Jaridar Hausa Reporters

  • Home
  • Jaridar Hausa Reporters

Jaridar Hausa Reporters ... Inganci

Ba za a sanar da wajen casun shagalin bikin cikar Lamine Yamal shekaru 18 a duniya ba, sai ana sauran kwana biyu shagali...
08/07/2025

Ba za a sanar da wajen casun shagalin bikin cikar Lamine Yamal shekaru 18 a duniya ba, sai ana sauran kwana biyu shagalin bikin. Kuma za a sanarwa waɗanda zasu halarci wajen ne kawai inda za a yi taron.

Sannan kuma matashin ɗan wasan na Barcelona, ya sanya dokar hana shiga da waya wajen casun shagalin bikin na shi.

Daga Fagen Wasanni

Noma: Babban Malamin addinin Musulunci, kuma shugaban majalisar malamai na ƙungiyar Izala a gonar shi dake Jingre, ƙaram...
08/07/2025

Noma: Babban Malamin addinin Musulunci, kuma shugaban majalisar malamai na ƙungiyar Izala a gonar shi dake Jingre, ƙaramar hukumar Bassa dake jihar Filato.

Shin akwai abin koyi a cikin hakan kuwa?

Faɗa akayi ko kuɗin break ne ba'a basu ba? Wa'inda s**ayi Islamiyya ne kaɗai zasu iya chanka 🤣
08/07/2025

Faɗa akayi ko kuɗin break ne ba'a basu ba?

Wa'inda s**ayi Islamiyya ne kaɗai zasu iya chanka 🤣

Akwai yiyuwar samun hatsaniya a zauren Majalisar dattawa a yau tsakanin majalisar da Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya...
08/07/2025

Akwai yiyuwar samun hatsaniya a zauren Majalisar dattawa a yau tsakanin majalisar da Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya, Natasha.

A wani faifen bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta, an hangi Sanata Natasha tana cin alwashin cewa zata halarci zaman zauren majalisa da za'a yi a yau talata.

Sanata Natasha dai har yanzu tana ƙarƙashin hukuncin dakatarwar da kwamitin ladabtarwa na Majilisar dattawan Najeriya s**a yi ma ta. Bisa laifin da s**a kira “Ƙazafi” wa shugaban zauren Majalisar ta dattawa, Sanata Akpabio.

Sanata Natasha dai ta zargi Sanata Akpabio da yunƙurin yin lalata da ita a matakai daban-daban. Hakan ya sanya ta nemi da majalisar ta hukunta shi.

Sai dai kwamitin ladabtarwa na majalisar ya bayyana cewa zarge-zarge na ta basu da tushe.

Akwai yiwuwar samun hatsaniya a zauren Majalisar matuƙar Sanata Natasha bata janye alwashin ta na halartar zauren Majalisar ba a yau.

Menene ra'ayin ku akan wannan alwashi na Sanata Natasha?

Daga zuwan ADC abu uku s**a faru.1. Anfara meeting din sauke farashin fetur.2. Da kotu taki yarda da karan Natasha jiya ...
08/07/2025

Daga zuwan ADC abu uku s**a faru.

1. Anfara meeting din sauke farashin fetur.

2. Da kotu taki yarda da karan Natasha jiya kuma ance hukuncin da majalisa tayi akan ta yayi tsauri.

3. Yanzu kuma wike yayarda zai biya Malaman makarantun Abuja minimum wage dakuma Albashin su na 3 months daya hanasu.

ADC wuya!!! koyanzu tayi rana wa talakawan Najeriya.....

Ra'ayin Muhammad Abu Sultan Jos

Da Ɗumi-Ɗumi: Fiye da Ƴan Sa-kai 70 Sun Rasa Rayukansu a Fada da Ƴan B|ndiga a Kanam, Jihar Filato.Aƙalla ƴan sa-kai 70 ...
08/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi: Fiye da Ƴan Sa-kai 70 Sun Rasa Rayukansu a Fada da Ƴan B|ndiga a Kanam, Jihar Filato.

Aƙalla ƴan sa-kai 70 ne aka tabbatar da mutuwarsu a wani mummunan h4ri da ƴan b|ndiga s**a kai a yankunan Kukawa da Bunyun da ke ƙaramar hukumar Kanam, a jihar Filato. Wannan h4rin da ya girgiza al’umma ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na ranar Litinin 7 ga watan yuli 2025, Inda aka ce ƴan sa-kai daga ƙaramar hukumar Wase suna kan hanyarsu ta kai farmaki kan mafakar ƴan b|ndiga kafin su faɗa cikin kwanton-baunar ƴan b|ndigan.

Aliyu Baffa, Shugaban rundunar ƴan sa-kai na Kukawa, ya bayyana cewa:

> “Fiye da ƴan sa-kai 70 ne aka ka$he a wannan h4ri. Har yanzu ana ci gaba da neman wasu gawarwakin a dazuka da gonaki. Bazamu taɓa iya mantawa da wannan abun ba.”

A cewarsa, Lamarin ya faru ne kimanin kilomita ɗaya daga garin Kukawa, A hanyarsu ta zuwa wata mafakar ƴan bindiga da ke cikin dajin gwamnati da ake kira Madam Forest, Wanda ke iyaka da jihohin Bauchi da Taraba. Wannan daji dai an daɗe ana kallonsa a matsayin mafaka ta manyan ƙungiyoyin ƴan ta’4dda.

