Channel Global News

Channel Global News Broadcasting News & Advertisement

22/06/2024

JIHAR KANO A YAU

Haqiqa al'amuran dake faruwa kuma ke cigaba da kakawo a Jihar Kano abin bakin ciki da takaici ne.

Wannan wayannan hanyoyi da ake bi, hanyoyi ne wayanda zasu cigaba da kawo mana tasgaro da koma baya a matsayin Jihar mu datayi shura a fannin kasuwanci, zaman lafiya da ilimin addini hadida mulkin masarautu a fadin na hiyar africa.

Tsaron Lafiya da dukiyoyi a Jihar Kano abin yana so ya huce gona da iri, kamar yarda Rahotonni suke fitowa na tashe tashen hankula da fadan daba dama shaye-shaye da fataucin muyagun kwayoyi ke neman samun gin din zama a Jihar mu.

A saboda haka muna kira da kwarkwarar murya da gwamnatin Tarayyar Najeriya data barranta kanta daga dukkan abubuwan dake faruwa a Jihar nan.

A kuma tabbatar da cewa doka da order tayi aiki akan kowa.

Cigaban Jihar Mu, zaman Lafiyar Mu Da dawwamuwar arzikin mu shine mafi a'ala Agaremu fiye da komai.

Muna Rokon Allah daya bamu Lafiya da Zama Lafiya.

Allah Kuma Ya tsare mana mutuncin mu, Imanin Mu dakuma addinin mu Ameen.

Hukumar Zartarwar  Kafofin Yada Labaran Sharhi Radio/Tv/Makaranta. Karkashin jagorancin Prof. Aliyu Abdullahi Jibia Gen....
18/09/2022

Hukumar Zartarwar Kafofin Yada Labaran Sharhi Radio/Tv/Makaranta.

Karkashin jagorancin Prof. Aliyu Abdullahi Jibia Gen. Manager na sanar da daukacin al'umma cewa da akwai Training da aka shirya bayarwa a fannoni daban-daban da s**a shafi kafafen sadarwa na social media.

Wannan Training din zai kasan ce na hadin gwiwa tsakanin Hukumar Kafafen Sharhi Dakuma Kafafen Sada Zumunta Na Facebook, Twitter da Instagram.

Training ( Horarwar ) zata kasan ce a ranar 1/10/2022 dakuma 2/10/2022 a ranakun Asabar Da Lahadi.

Fannonin za'a bada Training ( Horen ) sune

1. Gabatar Da Ma'ana Manufa Dakuma Aikin Kafafen Sada Zumunta.

2. Dabaru Da Hikimomin Yarda Ake Yada Labaran Siyasa Da Tallata Yan Siyasa A Kafafen Sada Zumunta.

3. Yarda Ake Amfani Da Kafafen Sada Zumunta Da Internet Wajen Gudanar Da Kasuwanci.

4. Koyarda Yarda Ake Hada Shafin Internet Wato Website.

5. Hanyoyin Da Mutum Zaibi Yayi Suna A Duniya A Shafukan Sada Zumunta.

6. Sanin Waye Dan Gwagwarmaya A Social Yarda Ake Zama Dakuma Hanyoyin Zama Shahararre.

Bayan kammalawa da akwai Certificate wanda hadin gwiwa ne da kafafen sada zumunta wanda za'abawa duk wanda ya shiga cikin shirin.

Domin shiga cikin shirin sai a tintibi wayannan lambobi +2349032720787, +2348164176343, +2348032815439.

Anayin register akan kudi Naira 2,000.

Allah Yabada Ikon Amfana Ameen.

