New Africa Hausa OnlineTv

New Africa Hausa OnlineTv Ku kasance tare da tashar New Africa Hausa da bibiyar shafukan mu na zumunta don kasancewa tare da mu

BREAKING NEWS: Super falcons of Nigeria 🇳🇬 wins Women's Africa Cup of Nations.   🏆
26/07/2025

BREAKING NEWS: Super falcons of Nigeria 🇳🇬 wins Women's Africa Cup of Nations. 🏆

Salamun AlikumAlhamdulillah Yau chikin iyawar Allah Mun gabatar da jin raayin Alumma da koken su akan gyaran kundin tsar...
26/07/2025

Salamun Alikum

Alhamdulillah Yau chikin iyawar Allah Mun gabatar da jin raayin Alumma da koken su akan gyaran kundin tsarin Mulkin Nigeria Wanda ya gudana a Centre B, Sokoto, kebbi da Zamfara a Garin Sokoto.

Alhamdulillah duka Alummar mu na Jihar Zamfara, wadanda s**a turamun da bukatun su, dukkan su sun gabatar da presentation na su a gaban committee lapia kalau Kuma kwamiti ya amshi duka takardun su domin wuche wa da su Abuja Don chi gaba da aikin.

Allah bamu dukkan Alherin da ke chikin wannan tsarin, Allah bamu Zaman lapia Mai dorewa a jihar Zamfara. Allah jikan Mai Martaba Sarkin katsinan Gusau Alh. DR. IBRAHIM BELLO.

Allah shi yabbamu
Allah mun gode

Hon. Kabiru Amadu Mai palace
MHR Gusau /Tsafe federal constituency Zamfara State
Chairman House Committee on Sports
26th July 2025.

Salamun Alaikum                                     SANARWA!     SANARWA!!      SANARWA!!! Kamar yadda nayi sanarwa sati...
22/07/2025

Salamun Alaikum

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

Kamar yadda nayi sanarwa sati biyu da s**a wuche akan kokarin da Majalisar kasa ke kanyi na Gyaran kundin tsarin Mulkin Nigeria wato (CONSTITUTION OF THE FEDERAL REPUBLIC OF NIGERIA).

Gobe idan Allah ya kaimu zan gabatar wa Kwamitin Majalisa wadanda da s**a nemi su gabatar da korafi su da koken su akan abunda suke bukata ayi musu ko a saka a chikin dokokin kasa, ko rashin amin chewa da wata doka da ke chiki yanzun wadda ake ganin chutarwa che ga addinin mu da Aladarmu.

Wadanda s**a turamun da takardu Don neman basu damar gabatarwa su sune kamar haka:-

1. Council of Ulamah Zamfara State Branch. Karkashin Jagoranchin Sheikh Ahmad Umar kanoma

2. Ulamah Cunsultative Forum Zamfara State. Karkashin Jagoranchin Sheikh Ahmad Umar kanoma

3. Zamfara State Coalition of NGO's, 2 Groups. Karkashin Jagoranchin Ambassador Ibrahim Tudu

3. National Council of Civil Society and NGO's Northwest region.

4. Movement for the creation SAURI LG from present Tsafe LG. Mutane 80 s**a saka hannu

5. Movement for the creation of DUTSI LG from present ZURMI LG. Mutum 32 s**a saka hannu.

6. Waziri Tsafe Cunsultative forum. Kakrkashin Jagoranchin Alh. Lawali saidu

7. Movement for the creation of MAGAMI LG from present GUSAU LG. Mutum 60 s**a saka hannu.

8. Movement for the creation of KWATARKWASHI LG From present BUNGUƊU LG. Advocacy Group for LG Development

9. Movement for the creation of KUYAMBANA LG (DANSADAU EMIRATE) from PRESENT MARU LG. Mutane 119 s**a saka hannu kakrkashin Jagoranchin Sarkin kudun Dan sadau. Alh Muhammadu Garba Atu II

10. Movement for the creation of YANKUZO LG From present TSAFE LG. Mutum 23 s**a saka hannu kakrkashin Yankuzo Development Association.

