YMR Media

YMR Media Media News Company
Education, Support and Entertainment
(3)

Yaƙin Iran kai tsaye: Sojojin Amurka da Saudiyya sun kai hari kan ƙungiyoyin da ke da alaƙa da Tehran a Iraki.Sojojin Am...
29/07/2026

Yaƙin Iran kai tsaye: Sojojin Amurka da Saudiyya sun kai hari kan ƙungiyoyin da ke da alaƙa da Tehran a Iraki.

Sojojin Amurka da Saudiyya sun kai hare-hare kan ƙungiyoyin da ke da alaƙa da Iran a Iraki a matsayin ramuwar gayya ga hare-haren jiragen sama marasa matuki "30 da dakarun juyin juya halin Iran (IRGC) ta jagoranta" a cikin kwanaki 30 da s**a gabata, ciki har da kan cibiyoyin mai na Saudiyya. Wannan ikirarin ya zo ne jim kaɗan bayan da Amurka ta zargi Iran da harba mak**ai masu linzami da dama a wani hari na ba zato ba tsammani" kan dakarunta a wani sansani da ke Jordan.

Daga Aljazeera News ✍️

'Yan bindiga sun yi garkuwa da babban Alkalin kotu a jihar Kebbi Faruk Hassan Bunza.Rahotonni sun bayyana cewa an sace a...
27/07/2026

'Yan bindiga sun yi garkuwa da babban Alkalin kotu a jihar Kebbi Faruk Hassan Bunza.

Rahotonni sun bayyana cewa an sace alkalin ne da misalin karfe 12:00 na daren ranar Lahadi a gidan shi da ke kan titin Zogirma, karamar hukumar Bunza a jihar Kebbi.

Kotu Ta Karɓe Motoci Guda Sha Ɗaya Na Kimanin Naira Bilyan 4.3, Da Kuɗi Dala $50,000, Da Naira Miliyan 30 Daga Wajen Mat...
16/07/2026

Kotu Ta Karɓe Motoci Guda Sha Ɗaya Na Kimanin Naira Bilyan 4.3, Da Kuɗi Dala $50,000, Da Naira Miliyan 30 Daga Wajen Matashiya Aisha Achimugu, Wadda Hukumar EFCC Ke Zargin Wani Kamfaninta Da Almundahnan Bilyoyin Kuɗaɗe

🚨🇳🇴 Hukumar Kwallon Kafa ta Norway ta bayar da duk kuɗin da aka samu daga wasan da Norway ta doke Isra’ila da ci 5-0 ga ...
16/07/2026

🚨🇳🇴 Hukumar Kwallon Kafa ta Norway ta bayar da duk kuɗin da aka samu daga wasan da Norway ta doke Isra’ila da ci 5-0 ga ƙungiyar likitocin agaji domin taimaka wa mutanen Gaza.

Za a yi amfani da kuɗin wajen bayar da magani na gaggawa da sauran tallafi ga mutanen da rikicin ya shafa.

Haka kuma, wani kamfani a Norway ya bayar da fiye da kroner miliyan 3, wato kusan dala 305,000.

Yau Shekaru 35 Da Hadarin Jirgin Alhazan Sokoto A ranar 11 ga watan Yuli 1991, jirgin Nigeria Airways mai lamba 2120 ya ...
11/07/2026

Yau Shekaru 35 Da Hadarin Jirgin Alhazan Sokoto

A ranar 11 ga watan Yuli 1991, jirgin Nigeria Airways mai lamba 2120 ya yi hatsari a Jeddah, Saudi Arabia, in da ya kashe fasinjoji 261 da ma’aikatan jirgin.

Jirgin sama mai lamba 2120 shi ne hatsari mafi muni da ya shafi jirgin DC-8 kuma ya kasance mafi munin bala'in jirgin sama da ya shafi wani jirgin sama kirar Kanada.