Sign.....Aliyu Danjuma Hamza
Manager Director Sharhi Radio
18/09/2022

Dole Ne A Dama Da  Mata A Siyasa Dama Harkokin Gudanar Da Gwamnati A Najeriya- Barr. Haj. Lailai Buhari Barr. Lailai buh...
16/09/2022

Dole Ne A Dama Da Mata A Siyasa Dama Harkokin Gudanar Da Gwamnati A Najeriya- Barr. Haj. Lailai Buhari

Barr. Lailai buhari wadda lauya ce yar gwagwarmaya kuma yar siyasa ta baiyana ce yanzu lokaci yayi wanda gwamnatoci, kungiyoyi dakuma hukumomi da sauran ma'aikatu masu zaman kansu dasu fahimci cewa mata suna da gagarumar gudunmawar dazasu bayar wajen kawu gagarumin sauyi a cigaba mai daurewa a fadin tarayyar Najeriya dama inda matan s**a tsinci kansu a ciki.

Inda takara da cewa " Sanin kowa ne cewa mata basa samun cikakkiyar dama dakuma yancin samun madafam iko a cikin harkokin siyasa da gudanar da mulki a matakan kananan hukumomi, jihohi dama kasa baki daya.

Duk da kasan cewar muna bada gagarumar gudunmawa wajen tabbatar da mulkin damakwaradiyya dakuma aiki tukuru a fannonin lafiya, ilimi da sauran su. Amma duk da haka muna cigaba da kokawa bisa watsi da akayi damu.

Babu wata gwamnati datake tafiya kafada da kafada da mata a Najeriya.

A saboda haka inamai amfani da wannan dama domin karfafawa yan'uwana mata gwiyoyin su akan sufito domin a dama dasu akan harkokin da s**a shafi siyasa, kungiyoyi domin kawo sauyi da cigaba "

Daga karshe ta baiyana gudurinta na tabbatar da cewa an samu kyakykyawa kuma ingantacciyar damakwaradiyya wadda zata bawa mata dama dakuma yancin zayawa takarkaru a matakan shugabancin kasa, gwamnoni, majalissar dattawa da majalissar wakilai hadi da majalissosin jihohin a fadin Najeria.

Inda takara da cewa darewar mata kan kujerun mulki a matsayin nadaddu ko zababbu na daya daga cikin hanyoyin da zasu kawo karshen matsaloli da kalubalolin da s**a addabi Najeriya ta fiskar fatara da talauci, shaye-shayen muyagun kwayoyi da fataucin su, rashin ilimi da rashin aiyukanyi hadi da matsalolin tsaron da s**a addabi Najeriya.

Inda takara da cewa "Rayuwar mata cike take da hakuri, juriya dakuma jajircewa.

Haqiqa inada tabbacin cewa mata a shirye suke s**awo karshen matsalolin da kasar nan ke ciki muddin aka basu dama.

Sannan idan akai duba natsanaki za'aga cewa mata ne ke iya sadaukar da rayuwarsu domin cigaban al'ummarsu kuma muna da baiwa da hazaka mai yawa wadda zamu iya tafikantar da shugabanci kuma muyi nasara

Daga karshe inafatam cewa yan'uwana mata zasu cigaba da jajircewa a dukkan lamuran su domin cigaban rayuwar su."

YANZU-YANZU| Sarkin Kano Ya Nada Sheikh Aminu Daurawa Limancin Juma'a.A ranar Alhamis 15/9/2022,  mai martaba sarkin kan...
16/09/2022

YANZU-YANZU| Sarkin Kano Ya Nada Sheikh Aminu Daurawa Limancin Juma'a.

A ranar Alhamis 15/9/2022, mai martaba sarkin kano Alh Aminu Ado Bayero, ya amince da nadin Sheik Aminu Ibrahim Daurawa, amatsayin sabon limamin masallacin juma'a na makarantar Skyline University, dake cikin birnin kano.

DA DUMI-DUMI: Shugaban Hukumar Kula da Ayyukan ‘Yan Sanda (PSC), Musiliu Smith ya yi murabus daga mukaminsa.An tattaro c...
14/09/2022

DA DUMI-DUMI: Shugaban Hukumar Kula da Ayyukan ‘Yan Sanda (PSC), Musiliu Smith ya yi murabus daga mukaminsa.

An tattaro cewa hukumar ta bukaci Smith ya yi murabus kuma ya karba.

