neman zaben sa a Jam'iyyar APC 2027
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa kwamitin da zai jagoranci shirye-shiryen yakin neman zabensa a ƙarƙashin jam’iyyar APC domin babban zaɓen 2027.
A cikin tsarin kwamitin, an ɗora wa tsohon Gwamnan Zamfara kuma Sanata, Abdulaziz Yari, alhakin jagorantar ayyukan kwamitin a matsayin Darakta-Janar. Shi kuwa Gwamnan Imo, Hope Uzodimma, an ba shi matsayin Sakatare.
Wannan bayani ya fito ne daga wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa ta wallafa a safiyar Asabar, wadda mai ba Shugaba Tinubu shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu shi ne zai jagoranci kwamitin, yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, zai kasance Mataimakin Shugaban Kwamitin na Farko.
An kafa kwamitin ne a yayin da jam’iyyar APC ke fara shirye-shiryenta gabanin babban zaɓen ƙasa na shekarar 2027.