02/02/2026
An k**a mutum 21 da ake zargi da haƙar ma'adanai ba bisa ƙa’ida ba a Zamfara
Dakarun rundunar haɗin gwiwa da ke yaƙi da haƙar ma'adanai ba bisa ƙa’ida ba a Jihar Zamfara, sun yi nasarar k**a mutum 21, waɗanda ake zargi da ayyukan haƙar ma'adanai ba bisa ƙa’ida ba.
Bayanai sun nuna cewa, tun da yammacin asabar ce aka k**a waɗanda ake zargin a mabambantan mahaƙun da basu da lasisi, da s**a haɗa da wata mahaƙa a ƙauyen Boko na ƙaramar hukumar Zurmi da ƙauyen Kaya na ƙaramar hukumar Muradun.
A wata sanarwa da ya fitar jiya Lahadi, mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Yazid Abubakar, ya tabbatar da aukuwar lamarin inda ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.
A baya-bayan nan dai, ana danganta masu haƙar ma'adanai ba bisa ƙa’ida ba da ayyukan ta'addanci da s**a yi ƙamari a yankunan jihar ta Zamfara, dalili kenan da ya sanya aka tsaurara matakan tsaro.