Ko da yake hukumar ba ta sanar da murabus din nasa a hukumance ba, wata majiya mai tushe a hukumar ta shaida wa Aminiya cewa ana sa ran Smith tsohon Sufeto-Janar na ‘yan sanda zai mika shi ga mai shari’a Clara Ogunbiyi mai ritaya mai wakiltar shari’a a hukumar.

Kakakin hukumar Ikechukwu Ani shi ma ya tabbatar wa wakilinmu murabus din ta wayar tarho.

Gwamnatin Kano Ta Gana Da ASUU, Ta Bukaci Dakatar Da Yajin aikin Mallakar Jihar.A yammacin ranar Talata ne gwamnatin jih...
14/09/2022

Gwamnatin Kano Ta Gana Da ASUU, Ta Bukaci Dakatar Da Yajin aikin Mallakar Jihar.

A yammacin ranar Talata ne gwamnatin jihar Kano ta kira wani taro da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) na jami’o’in jihar guda biyu da ke jihar tare da babban bukatarsu dangane da dakatar da yajin aikin da suke yi.

Aminiya ta ruwaito cewa taron ya gudana ne tsakanin jami’an gwamnatin jihar da ‘yan kungiyar ASUU daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kano (KUST), Wudil, da Jami’ar Yusuf Maitama Sule (YUMSUK).

Taron wanda ya dauki tsawon sa’o’i da dama ya kawo karshe cikin rashin jituwa tare da yin alkawarin sake haduwa nan da mako guda amma babu tabbacin.

Shugaban ma’aikatan jihar Kano, Usman Bala Muhammad ya roki kungiyar har ma ya bukaci shugabanninsu da su dakatar da kungiyar ta ASUU na tsawon watanni uku.

Ya, duk da haka, ya bai wa ƙungiyar mako guda don sake duba mafi kyawun zaɓuɓɓuka kuma sake yin taro yayin da yake ba su aiki su zo da gaskiya mai ɗaci - mafita don ayyukan ilimi don ci gaba.

2022 Cibiyar Falsafa da Ka'idar Siyasa don MatasaA cikin 2017 CITAD ta fara Ibrahim Muazzam Cibiyar Falsafa da tunani ma...
11/09/2022

2022 Cibiyar Falsafa da Ka'idar Siyasa don Matasa
A cikin 2017 CITAD ta fara Ibrahim Muazzam Cibiyar Falsafa da tunani mai zurfi, koyar da tunanin falsafa, musamman a cikin ilimin zamantakewa da ka'idar siyasa. Manufar Cibiyar ita ce ta dawo da koma bayan ingancin koyarwar Falsafa da Ka'idar Siyasa ga Matasa, wanda ya shafi ingancin tunanin daliban jami'a.
Cibiyar, wadda ta kasance taron shekara-shekara, an kaddamar da ita ne don karrama Ibrahim Muazzam wanda ya yi ritaya a kwanan baya bayan shafe shekaru fiye da arba'in yana karantar da ka'idar siyasa, falsafar siyasa, ka'idojin duniya na uku da sauran batutuwa masu alaka da s**a ci gaba da yin tasiri a cikin tunani mai zurfi. mutane da dama da s**a wuce Jami’ar Bayero, Kano.
Cibiyar tana da manyan ayyuka guda uku. Karatun tunani na siyasa na gargajiya, ka'idar da falsafa ta hanyar laccoci; haɗin kai tare da batutuwa na yanzu; da kuma muhawara don tsara haɗin kai na hankali na mahalarta.
Fitattun mutane uku ne za su gudanar da taron na bana. Su ne:
Ibrahim Mu'azzam
Ibrahim Bello-Kano (aka IBK)
Dipo Fashina
Buga na 2022 na Cibiyar zai gudana ne a Babban Ofishin CITAD da ke Kano. An tsara shi a cikin Nuwamba 2022. Idan kuna son shiga Cibiyar don Allah, ziyarci hanyar haɗin yanar gizon https://forms.gle/oaK3hhHTDUkUM8Rn6 kuma ku cika bayanin da ake buƙata, sabuwar Oktoba 23, 2022.
Hakanan zaka iya aiko da niyyar shiga: [email protected]. Don ƙarin bayani a kira/aiko da saƙon SMS zuwa 08036509534, 08054362931, 07033427467.
Za a ba da fifiko ga waɗanda s**a kammala karatun jami'a a fannin ilimin zamantakewa da ɗan adam, matasa malamai da ɗaliban da s**a kammala karatun digiri.
CITAD ba ta iya ba da tallafin kuɗi ga Cibiyar. Mahalarta zaɓaɓɓu suna da alhakin jigilar su (ciki har da sufurin gida) da masauki (ga waɗanda ke zaune a wajen Kano). Akwai masauki mai araha da tsafta a Cibiyar Dijital Bridge (DBI) wacce CITAD za ta iya tsarawa ga masu sha'awar (farashin da aka yi yarjejeniya ya kasance N5000 a kowane dare.

