Jaridar Hausa Reporters

Jaridar Hausa Reporters ... Inganci

RAHOTO:Comrade Yakub Nasir Khalid ya bayyana cewa, Alhassan Doguwa shi ne ɗan siyasar da har yanzu ba shi da kima ko mut...
17/02/2026

RAHOTO:

Comrade Yakub Nasir Khalid ya bayyana cewa, Alhassan Doguwa shi ne ɗan siyasar da har yanzu ba shi da kima ko mutunci a gurin ’yan uwansa ’yan siyasa. Ya ƙara da cewa dun daga lokacin da ya bar mulki, babu wanda zai ƙara jin motsinsa, domin a cewarsa mutane suna tunawa ne da abin alheri ko kuma yadda aka mu’amalanci su.

Hakazalika, Comrade Khalid ya zargi cewa za a tuna da shi ne da abubuwan da ba su dace ba, ciki har da ta’addanci, cin zarafin mutane, da kuma cutar da matasan yankin Tudun Wada da Doguwa ta hanyar hana su damar yin karatu da amfani da jahilcinsu wajen rusa rayuwarsu baki ɗaya.

A ƙarshe, ya bayyana cewa suna barin al’amuransu a hannun Allah, tare da addu’ar Allah Ya isa game da damar yankin da aka lalata.

17 February, 2026

Hon. Bello Aminu B/Ruga, tsohon Mataimakin Shugaban Riko na Gudanarwa na Karamar Hukumar Makoda, ya bayyana matsayinsa t...
30/12/2025

Hon. Bello Aminu B/Ruga, tsohon Mataimakin Shugaban Riko na Gudanarwa na Karamar Hukumar Makoda, ya bayyana matsayinsa tare da Shugabansa da kuma caucus ɗinsu na siyasa, inda s**a jaddada tsayuwarsu daram tare da Jagora Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, Shugaban jagoran Jam’iyyar NNPP na kasa.

A cewarsa, wannan matsaya ta samo asali ne daga gamsuwa da hikima, hangen nesa, da falsafar siyasar Jagoran, wanda ke tafiyar da siyasa bisa adalci da kishin al’umma. Ya ƙara da cewa, su ba za su taɓa cin amanar tafiyar Jagora Kwankwaso ba ko ta wace hanya.

Rahoton ya kuma nuna cewa sun yi addu’ar Allah Ya ci gaba da ba Jagoran jagoranci, hikima, da kariya a dukkan al’amuransa na siyasa da rayuwa.

30/12/2025

Hon. Umar Aliyu Burji, tsohon Interim Vice Chairman na Karamar Hukumar Doguwa kuma Shugaban Ƙungiyar Mataimakan Riko na ...
30/12/2025

Hon. Umar Aliyu Burji, tsohon Interim Vice Chairman na Karamar Hukumar Doguwa kuma Shugaban Ƙungiyar Mataimakan Riko na Kano ta Kudu, ya bayyana goyon bayansa ga Jagora, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, yana mai jaddada cewa wannan matsaya ta fito ne daga zuciya ɗaya da fahimta ta gaskiya.

Ya bayyana hakan ne tare da Shugaban Caucus ɗinsa na Doguwa, Hon. Ukasha Adam Ririwai, inda ya ce ya gamsu ƙwarai da adalcinsu, hangen nesansu, da kuma yadda suke tafiyar da harkokin siyasa cikin gaskiya, rikon amana, da bin doka.

Tare da fatan cewa za a ci gaba da tafiya a wannan tafarki domin amfanin jama’a da ci gaban Kano ta Kudu da Najeriya baki ɗaya.

30/12/2025

Jagoran da ya k**ata ya zama kariya ga jama’a ya juya ya zama barazana garesu; Shin a haka zamu cigaba da rayuwa? By Yak...
05/09/2025

Jagoran da ya k**ata ya zama kariya ga jama’a ya juya ya zama barazana garesu; Shin a haka zamu cigaba da rayuwa?

By Yakub Nasir Khalid

Mutum mai iyali da yara sama da ashirin, amma bai iya tsayawa wajen kare ‘ya’yan al’ummarsa daga yunwa, rashin ilimi, damuwa da lafiyarsu da rashin aikin yi. Tunda ya kasa kare jama’arsa daga wulakanci da samar da abin da ya dace, shin mai yasa ya tsaya tsayin daka wajen kare kansa daga zarge-zargen kisa......?

Jagoran da ya k**ata ya zama kariya ga jama’a ya juya ya zama barazana gare su. Lokacin da ake buƙatar kulawa da ci gaba, ya jefa jama’arsa cikin damuwa da far aba musamman lokutan zabe. Lokacin da ake bukatar shugabanci da adalc, hakan ya tabbatar da cewa shi ba jagora na gari bane.

