Hausa-Fulani

Hausa-Fulani Sallallahu Alaika wa,ala Alika Wasallim.👈

TARBIYYA: Nan Wasu Yara Mata Ne S**a Ajiye Kayan Tallarsu S**a Yi Sallar La'asar A Bakin Kofar Sakatariyar Karamar Hukum...
27/10/2025

TARBIYYA: Nan Wasu Yara Mata Ne S**a Ajiye Kayan Tallarsu S**a Yi Sallar La'asar A Bakin Kofar Sakatariyar Karamar Hukumar Jahun Dake Jigawa A Jiya Da Yamma

Wace fata za ku yi musu?

Kana Son Duba Sahihan Labarai Shigo Jaridar 👉 Hausa Fulani 👈 Yanzu Yi Following Karku Bari Komai Ya Wuceku...

🛑 DA DUMI-DUMI: Masu zanga-zanga a Garoua, Kamaru, sun kwace motocin jami’an tsaro, sannan suke yawo da su cikin zanga-z...
27/10/2025

🛑 DA DUMI-DUMI: Masu zanga-zanga a Garoua, Kamaru, sun kwace motocin jami’an tsaro, sannan suke yawo da su cikin zanga-zangar. 👇👇👇

Yadda zanga-zanga ta barke a birnin Douala da ke Kamaru, bayan sanar da sakamakon zaben shugaban kasar da ya bai wa Shug...
27/10/2025

Yadda zanga-zanga ta barke a birnin Douala da ke Kamaru, bayan sanar da sakamakon zaben shugaban kasar da ya bai wa Shugaba Paul Biya nasara.

📸: Aljazeera

20/10/2025

Tare da Musbahu Idris Musa – Yanzun nan aka san da ni a matsayin ɗaya daga cikin manyan masoyansu!

DA ƊUMI-ƊUMI: Fitaccen malamin addinin Musulunci Sharif Muhammad Auwal Zariya ya bayyana cewa wadanda Basu fihimci Al'qu...
20/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Fitaccen malamin addinin Musulunci Sharif Muhammad Auwal Zariya ya bayyana cewa wadanda Basu fihimci Al'qurani ba suna tunanin Akwai wata magana da Zata shafe Al'qurani Amma abin da Basu sani ba ba abun Dake shafe Al'qurani.

‎Inda suke cewa wajibi ne a yaki masu da'awar Al'qurani zallah inda s**a ce wai Yan kala kato ne sune s**a haddasa rikicin Mai tatsine, Amma Abun lura shine tun daga shekarar 2000 zuwa yanzu babu babbar musifa da ta addabi mutane irin Yan Boko Haram to Suma sunan su Jama'atu ahlussunah lid-da'awati Wal jihaad me yasa ba'a ce duk Dan ahlussunah Dan Boko Haram bane? Saboda hadafin su daban da na sauran ahlussunah , wannan shine adalchi.

‎Saboda haka ka Kalli Wanda yace shi Al'qurani zallah zaiyi kace masa Dan tatsine, to Kai ne Dan tatsine domin inda hakane to kaima Dan Boko Haram ne.

‎Inda ya Kara da jaddada cewa Taron Dangi Akan Alqurani Da Masu Bin Alqur'ani Zallah Bazaiyi Nasara Ba,Babu Wani Wahayi Bayan Alqur'ani,Shine Kadai Littafin Allah Wanda Ya Zama Dole Musulmi Yayi Imani Dashi,Ba Wani Ba.

Me zaku iya cewa ❓

-- S'C PRESS TV

15/10/2025

🌙 Tambaya ta biyu:

“Shin an haife shi da kwalli a idanunsa?”

❌ Amsa:

Babu wani hadisi sahihi, ko riwayar da ta karɓu daga sahabbai, da ta tabbatar da cewa Annabi (S.A.W) an haife shi da kwalli a idonsa.

Wannan magana ƙarya ce da aka shahara a cikin al’umma, ba ta da tushe daga Bukhari, Muslim, ko sauran sahihan hadisai.

Malamai irin su As-Suyuti, Ibn Hajar, da Al-Albani sun yi bayani cewa:

> “Babu asali ga maganar cewa Annabi an haife shi da kwalli. Abin da ya tabbata kawai shi ne — idanunsa suna da kyau, suna kyalli, kamar wanda yake da kwalli.”

08/10/2025

Tare da Adam Ashaka – Yanzun nan aka san da ni a matsayin ɗaya daga cikin manyan masoyansu!

08/10/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Malamin Addini Rabiu Abubakar, Ibrahim Abdullahi Abdullahi, Kamal Shaibu, Aliyu Dahiru, Zaharadden Ibrahim

Jajurtaccen soja mai da'awar Musulumci Malam Adamu Ashaka tare da wasu Mata masu bautar Doddani da ya musulumtar ya kuma...
04/10/2025

Jajurtaccen soja mai da'awar Musulumci Malam Adamu Ashaka tare da wasu Mata masu bautar Doddani da ya musulumtar ya kuma basu hijabai domin su suturta jikinsu ta hanyar taimako da wasu bayin Allah s**a tura masa.

