Madina Hausa TV

Madina Hausa TV Madina Hausa kafa ce ta yaɗa labarai wadda ke kawo muku sahihan labaran duniya da harshen Hausa.
(1)

Ba mu tsaya a labarai kaɗai ba, muna kuma kawo muku hirarraki da fitattun ‘yan jarida da kuma matasan da suka yi fice a fannoni daban-daban na fasaha.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya ce ya kammala dukkan shirye-shiryen tsaro domin bukuku...
22/12/2025

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya ce ya kammala dukkan shirye-shiryen tsaro domin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara a fadin jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta Kano, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar a yau Litinin.

Sanarwar ta bayyana cewa Kwamishinan ya gudanar da muhimmin taron tsaro da manyan jami’an rundunar, bisa umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, IGP Kayode Egbetokun, domin tabbatar da zaman lafiya a lokacin bukukuwan.

A taron, CP Bakori ya umarci jami’an da su ƙara yawan sintiri, su tabbatar da ganin ’yan sanda a fili, tare da ƙarfafa tsaro a wuraren ibada, wuraren shakatawa da manyan tituna.

Rundunar ta kuma gargaɗi jama’a da su guji tuki cikin ganganci da sauran ayyukan da ka iya tayar da hankalin jama’a.

An bukaci al’umma da su kai rahoton duk wani abu da suke zargi ga ofishin ’yan sanda mafi kusa ko ta lambobin gaggawa da aka tanada.

Kwamishinan ya gode wa al’ummar Kano bisa haɗin kai, tare da yi musu fatan bikin Kirsimeti lafiya lau da sabuwar shekara mai albarka.

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ayyana ranar Alhamis 25 ga watan Disamba da ranar Juma’a 26 ga watan a matsayin r...
22/12/2025

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ayyana ranar Alhamis 25 ga watan Disamba da ranar Juma’a 26 ga watan a matsayin ranakun hutun Kirsimeti.

Haka kuma, an ayyana ranar Alhamis 1 ga watan Janairu, 2026 a matsayin hutun bikin Sabuwar Shekara.

Matatar mai ta Dangote ta buƙaci ƴan kasar nan da su rika kai rahoton duk wani gidan man MRS da ke sayar da man fetur a ...
22/12/2025

Matatar mai ta Dangote ta buƙaci ƴan kasar nan da su rika kai rahoton duk wani gidan man MRS da ke sayar da man fetur a farashin da ya haura Naira 739 akan kowacce lita.

Wannan na zuwa ne bayan da matatar man ta bayyana cewa ta fara sayar da fetur a kasar nan kan farashin Naira 739 kowacce lita a dukkanin tashoshin MRS Oil Nigeria Plc.

A sanarwar da matatar Dangoten ta fitar a jiya Lahadi,ta bayyana cewa rage farashin fetur wata muhimmiyar nasara ce a burinta na samar da mai cikin saukin farashi ga yan Najeriya da daidaita harkokin kasuwar man fetur.

Matatar ta kuma ce fiye da gidajen mai 2,000 na MRS a fadin kasar nan, ana sa ran wannan sabon farashi zai fara aiki a dukkanin cibiyoyinsa, domin al’umma a ko’ina su amfana da wannan ragi.

Matatar ta yaba wa ƴan kasuwar da s**a rungumi sabon tsari, sannan ta shawarci sauran da su bi sahu domin farfadowar tattalin arzikin kasa.

Dakarun Soji na Operation HADIN KAI sun kashe ƴan ta’adda 17 tare da ƙwato kayayyakin amfani da ake musu jigila a wani k...
22/12/2025

Dakarun Soji na Operation HADIN KAI sun kashe ƴan ta’adda 17 tare da ƙwato kayayyakin amfani da ake musu jigila a wani kwanton bauna da s**a yi musu a Jihar Borno.

Wannan na cikin sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Operation HADIN KAI, Lieutenant Colonel Sani Uba, ya fitar a ranar Lahadi 21 ga Disamba 2025.

Sanarwar ta ce sojojin sun yi kwanton baunar ne tare da haɗin gwiwar Civilian JTF da mafarauta, bayan samun bayanan sirri kan yunƙurin jigilar kayayyaki ga ƴan ta’addar ISWAP tsakanin ƙauyukan Sojiri da Kayamla.

A yayin musayar wuta, sojojin sun kashe ƴan ta’adda 17, yayin da wasu s**a tsere da raunukan harbi, tare da ƙwato kekuna, kayan abinci, magunguna, kayan sawa, tayoyin keke, fitilun hannu, mak**ai da alburusai, da sauran kayayyakin da ake zargin an tanade su ne don tallafa wa ƴan ta’adda.

CAF ta ƙaddamar da sabuwar gasar African Nations League Hukumar Kwallon Ƙafa ta Afirka (CAF) ta sanar da ƙaddamar da sab...
22/12/2025

CAF ta ƙaddamar da sabuwar gasar African Nations League

Hukumar Kwallon Ƙafa ta Afirka (CAF) ta sanar da ƙaddamar da sabuwar gasa mai suna African Nations League, wadda za a riƙa gudanarwa duk shekara, domin nuna ƙwarewar manyan ƙungiyoyin ƙasa da fitattun ‘yan wasan Afirka.

CAF ta bayyana cewa wannan gasar za ta samar da dandalin gasa mai inganci na duniya ga ƙungiyoyin ƙasa na manya, tare da ba wa ‘yan wasan Afirka damar samun ƙarin ficewa da nuna basirarsu a matakin nahiyar.