11. Movement for the creation of FEGIN MAHE WARD from PRESENT RUWA BORE WARD in Gusau LG. Mutane 16 s**a turo da irin wannan sakon kakrkashin Jagoranchin NURA ISAH.

Wadannan sune na samu sakon su ta Email Dina Kuma gobe inshaAllah zan gabatar wa da kwamiti su domin asaka su chikin wadanda zasu gabatar a Sokoto gaban kwamiti Kuma a dauko Azo da su Majalisa domin tattauna su.

Kowa zaije da 2 copies na Presentation dinsa, mutum 2 ko 3 sun Isa Wakilchi wajen gabatarwa idan a je gabatarwa summary kawai Mai gabatarwa zai gabatar sannan ya isar da copies din ga hannun chairman na Kwamitin a wurin.

An gayyachi Mai girma Gwamnan jihar Zamfara a madadin Gwamnatin jiha da Alumma baki daya inda zai gabatar da Jawabi a madadin bukatun Alumma Zamfara baki daya.

An gayyachi sarakuna guda 4 daga Zamfara suma Mai Martaba sarkin Zamfara Anka zai gabatar da Jawabi a madadin su.

Wadannan sune kadai zaa ba dama suyi magana, Kuma abubuwan da s**a gabatar sue kadai abubuwan da zaa tattauna a Majalisa idan angama.

Yana da kyau kowa yasan haka saboda abune da ya shafi dukkan DAN Asalin Zamfara baki daya.
Muna rokon duka masu yin media suyi sharing a kowane group pls don kowa yasan me ake chiki, haka nasa ayi sanarwa a gidanjen Radio Don saboda wasu Alumma da basu amfani da kafofin sadarwa na Zamani.

Idan Kuma akwai Wanda na tsallake nasu ban saka ba pls. Su Kara turamun a Email Dina. [email protected]

Ranar Assabar 26th July, karfe 10 na safe a Garin Sokoto inshaAllah.

Allah shi yabbamu
Allah mungode

Hon. Kabiru Amadu Mai palace
MHR Gusau /Tsafe federal constituency Zamfara State
Chairman House Committee on Sports
21st July 2025.

Tsugunne bata karewa a Arewa...!!!Ana zargin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya mari Minista a gaban Mataimakin Shugaban ƙasa ...
19/04/2025

Tsugunne bata karewa a Arewa...!!!

Ana zargin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya mari Minista a gaban Mataimakin Shugaban ƙasa

Mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Auwal Jatau, da Ministan Harkokin Waje, Jakada Yusuf Tuggar, sun yi sa'in-sa mai zafi da ta rikide zuwa fada da hannu a jiya Juma’a.

Wannan lamari ya faru ne a cikin wata motar bas da ke dauke da masu rike da mukaman siyasa, yayin da suke kan hanyarsu zuwa garin Bauchi daga Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Sir Abubakar Tafawa Balewa da ke jihar Bauchi.

Jaridar Leadership ta gano cewa mataimakin gwamnan ya tsoma baki ne a cikin rikicin farko da ya fara tsakanin ubangidansa, Gwamna Bala Mohammed, da ministan. Tsoma bakin Jatau ya kara dagula lamarin, har ya sa sauran mutane da ke cikin motar s**a shiga tsakani domin hana ci gaba da rikicin.

Rahotanni da ba a tabbatar da su ba sun ce Jatau ya mari ministan a cikin hargitsin da ya biyo baya.

An kuma rawaito cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Farfesa Ali Pate, da wasu Sanatoci suna cikin motar a lokacin.

Da aka tuntubi mai magana da yawun gwamnan Bauchi, Mukhatar Gidado, ya ki yin tsokaci, inda ya ce bai ga abin da ya faru ba kuma ba a sanar da shi komai ba.

Wata majiya kusa da Tuggar, wadda ta nemi a boye sunan ta tabbatar da cewa an samu sabani tsakanin Gwamna Mohammed da ministan, amma ya ce Jatau ya tsoma baki ne domin goyon bayan ubangidansa.

Sai dai bai tabbatar da samun fada da hannu tsakanin mataimakin gwamnan da ministan ba, in ji jaridar Leadership.