A Yau Ne Sanata Oluremi Tinubu Da Hajiya Nana ShettimaS**a Bayar Da Tallafin Kayan Agaji Ga ‘Yan Gudun Hijira.Wayanda s*...
11/09/2022

A Yau Ne Sanata Oluremi Tinubu Da Hajiya Nana Shettima
S**a Bayar Da Tallafin Kayan Agaji Ga ‘Yan Gudun Hijira.

Wayanda s**a amfana da tallafin sun hadarda zawarawa, da masu bukata ta musamman a al’ummar Karon-majigi da ‘Yargoje a babban birnin tarayya Abuja.

Haka kuma an bada gudummawar buhunan shinkafa 70, masara buhu 60, wake 60, katon imdomie 250, jarkar mai 15, gishiri 10, katon Maggi 20, nannade 600 da tufafin jarirai 250. Sun kuma ba da gudummawar kuɗi ga al'ummomin biyu.

Sun kasance tare da su a ziyarar jin kai da shugabar mata ta kasa Dr. Betta Edu, tsohuwar shugabar mata ta kasa kuma babbar daraktar bankin NEXIM, Hon. Stella Okotete da mata da dama daga jam'iyyar Progressive fold.

Sun kuma kai ziyara ga Alhaji Yunusa Bako Abdullahi, sarkin gargajiya na Karon-majigi.

Haka zalika suma wayanda s**a amfana da tallafin sun baiyana farin cikin su da jindadin su bisa wannan tallafi da akai musu.

Daga karshe tawagar matan taja hankali wayanda s**a amfana da tallafin dasuyi amfani dashi domin magance matsalolin da s**a shafi yau da kullum tare da tabbatar musu da cewa zasu cigaba da amfana da ire-iren wayannan tallafuffukan.

Wata ‘yar jarida a kano tasha alwashin maka duk wani mai mukamin Siyasa a K/H Nasarawa a gaban kotu ‘yar jaridar tasha a...
10/09/2022

Wata ‘yar jarida a kano tasha alwashin maka duk wani mai mukamin Siyasa a K/H Nasarawa a gaban kotu

‘yar jaridar tasha alwashin maka duk wani mai mukamin Siyasa a K/H Nasarawa a gaban kotu


Daga Halima Musa Adam Sabaru

Yar jarida Hannatu Suleiman Abba taci alwashin maka duk wani mai mukami a karamar Hukumar Nassarawa dake jahar kano, bisa yadda unguwar Hotoro Arewa ta kasance tun da aka fara ruwa a dare juma’a a ranar 9 ga watan satumba.

Hannatu ta ci alwashin cewa, unguwar ta shafe sama da awa daya da rabi babu hanyar wucewa,Wanda Haka yasa s**a shiga ciki ruwa mai tare datti don samu gurin da zasu fake.

Inda ta wallafa a shafin ta na Facebiik cewa”

Inda har kuraje a kafa s**a fitomin bayan Shiga ruwan unguwar Hotoro North ,in Sha Allah sai na maka duk wani Dan siyasa Mai mukami a YANKI gurin a KUTU.Allah ne kadai yasan iya addadin wayenda ta sillar Shiga ruwar don neman hanyar wucewa yasa s**a kamu da cututukan fata.