A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X a ranar Litinin, CAF ta ce, ta ƙaddamar da sabuwar gasar African Nations League mai armashi, kuma ta tabbatar da cewa za ta riƙa shirya gasar ƙungiyoyin ƙasa ta manya a kowace shekara, inda mafi kyawun ‘yan wasan Afirka za su halarta.

Manufar wannan shiri ita ce ƙarfafa kwallon ƙafar Afirka ta hanyar samar da wasanni da bunƙasa ci gaban ‘yan wasa, da kuma ƙara jan hankalin masoya kwallo a faɗin nahiyar.

Jaridar punch ta rawaito cewa za a fara gudanar da Gasar Kofin Ƙasashen Afirka (AFCON) duk bayan shekara huɗu, bayan gasar da aka shirya yi a 2028.

kano pillars ta zamu nasara akan plateau da ci 2-1
21/12/2025

kano pillars ta zamu nasara akan plateau da ci 2-1

Barcelona ta samu nasara da ci 2– 0 a kan Villarreal, Raphinha da Lamine Yamal ne s**a zura ƙwallayen da s**a ba Barcelo...
21/12/2025

Barcelona ta samu nasara da ci 2– 0 a kan Villarreal, Raphinha da Lamine Yamal ne s**a zura ƙwallayen da s**a ba Barcelona wannan nasara.

Cikin Hotunan:Yadda Shugaban ƙasa  Bola Tinubu yaje ta’aziyya ga iyalan Marigayi Sheikh Dahiru Bauchi a jihar Bauchi ran...
21/12/2025

Cikin Hotunan:
Yadda Shugaban ƙasa Bola Tinubu yaje ta’aziyya ga iyalan Marigayi Sheikh Dahiru Bauchi a jihar Bauchi ranar Asabar.

📸 - Sunday Dare/Bala Mohammed

Jam’iyyar NNPP ɓangare Sanata Mas’ud Doguwa sun yi watsi da babban taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, tana mai cewa...
21/12/2025

Jam’iyyar NNPP ɓangare Sanata Mas’ud Doguwa sun yi watsi da babban taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, tana mai cewa ba halastacce ba ne.

Shugabancin jam'iyyar NNPP na Kano ɓangaren, Sanata Mas’ud Doguwa, sun ce taron bai bi doka ba, kuma ba a gayyaci dukkan ɓangarorin jam’iyyar ba.

Ya ce kafin a yi kowanne taron ƙasa, dole ne a fara sulhu domin samar da haɗin kai a jam’iyyar.

Sanatan ya kuma ce ba lokaci ba ne na goyon bayan ’yan takara gabanin zaɓen 2027.

Wannan rikici na zuwa ne bayan ɓangaren Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso sun sake zaɓen shugabannin jam’iyyar NNPP a taron Abuja k**ar yadda jaridar punch ta ruwaito.

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da kashe Naira Biliyan 38.7 domin manyan ayyukan raya ƙasa bayan ...
21/12/2025

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da kashe Naira Biliyan 38.7 domin manyan ayyukan raya ƙasa bayan taron Majalisar Zartarwa karo na 35.

Kuɗaɗen za su shafi ilimi, tsaro, kiwon lafiya, hanyoyi da samar da ruwa. A fannin ilimi, an ware Naira Biliyan 3.77 don biyan basuss**a, gyaran makarantu, sayen kayan makaranta da gina ajujuwa a kananan hukumomi 44.

A bangaren tsaro da kiwon lafiya, za a sayi babura 300 domin sintirin unguwanni, tare da kashe Naira Biliyan 6.81 don gyaran cibiyoyin lafiya da biyan diyya ga mutane 5,015 a Rimin Zakara.

Haka kuma, an amince da kashe Naira Biliyan 26.1 don gina hanyoyi da ayyukan ruwa, ciki har da manyan tituna da gyaran madatsun ruwa, domin inganta zirga-zirga, samar da ruwa da bunƙasar tattalin arzikin jihar Kano.

Kungiyar SERAP ta roƙi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da ya umarci Antoni Janar na ƙasa ya wallafa sahihan kwafen dokokin har...
21/12/2025

Kungiyar SERAP ta roƙi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da ya umarci Antoni Janar na ƙasa ya wallafa sahihan kwafen dokokin haraji da Majalisar Ƙasa ta amince da su.

SERAP ta ce hakan ya zama dole sak**akon zargin cewa an sauya wasu sassan dokokin kafin a fitar da su a hukumance.

Kungiyar ta kuma nemi a kafa kwamitin bincike mai zaman kansa domin gano gaskiya, tare da gargaɗin cewa za ta ɗauki matakin shari’a idan ba a bi buƙatarta ba k**ar yadda jaridar punch ta ruwaito.

Amurka da Najeriya sun sanya hannu kan yarjejeniyar lafiya ta shekaru biyar, wadda kudinta ya kai kusan dala biliyan biy...
21/12/2025

Amurka da Najeriya sun sanya hannu kan yarjejeniyar lafiya ta shekaru biyar, wadda kudinta ya kai kusan dala biliyan biyu da miliyan ɗari, domin ƙarfafa tsarin kiwon lafiya a Najeriya.

Yarjejeniyar za ta tallafa wa yaƙi da cututtuka k**ar HIV, tarin fuka, zazzabin cizon sauro, da lafiyar uwa da jariri, tare da ba da muhimmanci ga cibiyoyin lafiya na addini.

Najeriya ma za ta ƙara kashe kusan dala biliyan uku, yayin da Amurka ta ce yarjejeniyar za ta taimaka wajen bunƙasa ayyukan lafiya a ƙasar k**a yadda jaridar punch ta ruwaito.

Address

Kano
Kano

Telephone

+2348177352017

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Madina Hausa TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Madina Hausa TV:

Share