AAD MEDIA 24

AAD MEDIA 24 kafa dazata dinga kawo muku labarai da al'amuran yau da kullum hadi da nishadi kuna iya tuntubarmu ta wannan lambar 07019900927

06/08/2026

Ku kalli yadda Wasu matasa s**a bankawa motar Hukumar KAROTA wuta bayan zargin jami’an hukumar da haddasa wani hatsari a yankin Kwanar Dawaki da ke kan titin Kano zuwa Zariya.

ku bayyana ra’ayinku cikin mutunci da bin doka.

Labari Cikin HotunaGabanin ƙaddamar da shirin Gargaɗi Wuri na Kowa (Early Warnings for All – EW4All) a hukumance, Darakt...
06/08/2026

Labari Cikin Hotuna

Gabanin ƙaddamar da shirin Gargaɗi Wuri na Kowa (Early Warnings for All – EW4All) a hukumance, Darakta Janar ta Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, ta karɓi baƙuncin shugabannin manyan hukumomin ƙasa a wani muhimmin taron dabarun aiki da aka gudanar a hedkwatar NEMA da ke Abuja.

Taron ya haɗa da shugaban Hukumar Kula da Yanayi ta Ƙasa (NiMet), Farfesa Charles Anosike; shugaban Hukumar Kula da Harkokin Ruwa ta Ƙasa (NIHSA), Alhaji Ahmed Ibrahim Mohammed; shugaban Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), Dr. Aminu Maida; da shugaban Hukumar Bincike da Bunƙasa Fasahar Sararin Samaniya ta Ƙasa (NASRDA), Dr. Matthew Adepoju.

Shirin EW4All na da burin tabbatar da cewa nan da shekarar 2027, dukkan 'yan Najeriya sun samu kariya ta hanyar tsarin gargaɗin wuri daga haɗurran matsanancin yanayi, ambaliyar ruwa, sauyin yanayi da sauran barazanar muhalli.

Me za ku ce?

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya raba wa Babban Limamin Ilorin da Majalisar Malaman Masarautar Ilorin mot...
05/08/2026

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya raba wa Babban Limamin Ilorin da Majalisar Malaman Masarautar Ilorin motoci huɗu domin tallafa wa harkokin addini da ayyukan shugabannin addini a jihar.

Motocin sun haɗa da sabuwar Toyota Prado ga Babban Limamin Ilorin, Sheikh Muhammad Bashir Dasuki, bas ga Majalisar Malamai, da kuma motoci ga Limamin Imale da Limamin Gambari.

An miƙa motocin ne a fadar Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, wanda ya yaba wa gwamnan bisa cika alkawarin da ya yi tare da ci gaba da tallafa wa harkokin addini.

Me za ku ce kan wannan mataki na gwamnatin Kwara?

Mohamed Salah ya sauka a birnin Istanbul na ƙasar Turkiyya gabanin kammala komawarsa zuwa Trabzonspor, inda ake sa ran z...
05/08/2026

Mohamed Salah ya sauka a birnin Istanbul na ƙasar Turkiyya gabanin kammala komawarsa zuwa Trabzonspor, inda ake sa ran zai haɗu da Andre Onana.

Wannan sauyin sheka ya ɗauki hankalin masoya ƙwallon ƙafa a duniya, musamman ganin irin tarihin da Salah ya yi a Turai.

Me za ku ce kan wannan mataki na Salah? Shin Trabzonspor ta yi babban kamu?

Da Ɗumi-Ɗumi: Matatar Man Ɗangote Ta Rage Farashin Fetur Da DizalMatatar man Ɗangote ta sanar da rage farashin man fetur...
05/08/2026

Da Ɗumi-Ɗumi: Matatar Man Ɗangote Ta Rage Farashin Fetur Da Dizal

Matatar man Ɗangote ta sanar da rage farashin man fetur da dizal da take sayarwa ga masu dillanci. Sabon farashin ya nuna cewa an rage litar fetur daga N1,215 zuwa N1,165, yayin da aka rage litar dizal daga N1,650 zuwa N1,570.

Wannan mataki na zuwa ne a matsayin ƙoƙarin rage tsadar makamashi da sauƙaƙa wa ƴan Nijeriya nauyin farashin kayayyakin mai.

