KABO MEDIA WATCH

KABO MEDIA WATCH Shafi ne da zai mai da hankali wajen kawo al'amuran da s**a shafi rayuwar jama'a da cigaban yankin.

27/05/2026
Allah ya yiwa Mal. Ali Muhammad MUQADDAMIN TIJJANIYYA NA GARIN KABO. Bayan fama da rashin lafiya na wani lokaci.  Allah ...
27/04/2026

Allah ya yiwa Mal. Ali Muhammad MUQADDAMIN TIJJANIYYA NA GARIN KABO. Bayan fama da rashin lafiya na wani lokaci. Allah ya gafarta masa yasa ya huta.

Yadda  Bikin saukar Alqurani na Makarantar WOFAN Islamiyya ya kasance a Jiya Asabar 25th ga watan Aprilu, 2026.Makaranta...
26/04/2026

Yadda Bikin saukar Alqurani na Makarantar WOFAN Islamiyya ya kasance a Jiya Asabar 25th ga watan Aprilu, 2026.

Makarantar WOFAN Islamiyya ta yaye dalibai Maza da mata 32 wadanda s**a sauke alkur'ani.

A kokarin Haj. Dr. Salamatu Garba na samar da kyakyawan yanayi na tarbiyyar yara manyan gobe da kuma ilmi mai albarka a wannan Karon ma Wofan Islamiyya ta yaye Dalibai 32.

Iyayen yara Sunyi matukar nuna godiyarsu da Farinciki ganin yayansu sun sauke alkur'ani Mai girma.
Kuma sun Mika godiyarsu ga Haj. Salamatu Garba da Malaman WOFAN ISLAMIYYA.

Haj. Salamatu tayi addu'ar fatan Alkhairi ga dalibai da iyaye tare tayasu farin ciki Mara masaltuwa da wannan gagarumin cigaba wajen samarwa yayanmu ilimin boko da na addini dan Samar da rayuwa mai inganci Wanda zamu yi Alfahari dasu da kasarmu mai Albarka baki daya.

A karshe ta yiwa daukacin Alummar da s**a halarci wannan gagarimin bikin sauka fatan Alheri da fatan kowa ya koma gida lafiya.

Gwamnan Kano ya aika da sunan tsohon Kwamishina Kuma tsohon Dan takarar mataimakin gwamna Ho. Murtala Sule Garo zuwa Maj...
22/04/2026

Gwamnan Kano ya aika da sunan tsohon Kwamishina Kuma tsohon Dan takarar mataimakin gwamna Ho. Murtala Sule Garo zuwa Majalisa domin tantanceshi a matsayin mataimakin Gwamna.

Allah ya gafartawa Saddiku Mai Walda da Dahiru alkali. Allah  ya bawa ahalinsu hakurin rabuwa dasu. Allah ka gafarta Man...
20/04/2026

Allah ya gafartawa Saddiku Mai Walda da Dahiru alkali.
Allah ya bawa ahalinsu hakurin rabuwa dasu. Allah ka gafarta Mana.

A Rana irin ta Yau 31/03/2026.Yau Shekaru 11 Da Daukar Wadannan Hotunan. Jama'a sun cika tituna a unguwar Tudun Wada da ...
31/03/2026

A Rana irin ta Yau 31/03/2026.
Yau Shekaru 11 Da Daukar Wadannan Hotunan. Jama'a sun cika tituna a unguwar Tudun Wada da ke Kaduna da wasu sassan kasarnan su na murnar lashe zaɓen shugaban kasa a jam'iyyar APC, Muhammadu Buhari a ranar Talata 31 ga watan maris 2015..

Labarai cikin hotuna.  WOFANYadda kungiyar Wofan take  raba Kekuna ga masu bukata ta Musamman a garin Garo dake Karamar ...
28/03/2026

Labarai cikin hotuna. WOFAN

Yadda kungiyar Wofan take raba Kekuna ga masu bukata ta Musamman a garin Garo dake Karamar hukumar Kabo karo na farko.

An hangi wasu dubun dubatar  bakaken tsuntsaye masu matukar yawa a saman sararin samaniyar Babban birnin Israila Tel'abi...
27/03/2026

An hangi wasu dubun dubatar bakaken tsuntsaye masu matukar yawa a saman sararin samaniyar Babban birnin Israila Tel'abib Suna shawagi.

Tsuntsayen sunyi yawan da har s**a yiwa sararin samaniyar garin Tel'abib rumfa a yayin da s**a rufe Rana har hakan ya haifar da duhu Mai tsanani Musamman a yankin da Azrael Tower take. Bidiyon faruwar lamarin yayi yawo shafukan Sada zumunta.

Sakamakon faruwar hakan, a gurin masana Ilmin hasashe da tsatsuba na Israila sun kyautata hasashen lokacine na rushewar tasirin ikon yahudawa aduniya. Wadanda lokacinsu yayi Suna jiran lokacin jana'iza ne kawai.


Masana Ilmin hasashen da tsatsuba sunyi imanin cewa tsuntsayen Suna zuwane domin su hukunta abinda ya ragu bayan rushewar ikon Yahudu, ance Bakaken tsuntsayen Suna Jin Kamshin mutuwa da Kuma firgici.

A bangaren malamai masana Bible da Kuma Attaura, bakaken tsuntsayen alamace dake nuna karshen Israila.

Kungiyar Wofan ta kaddamar da gina rijiyoyin burtsatse masu sola a wasu sassan Karamar hukumar Kabo tare ginin Wofan Cen...
25/03/2026

Kungiyar Wofan ta kaddamar da gina rijiyoyin burtsatse masu sola a wasu sassan Karamar hukumar Kabo tare ginin Wofan Centre a garin Garo.

Shugabar Kungiyar Wofan Dr. Haj. Salamatu Garba ta jaddada kokarinta na tallafawa al'umma ta kowanne fannin rayuwa musamma mata. A yunkurinta na kawo dauki ga al'umma a wannan Karamar hukumar kungiyar ta fara aikin gina rijiyoyin a Garin Gude, Garo, Kanye,Balan da Kuma Rakwancan.

Wannan na zuwa Jim Kadan bayan Kungiyar ta kaddamar da ginin Wofan Centre a garin domin amfanin Kungiyoyin mata don dogaro dakai.

A yayin taron Mai unguwar Garo Mal
Sabiu Ali ya bayyana Jin dadinsa tare ta yabawa da Kuma godiya ga ayyukan Alkhairi da Wofan take kawowa wannan yanki.

Wasu daga cikin mata da s**a amfana sun nuna matukar farinciki da wannan kokari na Wofan domin inganta Rayuwarsu. Suna addu'a Allah ya biyata ya saka Alkhairi ya biya da Gidan Aljanna.

23/03/2026

An koma Makaranta yau.
Litinin 23/03/2026
Ya yanayin komawar makarantar yara a yankunanku?

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KABO MEDIA WATCH posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share