22/08/2026
Sheikh Ibrahim El-Zakzaky ya ce babu wani shugaban da zai iya gyara matsalolin Najeriya yadda ake fata, matukar tsarin tafiyar da ƙasar bai sauya ba.
Ya ce ko da wani mala’ika wanda bai taɓa aikata zunubi ba ya sauko daga sama ya zama shugaban Najeriya, zai fuskanci matsalar tsarin ƙasar da kuma mutanen da zai yi aiki da su.
A cewar sa, shugaban zai bukaci nada ’yan Najeriya a matsayin ministoci, daraktoci da shugabannin hukumomi, wanda hakan ke nufin matsalar ba ta tsaya kan mutum ɗaya da ke kan mulki ba.
Ya ce: “Ko mala’ika wanda bai taɓa zunubi ba ya sauko daga sama, ka ce shi ne shugaban ƙasar nan, dole sai ya zama azzalumin mala’ika.”
Sheikh Zakzaky ya yi wannan bayani ne wajen jaddada cewa sauya shugabanni kaɗai ba zai wadatar ba, sai an samu sauyin tsarin da ake tafiyar da Najeriya.