New Africa Hausa OnlineTv

YANZU-YANZU: Ana sa Ran Tinubu Zai Nada Kwankwaso a Matsayin Sakataren Gwabnatin Tarayya. Wata Majiya Mai Tushe ta ce, S...
18/04/2025

YANZU-YANZU: Ana sa Ran Tinubu Zai Nada Kwankwaso a Matsayin Sakataren Gwabnatin Tarayya. Wata Majiya Mai Tushe ta ce, Shugaba Tinubu na tunanin nada Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin sakataren Gwamnatin tarayya (SGF).

17/04/2025

Najeriya da Nijar sun rattaba hannu kan yarjejeniyar sulhu da sasanci a tsakanin su.

A yayin tattaunawa kenan da ta gudana da Alh. Ibrahim Danyaro, daya daga cikin Iyayen gidauniyar -Safa Green Hope Founda...
12/04/2025

A yayin tattaunawa kenan da ta gudana da Alh. Ibrahim Danyaro, daya daga cikin Iyayen gidauniyar -Safa Green Hope Foundation a lokacin wata ziyarar da ta kai masa a gidan sa dake kano a makon da ya gabata, yayi alkawarin bada kyautar itatuwan dashe adadi mai yawa domin mayar da kano koriya a karkashin wanann Foundation ta As-SAFA Green Hope, Chairman yayi wanann bayani ne a lokacin wannan ziyara da muka Kai masa har gidan sa dake kano.

Cikin Wadanda s**a halarta, akwai:-
(1) Founder/CEO As-safa, Alhafiz Ismail Maiduguri.
(2) Technical Director M Bashir Gafia.
(3) National Director Media and Publicity, Umar Isah.
(4) Kano State Co-ordinator, Ayuba Abdullahi.
(5) M Najashi Alkali.
(6) Photographer Rabiu Kabiru.

Allah ya saka masa da mafificin alkhairi, ya kuma saka mana Albarka a cikin wannan aiki na alkhairi.

Fitaccen mawakin nan dan asalin jahar lagos Idris Abdulkarim, wanda yayi wakar (Najeriya jaga-jaga) a lokacin mulkin Oba...
11/04/2025

Fitaccen mawakin nan dan asalin jahar lagos Idris Abdulkarim, wanda yayi wakar (Najeriya jaga-jaga) a lokacin mulkin Obasanjo, a yanzu ma ya sake yin sabuwar Waƙa mai taken (Tell Your Papa) don nuna kin jinin gwamnatin tinubu, inda mawaƙin ke kira ga ɗan shugaban ƙasa, Seyi Tinubu ya faɗa wa mahaifinsa cewa mutane na mutuwa saboda ƙuncin rayuwa da rashin tsaro a Najeriya.

Wanda tuni hukumomi a Najeriya musamman NCC ta hana gidajen rediyo da talabijin na kasar watsa wannan waka zuwa ga kunnuwan yan kasa.

Shin mu 'yan ƙasa yaya zamu kalli wannan mataki..?

Sannan ta wace fuska zamu kalli ita kanta wakar da sakon da ke cikin ta, shin Idris Abdulkarim yayi bajinta ne ko kuma rashin kyautawa...?
Abul Banāt

Tashar New Africa Hausa OnlineTv Don Bunƙasa Naahiyar Africa, na yiwa al'ummar Musulmi Barka da Sallah, da fatan Allah y...
30/03/2025

Tashar New Africa Hausa OnlineTv Don Bunƙasa Naahiyar Africa, na yiwa al'ummar Musulmi Barka da Sallah, da fatan Allah ya karɓi ibadunmu na Azumin Ramadana.

Fatan za a yi shagulgulan Sallah lafiya.

Address

Kano

Opening Hours

Monday 06:00 - 21:00
Tuesday 06:00 - 21:00
Wednesday 06:00 - 21:00
Thursday 06:00 - 21:00
Friday 06:00 - 18:00
Saturday 06:00 - 18:00
Sunday 06:00 - 21:00

Telephone

+2349078780740

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when New Africa Hausa OnlineTv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to New Africa Hausa OnlineTv:

Share