Hantsi24

Hantsi24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Hantsi24, Media/News Company, Kano.
(1)

Nijeriya za ta ƙaddamar da sabon tsarin watsa shirye-shiryen talbijin daga analog zuwa dijital a Yuni - IdrisMinistan Ya...
13/05/2026

Nijeriya za ta ƙaddamar da sabon tsarin watsa shirye-shiryen talbijin daga analog zuwa dijital a Yuni - Idris

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa shirin nan da aka daɗe ana jira na sauya tsarin watsa shirye-shiryen talbijin daga analog zuwa dijital (wato Digital Switch Over, DSO) a Nijeriya, an kammala shi tsaf, sai ƙaddamarwa a watan gobe.

Ministan ya bayyana haka ne lokacin da ya kai ziyarar musamman a cibiyoyin aiki na NIGCOMSAT da ke Cibiyar Sararin Samaniya ta Obasanjo a Abuja ranar Laraba.

Da yake bayyana wannan cigaban a matsayin wani muhimmin sauyi a fannin watsa shirye-shirye a Nijeriya, Ministan ya bayyana lamarin da wani babban cigaba a ajandar gyaran da Shugaba Bola Ahmed Tinubu yake yi a fannin yaɗa labarai.

Ya ce: “Ina ganin wannan wata sabuwar alfijir ce ga ƙasar mu. Alƙawarin da Shugaba Tinubu ya yi na gyaran dukkan fannoni yanzu ana ganin yadda ake aiwatar da shi a masana’antar watsa shirye-shiryen talbijin.”

Ya ƙara da cewa bayan shekaru masu yawa ana jinkiri, yanzu Nijeriya ta shirya kammala sauya tsarin daga analog zuwa dijital, yana mai cewa za a ƙaddamar da tsarin na DSO ne a ranar 17 ga Yuni, 2026.

Da yake bayani kan alfanun sabon tsarin, Ministan ya ce: “Wannan zai kawo fa’idoji masu yawa ga gidajen watsa shirye-shirye, masu kallo, da masu talla. Idan ana kallon wata tasha ta musamman, za a san su wanene ke kallo, abin da suke kallo, da kuma yawan masu kallon.”

A cewar sa, sabon tsarin zai samar da ingantattun bayanai da nazarin masu kallo, wanda zai taimaka wa masu talla da gidajen watsa shirye-shirye wajen yanke shawara mai kyau kan shirye-shirye da zuba jari, tare da inganta isar da abubuwan kallo ga ’yan Nijeriya.

Idris ya jaddada tasirin wannan shiri ga tattalin arziki da fasaha, yana mai cewa tsarin zai ƙara haifar da gasa a masana’antar watsa shirye-shirye, ya faɗaɗa damar kallon talbijin kyauta, tare da ɗaga ingancin kallo a Nijeriya da yankin Afrika mai hamadar Sahara.

Ya ce: "An karya tsarin mamayar kamfani guda a fagen. Kowa zai shiga gasa. Abubuwan kallo za su ƙaru, masu kallo za su ƙaru, kuma Nijeriya yanzu tana komawa daga SD zuwa HD wajen watsa shirye-shirye.”

Ya ƙara da cewa yanzu ’yan Nijeriya za su more ingantaccen siginar talbijin ta satalayit, wato tauraron ɗan'adam, da kuma manhajojin wayar hannu da fasahar NIGCOMSAT take samarwa.

A nasa jawabin a yayin ziyarar, Darakta-Janar na Hukumar Kula da Watsa Shirye-shiryen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC), Mista Charles Ebuebu, ya ce an yi sabon tsarin DSO ne domin ya dace da sababbin fasahohi da yadda mutane suke kallon shirye-shirye a wannan zamani.

Ya bayyana cewa sabon tsarin yana amfani da watsa shirye-shiryen satalayit da manhajojin wayar hannu domin tabbatar da cewa jama’a a ko’ina za su iya samun damar amfani da shi, ba kamar tsohon gwajin DSO da ya tsaya a wasu birane kaɗai ba.