Nayi wanka na wanke kafa ta ,Amma har yau ina jin Dan kaikayi”.

A wani faifain vediyo da ta saka a shafin nata ,ta Kara nuna yadda unguwar ta kasance ,duk da ta samu barazana ga wani Wanda Yake wuce wa a lokacin da take daukar rahoto Kai tsaye a kafar sadarwa ta Fesbuk

Unguwar Hotoro Arewa dai,na Daya daga cikin unguwani da ake samu ambaliyar ruwa da ke shiga gidanje mutane tare da Yi musu barazana lafiya da dukiya a duk damina.duk da yawan korafe korefe da Yan unguwar ke Kai wa ga mahukunta Amma har yau ba a samu mafita . dalibai da yawa basa samu damar zuwa makaranta inda har damina tayi karfi a Yanki,inji wani malamin makarantar Hotoro Arewa.

Tofa  NNPP mekayan marmari Tamaka INEC Akoto Kome Yai Zafi.     DAGA Halima Musa Adam SabaruJam’iyyar NNPP ta gurfanar d...
10/09/2022

Tofa NNPP mekayan marmari Tamaka INEC Akoto Kome Yai Zafi.
DAGA Halima Musa Adam Sabaru

Jam’iyyar NNPP ta gurfanar da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (NEC) a gaban Mai Shari’a Hadiza Shagari ta wata babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kaduna.

Jam’iyyar na kalubalantar jerin sunayen ‘yan takarar Gwamna da na ‘yan majalisar jiha na jam’iyyar APC da INEC ta wallafa a ranar 22 ga watan Yuli, domin gudanar da babban zabe.

NNPP Ta Maka INEC A Kotu, Tana Neman Ta Dakatar Da Cancantar ‘Yan Takarar APC A KadunaPublished

Jam’iyyar NNPP ta gurfanar da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (NEC) a gaban Mai Shari’a Hadiza Shagari ta wata babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kaduna.

Jam’iyyar na kalubalantar jerin sunayen ‘yan takarar Gwamna da na ‘yan majalisar jiha na jam’iyyar APC da INEC ta wallafa a ranar 22 ga watan Yuli, domin gudanar da babban zabe.

Jam’iyyar NNPP ta yi zargin cewa ‘yan takarar ba su fito ta hanyar doka ko kuma ka’ida ba kamar yadda dokar zabe da sauran wasu dokoki s**a tanada.

Don haka jam’iyyar ta bukaci kotu da ta tilasta wa INEC yin abin da ya dace ta hanyar cire ‘yan takarar jam’iyyar APC daga jerin sunayen ‘yan takarar da s**a cancanta a zaben 2023 a jihar Kaduna.

Shari’ar wacce aka fara a Kaduna ranar Juma’a, an dage ci gaba da sauraren karar zuwa ranar 15 ga watan Satumba.

Mai shari’a Hadiza ta bayyana cewa, an dage shari’ar ne bisa hujjar cewa har yanzu INEC ba ta kai dukkan bangarorin da muhimman takardu da tsare-tsare da ta kai wa kotu ba.

Lauyan shugaban jam’iyyar NNPP, Wole Agunbiade, SAN, ya shaida wa kotun cewa har yanzu INEC ba ta yi masa aiki ba.

A nasa bangaren, Lauyan jam’iyyar APC, Sule Shuaibu, ya ce an yi masa aiki, ya kara da cewa yana bukatar karin lokaci don gudanar da dukkan takardun, sannan ya roki a ba shi lokaci domin gabatar da bukatarsa.

A baya Lauya ga INEC, Halima Gachi, ta shaida wa kotun cewa ba ta da tabbacin cewa dukkanin bangarorin sun yi aiki.

Address

Ahamd Musa Road CBN Courtest
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Channel Global News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Channel Global News:

Share