An zarge shi akan abubuwa da dama da ya k**a ta amasa hukunci akan domin kare alumma daga koma bayan tarbiyya da kuma samun ingantaccen Shugaban a yankin, amma ya Shiga rigar mulki ya buya.

A shekarar 2023 akwai tarin zarge-zargen kisa, kone gidaje, da jefa jama’a cikin rikici sun tabbatar da cewa siyasar sa bata kawo ci gaba ko zaman lafiya bace, illa tashin hankali da rugujewar al’umma yankinmu. Wanda hakan kawo rasa rayuwakan mutane da dama, shin a haka zamu cigaba da rayuwa?

Alhassan ba jagora ba ne, bala’i ne ga jama’a. An zarge shi da kisan kai, tashin hankali da kone ofis, abin kunya da wulakanci. Shugabancinsa kazanta ne da ke rusa alumma, mutum mai irin wannan tabo bai cancanci kujerar jama’a ba.

A 2023 ya shiga hannun jami’an tsaro bisa zargin kisan kai da haɗin baki wajen tada rikici a Tudun Wada. Shugaba na gaskiya da kuma son cigaban alumma bazai bai k**ata a taɓa danganta shi da jinin al’ummarsa ba; tabbas muna bukatar sauyi.

A lokacin yaƙin neman zaɓe a 2022, Doguwa ya ce a fili: “Ranar zabe ko dai ku zabi jam’iyyar APC, ko kuma a yi muku hukunci.” Wannan magana ba siyasa ba ce, barazana ce ga jama’a. Shugaban da ke barazanar jama’arsa ba shugaba ba ne, mai zalunci ne.

Yakub Nasir Khalid
Email: yakubunasirukhalid@gmail

01/09/2025

YANZU-YANZU: Gwamnan jihar Niger, ya sauke dukkanin kwamishinoninsa.

Ba za a sanar da wajen casun shagalin bikin cikar Lamine Yamal shekaru 18 a duniya ba, sai ana sauran kwana biyu shagali...
08/07/2025

Ba za a sanar da wajen casun shagalin bikin cikar Lamine Yamal shekaru 18 a duniya ba, sai ana sauran kwana biyu shagalin bikin. Kuma za a sanarwa waɗanda zasu halarci wajen ne kawai inda za a yi taron.

Sannan kuma matashin ɗan wasan na Barcelona, ya sanya dokar hana shiga da waya wajen casun shagalin bikin na shi.

Daga Fagen Wasanni

Noma: Babban Malamin addinin Musulunci, kuma shugaban majalisar malamai na ƙungiyar Izala a gonar shi dake Jingre, ƙaram...
08/07/2025

Noma: Babban Malamin addinin Musulunci, kuma shugaban majalisar malamai na ƙungiyar Izala a gonar shi dake Jingre, ƙaramar hukumar Bassa dake jihar Filato.

Shin akwai abin koyi a cikin hakan kuwa?

Faɗa akayi ko kuɗin break ne ba'a basu ba? Wa'inda s**ayi Islamiyya ne kaɗai zasu iya chanka 🤣
08/07/2025

Faɗa akayi ko kuɗin break ne ba'a basu ba?

Wa'inda s**ayi Islamiyya ne kaɗai zasu iya chanka 🤣

Akwai yiyuwar samun hatsaniya a zauren Majalisar dattawa a yau tsakanin majalisar da Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya...
08/07/2025

Akwai yiyuwar samun hatsaniya a zauren Majalisar dattawa a yau tsakanin majalisar da Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya, Natasha.

A wani faifen bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta, an hangi Sanata Natasha tana cin alwashin cewa zata halarci zaman zauren majalisa da za'a yi a yau talata.

Sanata Natasha dai har yanzu tana ƙarƙashin hukuncin dakatarwar da kwamitin ladabtarwa na Majilisar dattawan Najeriya s**a yi ma ta. Bisa laifin da s**a kira “Ƙazafi” wa shugaban zauren Majalisar ta dattawa, Sanata Akpabio.

Sanata Natasha dai ta zargi Sanata Akpabio da yunƙurin yin lalata da ita a matakai daban-daban. Hakan ya sanya ta nemi da majalisar ta hukunta shi.

Sai dai kwamitin ladabtarwa na majalisar ya bayyana cewa zarge-zarge na ta basu da tushe.

Akwai yiwuwar samun hatsaniya a zauren Majalisar matuƙar Sanata Natasha bata janye alwashin ta na halartar zauren Majalisar ba a yau.

Menene ra'ayin ku akan wannan alwashi na Sanata Natasha?