01/10/2025
BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA GWAMNATIN KANO  DA KOMITIN BINCIKEN SHEIKH LAWAL TRIUMP  AKAN WA'AZINSA DA YA KAWO HUSUMA ACIK...
01/10/2025

BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA GWAMNATIN KANO DA KOMITIN BINCIKEN SHEIKH LAWAL TRIUMP AKAN WA'AZINSA DA YA KAWO HUSUMA ACIKIN AL'UMMA :-

Daga:- Sheikh Husaini Yusuf Mabera Sokoto.

Ina bada Shawara zuwa ga Gwamnatin Kano a karkashin jagorancin Mai Girma Gomnan Kano cewa ba bukatar wani zaman mukabala ko wata tattaunawar da zata kawo kace nace acikin al'umma game da zancen da Sheikh Lawal Triump yayyi acikin bayanan sa .

Wannan matsalar ta haihuwar Annabi da kwalli ko kaciya malamai da sauran magabata sun sha banban acikin ta kuma kowa yana da madogararsa acikin littafan musulunci da kuma tarihin haihuwar Annabi (SAW).

Don haka banga dacewar ayi wata mukabalar da zata iya kawo hargitsi da surutai acikin al'umma ba .

Abinda ya kamata shine , malamai masu tsoron Allah da kuma aikata abu domin neman yardar Allah da kuma masu adalci acikin makusantan Sheikh Lawal Triump su kira shi suyi masa nasiha akan rashin ingancin us'lubin da yayyi amfani da shi a wajen isar da sakon da yake son ya isar acikin al'umma musamman ga abinda ya shafi mutunci da matsayin Annabi Muhammad (SAW) .

Babu ko shakka , wallahi Sheikh Lawan Triump yayi kuskuren da masoyansa ko wasu makusantarsa s**a ki fada masa gaskiya saboda wani son rai ko kuma makauniyar kauna ko kungiyanci .

Ba laifi bane ko abin kunya idan malami yayi tuntuben harshe ko kuskure ga fadin magana ko ga wa'azi anyi masa gyara .

Saboda haka ya kamata Malaman Sheikh Lawan Triump su gargade shi ya janye wasu kalamai da yayyi na rashin hikima a lokacin da yake bayaninsa ga abinda ya shafi manzon Allah .

Kuma ya bayyanar da janyewarsa daga maganganun a bayyane kamar yadda ya further suba bayyane .

Muna rokon Allah ya datar damu akan tafarkin gaskiya . Ameen .

*"Shekarar 1985 ta bar tarihi!*  Lokacin da Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB) ya kifar da gwamnatin Janar Muhammadu...
27/09/2025

*"Shekarar 1985 ta bar tarihi!*
Lokacin da Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB) ya kifar da gwamnatin Janar Muhammadu Buhari. Wannan lamari ya canza salon siyasar Najeriya har abada. Me ya faru? Me ya sa? Wannan hoton ya tunatar da mu irin jarumtaka da rikice-rikicen da s**a faru a baya. Tarihi bai manta ba."
A juyin mulkin da aka yi a ranar 31 ga Disamba, 1983, an kifar da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari daga mulki a ranar 27 ga Agusta, 1985, ta hannun Janar Ibrahim Badamasi Babangida. Ga wasu daga cikin dalilan da ake ganin sun janyo hakan:

1. *Tsauraran Matakai*: Gwamnatin Buhari ta dauki matakai masu tsauri na gyaran hali ("War Against Indiscipline – WAI"), wanda ya hada da hukunci mai tsanani ga laifuka da kananan kurakurai, wanda wasu s**a dauka a matsayin rashin adalci da danniya.

2. *Rashin 'Yancin Fadar Albarkacin Baki*: An kulle 'yan jarida da dama kuma aka takaita kafafen yada labarai, wanda ya janyo cece-kuce da rashin goyon baya daga wasu sassa na kasa.

3. *Tattalin Arziki*: Duk da cewa an nemi hana cin hanci da rashawa, tattalin arzikin kasar ya shiga mawuyacin hali. An saka takunkumi kan kasuwanci, an rage shigo da kayayyaki, kuma 'yan kasuwa da manoma sun shiga cikin kunci.

4. *Rikicin Cikin Gida a Soji*: Akwai rahotannin rashin jituwa tsakanin manyan hafsoshin soja, musamman tsakanin Buhari da Babangida, wanda ya kai ga juyin mulki.

5. *Babu Ci Gaba Mai Gamsarwa*: Duk da manufofi nagari, mutane da dama sun ji kamar babu canji mai gamsarwa, kuma an ci gaba da fama da talauci da rashin aikin yi.
*








**

Address

Dorayi
Kano
641113

Telephone

+2347082104343

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa-Fulani posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa-Fulani:

Share