Shin kuna ganin wannan ragin farashi zai sa gidajen mai su rage farashin da suke sayar wa jama'a?

HOTUNA: Cunkoson ababen hawa ya mamaye babbar titin Kano zuwa Gwarzo bayan wata motar dakon simintin kamfanin BUA ta maƙ...
05/08/2026

HOTUNA: Cunkoson ababen hawa ya mamaye babbar titin Kano zuwa Gwarzo bayan wata motar dakon simintin kamfanin BUA ta maƙale yayin da take ƙoƙarin juyawa a kwanar da ke kusa da ofishin ’yan sanda na Rijiyar Zaki.

Me za ku ce?

Hotunan yadda aka ɗaga jirgin kamfanin sufurin Enugu Air da ya yi hatsari a kwanakin baya a filin jirgin saman Benin da ...
05/08/2026

Hotunan yadda aka ɗaga jirgin kamfanin sufurin Enugu Air da ya yi hatsari a kwanakin baya a filin jirgin saman Benin da ke Jihar Edo, domin kai shi wurin da za a ajiye shi.

A ganinku, shin za a gyara jirgin ya koma aiki, ko kuwa lalacewar da ya yi ta kai matsayin da zai zama kayan jari-bola?

Ku bayyana ra'ayoyinku a sashen sharhi.

Kotun Tafi da Gidanka kan Tsaftar Muhalli ta Hukumar REMASAB a Jihar Kano ta hukunta wuraren kasuwanci takwas bisa karya...
05/08/2026

Kotun Tafi da Gidanka kan Tsaftar Muhalli ta Hukumar REMASAB a Jihar Kano ta hukunta wuraren kasuwanci takwas bisa karya dokokin tsaftar muhalli.

Daga cikin matakan da aka ɗauka akwai rufe gidan man Ama Zuma saboda rashin tsafta, yayin da aka hukunta wasu gidajen mai da wuraren kasuwanci kan laifuffuka da s**a haɗa da zubar da shara ba bisa ƙa'ida ba, rashin kwandunan shara, ciyayi da gurɓata muhalli.

Shugaban REMASAB, Dakta Muhammad S. Khalil, ya jaddada cewa hukumar za ta ci gaba da aiwatar da dokokin tsaftar muhalli tare da ɗaukar mataki kan duk masu karya su domin tabbatar da tsaftataccen muhalli a faɗin jihar Kano.

Me za ku ce?

Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar Bauchi, Sani Omolori Aliyu, ya karɓi tawagar Hukumar Kula da Ababen More Rayuwa ta Jihar B...
05/08/2026

Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar Bauchi, Sani Omolori Aliyu, ya karɓi tawagar Hukumar Kula da Ababen More Rayuwa ta Jihar Bauchi (BASIDMA) domin tattauna hanyoyin ƙarfafa haɗin gwiwa wajen kare kadarorin gwamnati da inganta tsaro a faɗin jihar.

A yayin ganawar, kwamishinan ya tabbatar da shirye-shiryen rundunar na ci gaba da ba da cikakken goyon baya wajen kare muhimman kadarorin gwamnati, tare da buƙatar BASIDMA ta riƙa bayar da sahihan bayanai domin ɗaukar matakan kariya cikin lokaci.

Haka kuma, ya karɓi tawagar al'ummar Ebira da ke Azare a Ƙaramar Hukumar Katagum, inda ya yaba da ziyarar tare da sake jaddada kudirin rundunar wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar Bauchi.

Me za ku ce?

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya raba motocin alfarma ga jami'an gudanarwar Jami'ar Abdulkadir Kure da ke Min...
05/08/2026

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya raba motocin alfarma ga jami'an gudanarwar Jami'ar Abdulkadir Kure da ke Minna (AKUM) domin sauƙaƙa musu gudanar da ayyukansu.

Gwamnan ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da fifiko ga harkokin ilimi da walwalar ma'aikatan jami'o'i, yayin da Shugaban Majalisar Gudanarwar jami'ar, Farfesa Mohammed Kuta Yahaya, ya yaba da wannan tallafi tare da bayyana cewa ya ƙara wa jami'ar kima da jan hankalin masu neman ilimi a Najeriya.

Me za ku ce?

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AAD MEDIA 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share