09/10/2025
Takaddama
Tsakakani Kungiyar yan Kasuwar Kabo da Mataimakan Sanata Barau.
A Yan kwanakin nan anji takaddama ta barke tsakanin kungiyar Yan Kasuwa ta karamar hukumar kabo da Kuma wakilan sanata Barau wato masu taimaka masa na musamman (PA's). Biyo bayan kalaman Sakataren kungiyar Yan Kasuwar Alh. Magaji na Alh Sulaiman, inda ya zargi wakilan Sanata Barau da nuna rashin kulawa ga al'umma da Kuma korarwa Sanata mutane, inda ya zargi wakilan nasa da rashin taimakawa al'umma sai dai su azurta kansu, harma ya jefa zargin cewa sun mayar da al'amuran mutane kasuwanci suna azurta kansu da sunan Sanata Barau a wani lokaci da iftila'in hadarin mota ya ritsa jama'a a yayin tafiya dauren auren yayan Sanata Barau.
Kalamansa sun nuna karara cewa makusantan Sanata Barau sune matsalar tafiyar siyasarsa a karamar hukumar kabo. Kuma ya bayyana cewa suna munafinci domin raba Sanata Barau da mutane idan ba su ba.
A karshe ya nuna cewa lokacin da Sanata Barau ya baro Karamar hukumar Tarauni ya dawo Kabo, sanatan ya rokesu Kan su amince domin hada hotonshi da sunansu tun a Farkon yini. Kuma yaja hankalin Yan kungiya Kan suyi rijistar zabe domin inda ba kasa nan ake gardamar kokawa.
A bangaren wakilan Sanata Barau kuwa Alh. Bala D.P.O ya mayar da martani inda bayyana zarge-Zargen da rashin ilmi Kan lamuran da suke faruwa, yace lokacin da Barau yazo Kabo ba'a kirkiri kungiyar Yan Kasuwa ba, domin kuwa Shima member ne a kungiyar a baya har ya rike matsayin Mataimakin shugaba.
Sannan ya karyata ikirari cewa suna kasuwanci domin azurta kansu ta hannun Sanata Barau, yayi bayanin yadda aka kula da wadanda hadarin mota ya ritsa dasu a yayin zuwa daurin Auren yayan Sanata Barau akan hanyarsu ta Abuja a watannin baya.
Kuma yace idan ba'a yabawa Sanata Barau ba bai kamata a kushe ba. A karshe yayi addu'ar Allah ya saka musu Kan tuhume-tuhumen da yayi musu cewa Allah na kallo Kuma ya bayyana cewa basa tsoran Kowa a bakin akwatu mu zuba mu gani a 2027 din.
Lamarin ya jawo kace-nace a shafukan sada zumuta, a inda wasu suke goyan bayan kalaman Kungiyar a yayin da wasu suke ganin cewa kungiyar bata da alaka da siyasa yin kalaman zai iya jawo mata matsala tunda ba kungiyar Siyasa bace.
A hannu guda Kuma anjiyo Shugaban wannan kungiyar Alh. Adamu Salisu ya gargadi Yan kungiya Kan Kar su Kara magana Kan Sanata Barau.