Sarauniya TV

Sarauniya TV 🤫🤫🤫🤫🤫👊
(2)

16/05/2026
Gabon Ta Ce 'Yar Siyasa Ce Ita 😂👇Ku Yi Following Ɗin Jaridar Idon Mikiya Don Samun Ingantattun Labarai Masu Ƙayatarwa 👇👇...
14/05/2026

Gabon Ta Ce 'Yar Siyasa Ce Ita 😂👇
Ku Yi Following Ɗin Jaridar Idon Mikiya Don Samun Ingantattun Labarai Masu Ƙayatarwa 👇👇👇

Jarumar masana'antar Kannywood, Hadiza Aliyu Gabon, ta bayyana cewa ta na yin siyasa, amma mutum take yi ba jam'iyya ba.

Ta Rasu a Hanyarta Ta Zuwa Filin Jirgin Sama Domin Gudanar Da Aikin Hajjin BanaRahotanni sun bayyana rasuwar Sadiya Isma...
13/05/2026

Ta Rasu a Hanyarta Ta Zuwa Filin Jirgin Sama Domin Gudanar Da Aikin Hajjin Bana

Rahotanni sun bayyana rasuwar Sadiya Ismail Uba, wadda ta kammala digiri a fannin Medical Microbiology a watan da ya gabata, bayan wani mummunan haɗarin mota da ya rutsa da ita a hanyarta ta zuwa Damaturu domin wucewa filin jirgin sama na Muhammadu Buhari dake Maiduguri zuwa ƙasa mai tsarki domin aikin Hajjin bana.

Majiyoyi sun ce an shirya aurenta ne a watan Janairun 2027, yayin da kuma take shirin tafiya Saudiyya a mako mai zuwa kafin ajalinta ya zo.

Allah Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata, Ya sanya Aljanna ce makomarta. Ameen.

Idon Mikiya

Babbar Kotun Tarayya ta yanke wa tsohon Ministan Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75 a gidan yari bayan s...
13/05/2026

Babbar Kotun Tarayya ta yanke wa tsohon Ministan Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75 a gidan yari bayan samun sa da laifin almundahanar kuɗi sama da naira biliyan 33.

Kotun ta bayyana cewa an same shi da hannu a badakalar kuɗaɗe da ta faru lokacin da yake riƙe da muƙamin minista a gwamnatin tsohon shugaban ƙasa marigayi Buhari.

Idon Mikiya

Sojoji Sun Jefawa Kasuwar Zamfara Bam, Mutane 117 Sun MutuAƙalla mutane 117 ciki har da 'yan mata masu tallar awara da ’...
13/05/2026

Sojoji Sun Jefawa Kasuwar Zamfara Bam, Mutane 117 Sun Mutu

Aƙalla mutane 117 ciki har da 'yan mata masu tallar awara da ’yan kasuwa sun mutu sakamakon harin bam da sojoji s**a kai a kasuwar Tumfa da ke ƙaramar hukumar Zurmi a jihar Zamfara.

Rahotanni sun ce ’yan bindiga sun mamaye kasuwar lamarin da ya sa ba a iya bambance su da fararen hula ba kafin kai harin.

An ce harin ya faru ne a ranar Lahadi, ranar da aka kuma kai wani harin bam a kauyen Guradnayi da ke kusa da Kusasu a jihar Neja, inda fararen hula 13 s**a rasa rayukansu.

Idon Mikiya

-------------------
TĀLLĀ: Dama ce ta musamman ga masu sha'awar fara kasuwancin data, ko sanya wa kan su, ku Sauke Application na KSBDATA daga ‘Playstore’ zuwa kan wayoyin ku yanzu ku mori Data da kati ‘Airtime’ mafi arha. 👇👇

Ku dauba sashen comment👇

Museveni Ya Sake Lashe Mulkin Uganda Karo Na Bakwai (7)An rantsar da Shugaba Yoweri Museveni na Uganda karo na bakwai ba...
13/05/2026

Museveni Ya Sake Lashe Mulkin Uganda Karo Na Bakwai (7)

An rantsar da Shugaba Yoweri Museveni na Uganda karo na bakwai bayan ya yi nasara a zaɓen Janairun 2026, inda ya doke babban abokin hamayyarsa, Bobi Wine.

