Hantsi24

Hantsi24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Hantsi24, Media/News Company, Kano.

Shugaban Hukumar NAHCON da Tawagarsa Zasu Tafi Saudiyya Don Kammala Shirye-shiryen Hajjin 2026Hukumar Alhazai ta Ƙasa (N...
21/09/2025

Shugaban Hukumar NAHCON da Tawagarsa Zasu Tafi Saudiyya Don Kammala Shirye-shiryen Hajjin 2026

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da cewa Shugabanta, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, tare da wasu kwamishinoni da sakataren hukumar, Dakta Mustapha M. Ali, zasu tafi kasar Saudiyya a ranar Litinin, 22 ga Satumba, 2025.

Ziyarar na da nufin kammala yarjejeniyoyin da ake yi da masu yiwa alhazai hidima a Saudiyya, musamman kan harkokin sansanoni alhazai a Mina da Arfat, da sufuri da kuma masauki, domin tabbatar da shirye-shirye tun kafin lokacin gudanar da Hajjin shekarar 2026.

Hakan na zuwa ne bisa ga jadawalin da Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta fitar, wanda ya kayyade cewa daga ranar 6 zuwa 23 ga Satumba, 2025 (15–29 Safar 1447H) za a kammala saka hannu a kan yarjejeniyar da biyan kuɗin farko na sansanonin Hajji. Haka kuma an sanya ranakun 23 zuwa 24 ga Satumba, 2025 (1–2 Rabi’ul Awwal 1447H) a matsayin wa’adin ƙarshe na yin kammala yarjejeniyar kan muhimman ayyuka irin su sufuri da masauki.

A cewar sanarwar, Ma’aikatar ta kuma bayyana ranar 12 ga Oktoba, 2025 (20 Rabi’ul Thani 1447H) a matsayin wa’adin ƙarshe na shigar da bayanan alhazai da kuma rabonsu cikin rukuni ta hanyar manhajar Nusuk.

Daga ɓangaren Najeriya kuwa, NAHCON ta saka ranar 8 ga Oktoba, 2025 a matsayin ƙarshe ga hukumomin jin daɗin alhazai na jihohi da kamfanonin hajji masu lasisi su mika kuɗaɗen hajjin 2026.

Hukumar ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki su yi biyayya da waɗannan wa’adin domin gudanar da shirye-shiryen Hajji cikin sauƙi tare da tabbatar da nasarar aikin Hajji ga alhazan Najeriya.

UNGA: Najeriya ta goyi bayan Falasɗinu su gabatar da jawabi ta bidiyo bayan hana su Visa da Amurka tayiNajeriya tare da ...
21/09/2025

UNGA: Najeriya ta goyi bayan Falasɗinu su gabatar da jawabi ta bidiyo bayan hana su Visa da Amurka tayi

Najeriya tare da ƙasashe 144 sun kada kuri’a a zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) domin ba wa Shugaban Falasɗinu, Mahmoud Abbas, damar yin jawabi ta bidiyo a babban taron Majalisar bayan Amurka ta ƙi ba da visa ga tawagarsa.

An kada kuri’ar ne a New York, inda aka samu ƙuri’u 145 na amincewa, ƙasashe biyar s**a ƙi (ciki har da Amurka da Isra’ila), yayin da ƙasashe shida s**a kaurace wa kaɗa kuri’ar.

Wannan matakin zai bai wa Abbas damar aiko da jawabin sa da aka riga aka ɗauka ta bidiyo, wanda wani wakilin Falasɗinu a New York zai gabatar a dakin taron. Haka kuma an amince a yi amfani da wannan tsari na jawabin bidiyo ko ta haɗin kai tsaye (live) a wasu muhimman taruka na MDD, amma a abin da ya shafi zaman majasar karo na 80 kawai.

Hon Sani Wakili dan majalisar tarayya na Ungoggo da Minjibir a majalisar tare da Amaryarsa!
20/09/2025

Hon Sani Wakili dan majalisar tarayya na Ungoggo da Minjibir a majalisar tare da Amaryarsa!