Jirgin Nigeria Airways mai lamba 2120 an yi hayarsa ne daga Jeddah, Saudi Arabia, zuwa Sokoto a Nigeria, a ranar 11 ga Yulin 1991, wanda ya k**a da wuta jim kadan bayan tashinsa daga filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz, kuma ya yi hadari a lokacin da yake kokarin komawa domin yin saukar gaggawa, in da mutane 247 s**a mutu da fasinjoji da ma'aikatan jirgin 14.

Jirgin Douglas DC-8 ne wanda Kamfanin Nationair Canada ke sarrafa shi don Jirgin Saman Najeriya.

Hadarin Jirgin sama mai lamba 2120 shi ne hatsari mafi muni da ya shafi jirgin DC-8 kuma ya kasance mafi munin bala'in jirgin sama da ya shafi wani jirgin saman Kanada.

~ Dr Muhammad Cisse

WATA MIYAR: Tsohuwar Yar Takarar Sanatan Jigawa Ta Tsakiya, Dr. Nana Halima Ta Rabawa Yaranta Jarin NairabMilyan 50 Ga M...
11/07/2026

WATA MIYAR: Tsohuwar Yar Takarar Sanatan Jigawa Ta Tsakiya, Dr. Nana Halima Ta Rabawa Yaranta Jarin NairabMilyan 50 Ga Mutane 25, Inda Kowanne Ya Samu Naira Milyan Bibiyu

Ko kuna da irin waɗannan 'yan siyasar a yankunan da kuke?

Daga Abubakar Shehu Dokoki

Yadda gwamnan jihar Sokoto Dr. Ahmad Aliyu Sokoto ya sayi motocin yaƙi na sulƙe tare da gabatarwa da jami'an tsaro a mat...
10/07/2026

Yadda gwamnan jihar Sokoto Dr. Ahmad Aliyu Sokoto ya sayi motocin yaƙi na sulƙe tare da gabatarwa da jami'an tsaro a matsayin gudummawa domin ƙara ƙaimi a yaƙi da matsalar ƴan ta'adda a faɗin jiharsa.

Ministan Tsaro Janar Christopher Musa ne ya karɓi kayan a madadin jami'an tsaro a jiya Alhamis.

Yanzu wannan yar TikTok ɗin data rasu ai kowa yasan tana da kyau, indai kyau ne na ɗaukar hankalin ɗa namiji Allah ya ba...
10/07/2026

Yanzu wannan yar TikTok ɗin data rasu ai kowa yasan tana da kyau, indai kyau ne na ɗaukar hankalin ɗa namiji Allah ya bata.

Gata da ido da ƙirar jiki irin wanda maza ke so, sai dai kash ta mutu ne a ƴar rawar TikTok, tana fitowa tana rawa yanzu Daan Allah wa zaiso yai irin wannan karshen.

Wa zaiso ya mutu ana roƙon jama’a su goge videon sa, shi yasa mukace yan mata kuji tsoron Allah wannan ranar muke jiye muku.

Inji Malam Abdurrahaman Sautus Sunnah

Yadda Sojoji S**a Yi Nasara Kan Ƴan Tà'addà A Yankunan Arewa Maso Gabas
09/07/2026

Yadda Sojoji S**a Yi Nasara Kan Ƴan Tà'addà A Yankunan Arewa Maso Gabas

Innalillahi wainna ilaihi rajun,Wannan mutumin da kuke gani lecturer ne a wata jamia a KanoAnman yakan shiga university'...
08/07/2026

Innalillahi wainna ilaihi rajun,

Wannan mutumin da kuke gani lecturer ne a wata jamia a Kano

Anman yakan shiga university's dayawa yayi lecturing ,shekara biyu kenan daya hana yarinyan mutane gama makaranta idan tayi project takai Saiyace bahaka ba yace saita sake shine s**a hada baki da mujinta, s**ayi masa wayyo yace su Hadu a Cikin BuK saboda yayi lalata da ita.

Bayan ya shiga hannu anga videon sa yana cin dukaa kan lamarin

Daga Madam Korede

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when YMR Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share