Ya ce: “Za mu fara da tashoshi 100 a ranar ƙaddamarwa, ko ma fiye da haka, domin masu samar da abubuwan kallo da dama suna tattaunawa da mu. Muna son samar da kasuwa guda da dandali guda ga Nijeriya.”

Ya bayyana cewa an kafa cibiyoyin samar da shirye-shirye na yankuna daban-daban da cibiyoyin tallafin kwastomomi masu harsuna daban-daban a faɗin ƙasar nan.

Ita ma da take jawabi yayin ziyarar, Manajar Darakta kuma Shugabar NIGCOMSAT, Jane Egerton-Idehen, ta bayyana haɗin gwiwar NIGCOMSAT da NBC a matsayin dabarar haɗin kai mai ƙarfi da ta inganta ayyuka da ɗaga ƙa’idojin aiki a fannin watsa shirye-shiryen dijital a Nijeriya.

A cewar ta, zuba jari da ake ci gaba da yi da kuma shirye-shiryen faɗaɗa ayyukan satalayit a ƙarƙashin wannan gwamnati za su tabbatar da ingantaccen cigaba da bayar da gamsasshen sabis.

Ta ce, “Aikin fa yanzu ne kawai ya fara. Aikin fa yanzu ne kawai ya soma."

Daga cikin waɗanda s**a raka Ministan a ziyarar akwai Darakta Janar na Hukumar Talbijin ta Nijeriya (NTA), Salihu Abdullahi Dembos; Darakta Janar na Muryar Nijeriya (VON), Jibrin Baba Ndace; Darakta Janar na Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Mohammed Bulama, da Darakta Janar na Hukumar Wayar da Kai (NOA), Lanre Issa-Onilu, tare da sauran manyan jami’an gwamnati da manyan baƙi.

ZANGA-ZANGA A TOFA: Matasa Sun Bukaci a Sauya Jobe, Sun Ce “Jobe Must Go”Daga Ahmad RabiuAn samu barkewar zanga-zanga a ...
13/05/2026

ZANGA-ZANGA A TOFA: Matasa Sun Bukaci a Sauya Jobe, Sun Ce “Jobe Must Go”

Daga Ahmad Rabiu

An samu barkewar zanga-zanga a Karamar Hukumar Tofa da ke Jihar Kano, inda wasu matasa s**a fito kan tituna dauke da kwalaye masu dauke da rubutun “Jobe Must Go”, suna kira ga Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, da ya sauya Tijjani Abdulkadir Jobe a matsayin dan takarar kananan hukumomin Dawakin Tofa, Rimin Gado da Tofa.
Rahotanni sun bayyana cewa matasan sun zagaya sassan garin Tofa suna gudanar da zanga-zangar lumana tare da bayyana rashin gamsuwarsu da wakilcin Jobe, wanda s**a ce sun ba shi dama har sau biyar ba tare da ganin wani gagarumin ci gaba a yankin ba.
Da yake zantawa da manema labarai, jagoran zanga-zangar, Kwamaret Uba Sule Tofa, ya ce matasan sun dauki wannan mataki ne domin isar da sakonsu ga gwamnati da jam’iyya, yana mai cewa lokaci ya yi da za a bai wa wani dama domin kawo sauyi.

“Mun zabi Jobe har karo biyar, amma babu abin a zo a gani dangane da ci gaban yankinmu. Wannan ne ya sa muka fito domin a saurare mu,” in ji shi.

A cewarsa, wannan ba shi ne karon farko da ake nuna adawa da Jobe ba, domin tun a baya ma ya fuskanci turjiya daga matasa. Ya kara da cewa a wani taron jam’iyyar APC na karamar hukumar Tofa, matasa sun nuna rashin amincewarsu da shi ta hanyar yi masa ihun “bamayi” a cikin sakatariyar karamar hukumar.

Zanga-zangar dai ta gudana cikin lumana, ba tare da samun rahoton tashin hankali ba, yayin da ake sa ran hukumomi da shugabannin jam’iyya za su dauki matakan da s**a dace domin magance rikicin.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren Tijjani Abdulkadir Jobe ko gwamnatin jihar Kano dangane da lamarin.