DA DUMI-DUMI: Gwamnoni da ministoti da manyan 'yan siyasa sun halarci taron karrama mawaki Rarara da digirin digirgir (D...
20/09/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnoni da ministoti da manyan 'yan siyasa sun halarci taron karrama mawaki Rarara da digirin digirgir (Doctorate Degree) daga jami’ar European American University da ke Jamhuriyar Panama, kan tallata al’adu da zaburar da matasa da yake yi a Najeriya.

20/09/2025

CIKIN BIDIYO YADDA KACHALLA ISYA YA SAKE SAKO MUTUM ARBA'IN DA SUKE GARKUWA DA SU BAYAN SUNYI SULHU DA MUTANEN FASKARI

Jiya juma'a Kachalla Isiya (Kwashen Garwa) ya sake sako mutane 40 ba tare da karban sisin kobo ba, sakamakon sulhu da akayi da su a karamar hukumar Faskari jihar Katsina

Sai dai ya nuna damuwarsa game da harin da jami'an tsaro s**a kaddamar a garin Ruwangodiya da safen jiya juma'a bayan sulhun da akayi

Yace jami'an tsaro sun je garin sun bude wa 'yan uwansa Fulani harma da Hausawa wuta s**a karkashe mutane, yace idan har ba'a bi ka'idar sulhun da akayi aka daina kai masu hari ba, to suma za su karya alkawarin da s**a dauka a koma gidan jiya.

Wasu naga Kamar jami'an tsaron da basu son a zauna lafiya ne s**a kara takalarsu domin sulhu da akai da su ya lalace!

Shin masu karatu ya Luke kallon wannan al'amarin?

Yanzu-yanzu; Ɗan bindiga Isya Kwashen Garwa ya ƙara sako mutane Arba'in 40 ƴan ƙaramar hukumar Faskari bayan an yi zaman...
19/09/2025

Yanzu-yanzu; Ɗan bindiga Isya Kwashen Garwa ya ƙara sako mutane Arba'in 40 ƴan ƙaramar hukumar Faskari bayan an yi zaman sulhu da su

Idan ba'a manta ba dai a ranar Laraba ƴan bindigar sun saki Mutane Talatin 30, wanda idan an haɗa da na yau sun sako mutane Saba'in 70 daidai kenan

Katsina Daily News ta ruwaito cewa Isya Kwashen Garwa ya nuna damuwar shi kan harin da ya zargi sojoji sun kai masu yau a Ruwangodiya daidai lokacin sallar Jumu'ah, inda ya ce muddin aka ci gaba da kashe masu ƴan uwa suma za su tada alƙawari

An Daura Auren Dan Tsohon Gwamnan Kano Mustapha Rabiu KwankwasoDaurin auren, ya gudana a Masallacin Juma'a na, Al Furqan...
19/09/2025

An Daura Auren Dan Tsohon Gwamnan Kano Mustapha Rabiu Kwankwaso

Daurin auren, ya gudana a Masallacin Juma'a na, Al Furqan da ke nan Kano, wanda ya samu halartar dubban mutane.

Gwamna Abba Kabiru Yusuf, da mataimakinsa Aminu Abdussalam Gwarzo, da shugaban majalisar dokokin Kano Jibril Ismail Falgore, duka sun halarci daurin auren.

Haka zalika Sanata Kwankwaso, mahaifin ango Mustpha Rabiu Musa, shima ya halarci daurin auren.

Ango Mustpha Kwankwaso dai ya auri yar gidan Sheikh Tijjani Bala Kalarawi, wato Sayyada Zulaihat.

19/09/2025
19/09/2025

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sauka a jihar Kaduna yau Juma'a domin halattar daurin aure tare da kaddamar da aikin sabunta babban masallacin Sultan Bello dake Kaduna, duk dai a lokacin ziyarar shugaba Tinubu zai ziyarci iyalan tsohon Shugaban Nigeria Marigayi Muhammadu Buhari....