Daga zuwan ADC abu uku s**a faru.1. Anfara meeting din sauke farashin fetur.2. Da kotu taki yarda da karan Natasha jiya ...
08/07/2025

Daga zuwan ADC abu uku s**a faru.

1. Anfara meeting din sauke farashin fetur.

2. Da kotu taki yarda da karan Natasha jiya kuma ance hukuncin da majalisa tayi akan ta yayi tsauri.

3. Yanzu kuma wike yayarda zai biya Malaman makarantun Abuja minimum wage dakuma Albashin su na 3 months daya hanasu.

ADC wuya!!! koyanzu tayi rana wa talakawan Najeriya.....

Ra'ayin Muhammad Abu Sultan Jos

Da Ɗumi-Ɗumi: Fiye da Ƴan Sa-kai 70 Sun Rasa Rayukansu a Fada da Ƴan B|ndiga a Kanam, Jihar Filato.Aƙalla ƴan sa-kai 70 ...
08/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi: Fiye da Ƴan Sa-kai 70 Sun Rasa Rayukansu a Fada da Ƴan B|ndiga a Kanam, Jihar Filato.

Aƙalla ƴan sa-kai 70 ne aka tabbatar da mutuwarsu a wani mummunan h4ri da ƴan b|ndiga s**a kai a yankunan Kukawa da Bunyun da ke ƙaramar hukumar Kanam, a jihar Filato. Wannan h4rin da ya girgiza al’umma ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na ranar Litinin 7 ga watan yuli 2025, Inda aka ce ƴan sa-kai daga ƙaramar hukumar Wase suna kan hanyarsu ta kai farmaki kan mafakar ƴan b|ndiga kafin su faɗa cikin kwanton-baunar ƴan b|ndigan.

Aliyu Baffa, Shugaban rundunar ƴan sa-kai na Kukawa, ya bayyana cewa:

> “Fiye da ƴan sa-kai 70 ne aka ka$he a wannan h4ri. Har yanzu ana ci gaba da neman wasu gawarwakin a dazuka da gonaki. Bazamu taɓa iya mantawa da wannan abun ba.”

A cewarsa, Lamarin ya faru ne kimanin kilomita ɗaya daga garin Kukawa, A hanyarsu ta zuwa wata mafakar ƴan bindiga da ke cikin dajin gwamnati da ake kira Madam Forest, Wanda ke iyaka da jihohin Bauchi da Taraba. Wannan daji dai an daɗe ana kallonsa a matsayin mafaka ta manyan ƙungiyoyin ƴan ta’4dda.

Baffa ya ƙara da cewa bayan fadan, An gano gawarwakin wasu daga cikin ƴan sa-kai a gonaki daban-daban.

> “Mun binne fiye da mutum 60 a Kukawa kawai. Muna da tabbacin cewa har yanzu akwai gawarwaki a cikin daji. Wasu daga cikin ƴan b|ndigar da s**a tsira sun bayyana cewar sun ci galabar wannan yaƙ|n, Lamarin da ya ƙara nuna girman harin,” in ji shi.

A wani ɓangare na rahoton, Musa Ibrahim, Mazaunin ƙauyen Bunyun da ke cikin gundumar Nyalun, ƙaramar hukumar Wase, Ya bayyana cewa ƴan b|ndigar sun kai h4ri kan ƙauyensu inda s**a ka$he ƴan sa-kai goma da ke kan bakin aiki a yankin.

> “Sun ƙ0ne gidaje da dama, Sun kuma tayar da hankalin al’umma. Mutane da yawa sun tsere zuwa dazuka domin tsira da rayukansu,” in ji Musa cikin damuwa.

Rahotanni daga yankin na nuna cewa jama’a na cikin firgici da fargaba, Yayin da ake ci gaba da bin sahun ƴan b|ndigar da s**a tsere daga wajen harin.

Hukumomi dai na ci gaba da bincike da ƙoƙarin dawo da zaman lafiya a yankin, Sai dai al’umma na kira da a kawo ɗauki cikin gaggawa domin daƙile irin wannan rikicin mai nasaba da rashin tsaro.

Allah ya kyauta! 🤲🏻

— Faisal Sadauki

Ra'ayi: Idan kinsan ke kyakkwawa ce karki sake ki auri talaka ya dinga ciyar dake da shinkafa da mai da yaji ki lalace d...
08/07/2025

Ra'ayi: Idan kinsan ke kyakkwawa ce karki sake ki auri talaka ya dinga ciyar dake da shinkafa da mai da yaji ki lalace duk ki tsofa 🤌🙈

Shawara Kyauta 😎🚶‍➡️

Daga Musa Lawan Ɗan Iya

Address

Kano

Telephone

+2349035856764

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Hausa Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Hausa Reporters:

Share