Yakamata Shugaban Hukumar Karota Engr. Faisal Mahmud Kabir da Gov. Abba Kabir Yusuf Suyi Duk Iyayinsu Wajan Nemawa Yan K...
13/05/2026

Yakamata Shugaban Hukumar Karota Engr. Faisal Mahmud Kabir da Gov. Abba Kabir Yusuf Suyi Duk Iyayinsu Wajan Nemawa Yan Karota Hanyar Kare Lafiyarsu da Rayukansu.

A Kwana Kwanannan A Dai dai Gadar Lado A Kasamu Gawar Wani Dan Karota Mai Babbar Mota Ya bigeshi ya Gudu.

Yanzu Ga Wannan A Kwance Shima An bugeshi. Aikin Da Sukeyi Akan Tituna Aikine Mai mahimmanci, Idan Babusu Wani in Ance Yayi Yawo Da Mota A Cikin Gari Bazeyi ba. Suma mutanene Kamar kowa, Sunada Yancin da Yakamata Adinga Bimasu Kadin Hakkin Jinanasu da Rayukansu da Ake Salwantarwa.

Ta Fuskar Gogewar Aikin Karota Akwai Bukatar Karin Horo Na Musamman Wajan kara Koyar Dasu Yadda Ake Mu'amala da Kowane Irin Mutun Musamman Direbobi da Yan Private.

ALLAH YASA A GYARA ALLAH YA KIYAYE.

13/05/2026

Kaki ne dakai kaki ne dani.

12/05/2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu Yana Aikin Shimfiɗa T**i A Jihar Kaduna Wanda Zai Taimaka Wajen Sauƙaƙa Harkokin Sufuri A Yankunan: Unguwar Ma'azu, Rigasa, Kurmin-Mashi, Mando, Da Sauransu.

In Ji Rahoton Ƙungiyar Wayar Da Kan Al'umma Ta Ƙasa, Ƙarƙashin Jagorancin Hon. Nuhu Abdullahi.

12/05/2026

Yadda DIG Musa Yusuf Gusau (Ritaya) ya yanki katin zama ɗan jam'iyyar SDP bayan ficewarsa daga ADC

Kuma yayi Alkawalin kawo tsaro matukar ya zama Gwamnan Zamfara a 2027.

Wani tsohon Shugaban APC ya karbo kwangilar tade DSP saboda taimakon dan wata jahar akan takarar Senate President Inji I...
12/05/2026

Wani tsohon Shugaban APC ya karbo kwangilar tade DSP saboda taimakon dan wata jahar akan takarar Senate President Inji Injiya Muaz Magaji Dansarauniya.

Masu Karatu kuna ganin da wanne tsohon shugaban Muaz Magaji yake?

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Mohammad Idris, ya karɓi manyan baƙi ƙarƙashin inuwar ƙungiyar Bida G-10, wadda t...
12/05/2026

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Mohammad Idris, ya karɓi manyan baƙi ƙarƙashin inuwar ƙungiyar Bida G-10, wadda ta ƙunshi fitattun mutane masu tasiri daga Bida.

Sun tattauna muhimman batutuwa waɗanda s**a shafi ci gaba da bunƙasa Jihar Neja.

Ziyarar ta gudana ne a ranar Talata, 12 ga Mayu, 2026.

Fitacciyar 'yar siyasar nan mai amfani kafafen watsa labarai na zamani wato social media dake zama a Saudiyya mai Suna U...
12/05/2026

Fitacciyar 'yar siyasar nan mai amfani kafafen watsa labarai na zamani wato social media dake zama a Saudiyya mai Suna Ummi Ubba Gama wacce take biyayya da tsarin Aci Dadi Lafiya ta koka inda tace "Wai sai yaushe zamu fara cin dadin gwamnatin tamu ne?

12/05/2026

Hon

Dan allah jama'a kuyi watsi da duk wanda zai kawuo muku tallan Peter obi ko waye Inji Ummi Uba Gama.
11/05/2026

Dan allah jama'a kuyi watsi da duk wanda zai kawuo muku tallan Peter obi ko waye Inji Ummi Uba Gama.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hantsi24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share