Burkina Faso Ta Yaye Matasa Fararen Hula Kan Sanin Dabarun Kare Kai. Shugaban kasar burkina faso Ibrahim Traore ya yaye ...
19/09/2025

Burkina Faso Ta Yaye Matasa Fararen Hula Kan Sanin Dabarun Kare Kai.

Shugaban kasar burkina faso Ibrahim Traore ya yaye rukunin farko na matasa fararen hula dubu sittin da aka koya masu yadda ake sarrafa b'ndga domin su tun kari masu ikirarin Jhdi dake kokarin kwace iko da kasar.

A halin yanzu shugaban kasar yana da kudirin ganin cewar sama da mutum dubu dari biyar sun samu wannan horo kuma za'a raba masu makamai tare da iznin mallakar su ga masu wannan training din domin zama cikin halin kota kwana a kowanne irin lokaci.

Pantami Ya Karɓi Ziyarar Atiku Abubakar: Sun Tattauna Tattalin Arziƙi, Ilimi da ƘasaTsohon Ministan Sadarwa na Ƙasa, Far...
19/09/2025

Pantami Ya Karɓi Ziyarar Atiku Abubakar: Sun Tattauna Tattalin Arziƙi, Ilimi da Ƙasa

Tsohon Ministan Sadarwa na Ƙasa, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya bayyana cewa daren jiya ya karɓi ziyarar tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugabancin ƙasar a jam’iyyar PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar (GCON), a gidansa dake Abuja.

A cewar Pantami, ziyarar ta mayar da hankali ne kan tattaunawa mai ma’ana game da tattalin arziƙi, ilimi, haɗin kan ƙasa da kuma sha’anin mulki da sauran muhimman batutuwa.

Farfesa Pantami ya kara da cewa shi da iyalinsa sun yi matuƙar farin ciki da ziyarar Atiku Abubakar tare da lokacin da ya dauka a tare da su.

PDP Ta Roki Gwamna Fubara Kada Ya Bar Jam’iyya, Ta Bukaci Ya Tsaya Ya Gina Jihar Ribas SabuwaJam’iyyar PDP ta Lagos ta y...
18/09/2025

PDP Ta Roki Gwamna Fubara Kada Ya Bar Jam’iyya, Ta Bukaci Ya Tsaya Ya Gina Jihar Ribas Sabuwa

Jam’iyyar PDP ta Lagos ta yi kira ga Gwamna Siminalayi Fubara na Jihar Ribas da kada ya bar jam’iyyar, bayan sake dawo da shi ofis daga dakatarwar da aka yi masa tsawon watanni shida.

An dakatar da Fubara tare da ‘yan majalisar dokoki na jiharsa a watan Maris bayan rikicin siyasa da ya kunno kai tsakaninsa da tsohon gwamnan jiharsa, wanda yanzu shi ne Ministan Abuja, Nyesom Wike. Shugaba Bola Tinubu ne ya ayyana dokar ta-baci a jihar, ya nada tsohon hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas, a matsayin Sole Administrator.

Sai dai a ranar Laraba, Shugaba Tinubu ya sanar da kawo karshen dokar ta-bacin, inda ya ba da umarnin a mayar da dukkan zababbun jami’an gwamnati ofis daga Alhamis.

Mataimakin Shugaban PDP na Lagos, Hakeem Olalemi, ya ce Gwamna Fubara ya kamata ya nuna jarumta wajen jagorantar jihar ba tare da tsoro ba, ya kuma yi aiki don sake gina Ribas. Ya bukace shi da ya ci gaba da karfafa jam’iyyar da ta kawo shi mulki.

Olalemi ya kuma shawarci ‘yan siyasar jihar su sanya jama’a gaba don a samu zaman lafiya, ya kuma kira ‘yan majalisar da s**a koma APC su koma PDP domin ci gaban jam’iyyar.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hantsi24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share