Baffa ya ƙara da cewa bayan fadan, An gano gawarwakin wasu daga cikin ƴan sa-kai a gonaki daban-daban.

> “Mun binne fiye da mutum 60 a Kukawa kawai. Muna da tabbacin cewa har yanzu akwai gawarwaki a cikin daji. Wasu daga cikin ƴan b|ndigar da s**a tsira sun bayyana cewar sun ci galabar wannan yaƙ|n, Lamarin da ya ƙara nuna girman harin,” in ji shi.

A wani ɓangare na rahoton, Musa Ibrahim, Mazaunin ƙauyen Bunyun da ke cikin gundumar Nyalun, ƙaramar hukumar Wase, Ya bayyana cewa ƴan b|ndigar sun kai h4ri kan ƙauyensu inda s**a ka$he ƴan sa-kai goma da ke kan bakin aiki a yankin.

> “Sun ƙ0ne gidaje da dama, Sun kuma tayar da hankalin al’umma. Mutane da yawa sun tsere zuwa dazuka domin tsira da rayukansu,” in ji Musa cikin damuwa.

Rahotanni daga yankin na nuna cewa jama’a na cikin firgici da fargaba, Yayin da ake ci gaba da bin sahun ƴan b|ndigar da s**a tsere daga wajen harin.

Hukumomi dai na ci gaba da bincike da ƙoƙarin dawo da zaman lafiya a yankin, Sai dai al’umma na kira da a kawo ɗauki cikin gaggawa domin daƙile irin wannan rikicin mai nasaba da rashin tsaro.

Allah ya kyauta! 🤲🏻

— Faisal Sadauki

Ra'ayi: Idan kinsan ke kyakkwawa ce karki sake ki auri talaka ya dinga ciyar dake da shinkafa da mai da yaji ki lalace d...
08/07/2025

Ra'ayi: Idan kinsan ke kyakkwawa ce karki sake ki auri talaka ya dinga ciyar dake da shinkafa da mai da yaji ki lalace duk ki tsofa 🤌🙈

Shawara Kyauta 😎🚶‍➡️

Daga Musa Lawan Ɗan Iya

Jami'o'in tarayya a Najeriya wa'inda suke bin bashin albashi watan da ya gabata suna barazanar tsunduma yajin aikin sai-...
08/07/2025

Jami'o'in tarayya a Najeriya wa'inda suke bin bashin albashi watan da ya gabata suna barazanar tsunduma yajin aikin sai-baba-ta-gani matuƙar Gwamnatin tarayya bata biya su ba.

Ƙungiyar malam jami'o'i, wato ASUU a turance kuma a taƙaice, itace tayi wannan barazanar. A yayin da rassanta na jami'o'i kamar Jami'ar Jos ta jami'ar Abubakar Tafawa dake Bauchi, tuni s**a shiga yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyu, tare ta jan kunnen Gwamnatin tarayya da ta guji jinkirta albashin na su na watanni masu zuwa.

Sunayen motoci da Hausa:1. A-kori-kura2. Bilhodi 3. Hajiya-ba-ɗuwawu4. Shiga-da-alwalar-ka5. Ladan-ɗan-boko6. Astin 7. S...
08/07/2025

Sunayen motoci da Hausa:

1. A-kori-kura

2. Bilhodi

3. Hajiya-ba-ɗuwawu

4. Shiga-da-alwalar-ka

5. Ladan-ɗan-boko

6. Astin

7. Shorido

9. Tan-tan

10. Kiya-kiya

11. Bana-ba-harka

12. Rumfar-jaki

13. Titiri

14. Mandisil

15. Hayis

16. Ayon

17. Balbo

18. Pijo

19. Fanda-akod

20. Marsandi

21. Mai-jin kunyar talaka

22. Makafolo

23. Katafila

24. Tangul

25. Tan-goma

26. Singul

27. Boksa

28. Bokswajen

29. Tifa

30. Gireda

31. Hayundi

32. Fasledi

A cikin su, wacce ka sani, kuma wacce ce ban lissafo ba?

Wata ƙungiyar matasa a garin Jos mai suna ARRYNA ta ƙaddamar da hamshaƙin taron rufe gasa tsakanin makarantu a garin Jos...
07/07/2025

Wata ƙungiyar matasa a garin Jos mai suna ARRYNA ta ƙaddamar da hamshaƙin taron rufe gasa tsakanin makarantu a garin Jos a jiya kamar yadda da sabayi duk shekara.

Ɗan majalisan jiha mai wakiltar Arewacin Jow ta arewa a majalisar jihar Filato, Adamu Aliyu ya gwangwaje gwarzuwar gasar da tallafin karatu kyauta har zuwa kammala jami'a.

Shugaban ƙungiyar, Harisu Babando ya bayyana jin daɗin shi da miƙa godiya ga ɗan majalisar bisa wannan babban tallafi da ya yi.

Wace ƙungiyar matasa kuke da shi a yankin ku?

07/07/2025

Barka da safiya

Da me ku ka karya yau? 😊

Bisa jajircewar shi a wannan yunƙurin haɗin gwiwar jam'iyyun, wani matsayi ne kuke ganin ya dace da Malam Nasiru El-rufa...
07/07/2025

Bisa jajircewar shi a wannan yunƙurin haɗin gwiwar jam'iyyun, wani matsayi ne kuke ganin ya dace da Malam Nasiru El-rufa'i idan haƙarsu da cimma ruwa daga ƙarshe?

Address


Telephone

+2349035856764

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Hausa Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Hausa Reporters:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share