Idon Mikiya

------------------------
TĀLLĀ: Dama ce ta musamman ga masu sha'awar fara kasuwancin data, ko sanya wa kan su, ku Sauke Application na KSBDATA daga ‘Playstore’ zuwa kan wayoyin ku yanzu ku mori Data da kati ‘Airtime’ mafi arha. 👇👇

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp 👇👇

https://wa.me/2349018986971

An Fara Sanya Tsofaffin ‘Yan Ta’adda Yin Rantsuwa Da Alƙur’ani Kafin Komawa Cikin Al’umma a BornoGwamnatin Borno ta ce a...
13/05/2026

An Fara Sanya Tsofaffin ‘Yan Ta’adda Yin Rantsuwa Da Alƙur’ani Kafin Komawa Cikin Al’umma a Borno

Gwamnatin Borno ta ce ana sanya ‘yan ta’addan da s**a tuba yin rantsuwa da Alƙur’ani kafin a mayar da su cikin al’umma, domin tabbatar da ba za su koma ta’addanci ba. Kwamishiniyar hakokin mata da cigaban al'umma ta jihar, Haj. Zuwaira Gambo ta ce wannan na daga cikin tsarin gyaran hali da kawar da tsattsauran ra’ayi a jihar.

Idon Mikiya

-----------------------
TĀLLĀ: Dama ce ta musamman ga masu sha'awar fara kasuwancin data, ko sanya wa kan su, ku Sauke Application na KSBDATA daga ‘Playstore’ zuwa kan wayoyin ku yanzu ku mori Data da kati ‘Airtime’ mafi arha. 👇👇

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp 👇👇

https://wa.me/2349018986971

TĀLLĀ: Ku Sāyā Data Mafi Inganci Da Arha A Wurin MuIdan kuka fara amfani da kamfanin  kasuwancin DATA da katin waya na K...
13/05/2026

TĀLLĀ: Ku Sāyā Data Mafi Inganci Da Arha A Wurin Mu

Idan kuka fara amfani da kamfanin kasuwancin DATA da katin waya na KSBDATA ba za ku sake amfani da wani kamfanin ba.

Ina masu sana'ar data da katin waya? ga dama ta samu, KSBDATA mun shirya ba ku rìbà mai yawa, zaku iya siyan DATA ku sakawa kanku da wannan Application ɗin namu na KSBDATA, muddin kuka fara amfani da KSBDATA ba za ku iya dainawa ba saboda ingancin datarmu.

Ku sauke “Application” ɗinmu na KSBDATA a “Playstore” zuwa kan wayoyinku.👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp👇
https://wa.me/2349018986971

Atiku Ya Caccaki Matakan Tsaron Tinubu Bayan Rasuwar Tsohon Dan Majalisa a Hannun ’Yan BindigaTsohon Mataimakin Shugaban...
12/05/2026

Atiku Ya Caccaki Matakan Tsaron Tinubu Bayan Rasuwar Tsohon Dan Majalisa a Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya caccaki matakan tsaron gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bayan rasuwar tsohon ɗan Majalisar Wakilai, Hon. Abba Adamu, a hannun masu garkuwa da mutane.

Rahotanni sun bayyana cewa an sace marigayin ne a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna a ranar 3 ga watan Mayu, sannan ya rasu bayan kwana tara yana hannun ’yan bindiga duk da ƙoƙarin da iyalansa s**a yi na ganin an sake shi.

A cikin wata sanarwa da Babban Mataimakinsa na Musamman kan Hulɗa da Jama’a, Phrank Shaibu, ya fitar a Abuja, Atiku ya bayyana lamarin a matsayin wata babbar alama da ke nuna yadda matsalar rashin tsaro ke ƙara ta’azzara a Najeriya.

Ya ce ci gaba da kashe-kashe da sace mutane na nuna cewa gwamnati ta gaza kare rayuka da dukiyoyin al’umma, yana mai kira ga gwamnatin tarayya da ta ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalar tsaro a ƙasar.

Na Ƙi Shiga ADC Ne Gudun Kar Tinubu Ya Jefa Mana Bam Mu Mutu Gaba Daya, Cewar Buba GaladimaFitaccen ɗan siyasa a Najeriy...
12/05/2026

Na Ƙi Shiga ADC Ne Gudun Kar Tinubu Ya Jefa Mana Bam Mu Mutu Gaba Daya, Cewar Buba Galadima

Fitaccen ɗan siyasa a Najeriya, Alhaji Buba Galadima, ya bayyana cewa bai shiga jam’iyyar ADC ba ne saboda tsoron abin da ka iya faruwa ga masu adawa da gwamnati.

Galadima ya ce:

“Tun da farko shiyasa na ƙi shiga ADC ne, gudun kar Tinubu ya jefa mana bam mu mutu gaba ɗaya.”

Ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da ya yi da kafar BBC Hausa, inda kalamansa s**a janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin masu bibiyar siyasar Najeriya.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sarauniya TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share