15/08/2025
'Yan sanda a Kano sun tabbatar wa mazauna yankin da tsaro mai kyau yayin zaɓen cike gurbi.
CP Bakori ya ce hukumomin tsaro a Kano suna aiki tare don tabbatar da zaben cike gurbi ba tare da rikici ba.
Rundunar 'yan sanda a Kano ta tabbatar wa mazauna yankin da za a gudanar da zaben cike gurbi a Bagwai/Shanono da Ghari/Tsanyawa a ranar Asabar da tsaro mai kyau.
Kwamishinan ‘yan sandan, Ibrahim Bakori ne ya bayyana haka a wata tattaunawa ta wayar tarho ranar Juma’a a Kano.
Mista Bakori ya ce hukumomin tsaro a Kano suna aiki tare don ganin an gudanar da zaben fidda gwani ba tare da rikici ba.
Ya yi bayanin cewa an bayar da umarni karara na aiki ga jami’an da aka tura domin samar da tsaro a kowace rumfar zabe a fadin kananan hukumomin da abin ya shafa.
Kwamishinan ya ce an tattara isassun jami’an tsaro domin samar da isasshen tsaro kafin zaben fid da gwani, da lokacin da kuma bayan zaben.
Ya ce an samar da isassun matakan tsaro da za su tabbatar da zaman lafiya a jihar.
Kwamishinan ya tabbatar wa mazauna jihar cewa za su iya gudanar da aikinsu cikin walwala a ranar Asabar ba tare da wata fargaba ba.
Ya bukaci jam’iyyun siyasa da ‘yan takara da su gudanar da ayyukansu yadda ya k**ata domin samar da zaman lafiya da gudanar da zaben cikin lumana.
"Za mu ci gaba da kasancewa a bayyane a rumfunan zabe don kare haƙƙin masu jefa ƙuri'a da kuma hana tsoratarwa.
“Ba za mu amince da ‘yan daba, da tsoratarwa, da tada kayar baya kafin zabe, da lokacin zabe, da kuma bayan zabe ba, za mu samar da daidaito ga dukkan jam’iyyun siyasa, kuma duk wani abu da zai iya kawo rudani a jihar ba za a amince da shi ba,” inji shi.
CP Bakori ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu ya karya doka za a k**a shi tare da gurfanar da shi a gaban kuliya.