Taskira H Online TV

Taskira H Online TV Taskira H Online TV, Kafa ce da ke kawo muku sahihan labarai daga sassa daban-daban na duniya, za ku iya turo mana labarin domin sanar da al'umma kai tsaye!
(2)

Sheikh Ibrahim El-Zakzaky ya ce babu wani shugaban da zai iya gyara matsalolin Najeriya yadda ake fata, matukar tsarin t...
22/08/2026

Sheikh Ibrahim El-Zakzaky ya ce babu wani shugaban da zai iya gyara matsalolin Najeriya yadda ake fata, matukar tsarin tafiyar da ƙasar bai sauya ba.

Ya ce ko da wani mala’ika wanda bai taɓa aikata zunubi ba ya sauko daga sama ya zama shugaban Najeriya, zai fuskanci matsalar tsarin ƙasar da kuma mutanen da zai yi aiki da su.

A cewar sa, shugaban zai bukaci nada ’yan Najeriya a matsayin ministoci, daraktoci da shugabannin hukumomi, wanda hakan ke nufin matsalar ba ta tsaya kan mutum ɗaya da ke kan mulki ba.

Ya ce: “Ko mala’ika wanda bai taɓa zunubi ba ya sauko daga sama, ka ce shi ne shugaban ƙasar nan, dole sai ya zama azzalumin mala’ika.”

Sheikh Zakzaky ya yi wannan bayani ne wajen jaddada cewa sauya shugabanni kaɗai ba zai wadatar ba, sai an samu sauyin tsarin da ake tafiyar da Najeriya.

Tsohon Shugaban Sojojin Ƙasan Najeriya Ambasada Laftanal Janar Tukur Buratai CFR (Mai Ritaya) Betaran Biu kuma Garkuwan ...
22/08/2026

Tsohon Shugaban Sojojin Ƙasan Najeriya Ambasada Laftanal Janar Tukur Buratai CFR (Mai Ritaya) Betaran Biu kuma Garkuwan Keffi, Ya ce ƙwace gwamnati na iya zama abu mafi sauƙi idan aka kwatanta da gudanar da ita yadda ya kamata, Ya bayyana cewa, ko da yake sojoji na iya amfani da ƙarfin su wajen ƙwato yankunan da ƴan ta’adda s**a mamaye, hakan kaɗai ba zai wadatar wajen tabbatar da ingantaccen shugabanci ba.

Kuma ya yi wannan tsokaci ne yayin da yake magana kan gwamnatocin soji da ke mulkin Mali, Burkina Faso da Nijar, inda ya ce ya kamata a duba ko waɗannan gwamnatoci sun samu nasarar da ta fi ta gwamnatocin farar hula da s**a hamɓarar.

A cewar sa, Yaƙi da ta’addanci yana buƙatar nagartaccen shugabanci, adalci, ci gaban tattalin arziƙi, ingantaccen tattara bayanan sirri da kuma ƙarfafa hukumomin cikin gida, Ya kuma yi gargadin cewa yawan dogaro da sojoji wajen gudanar da ayyukan tsaron cikin gida na iya raunana hukumomin farar hula, musamman ƴan sanda da sauran hukumomin leƙen asiri.

Kazalika, Janaral Buratai ya daɗe yana jaddada cewa magance matsalolin tsaro na buƙatar haɗin gwiwar gwamnati, hukumomin tsaro da sauran ɓangarorin al’umma, ba ƙarfin soja kaɗai ba.

Taskira H Online TV :- Shin gwamnatocin sojoji da s**a karɓi mulki a Mali, Burkina Faso da Nijar suna gudanar da mulkin ƙasashen na su fiye da gwamnatocin farar hula da s**a hamɓarar?

‎"Alhaji Tanimu Akawu Yana Nan Da Ransa Bai Mutu Ba", In Ji Jarumin Kannywood, Sadiq Ahmad.‎‎A cewarsa, Allah ya Jarabce...
21/08/2026

‎"Alhaji Tanimu Akawu Yana Nan Da Ransa Bai Mutu Ba", In Ji Jarumin Kannywood, Sadiq Ahmad.

‎A cewarsa, Allah ya Jarabce shi ne da ciwon suga wato Diabetics, kuma yanzu haka yana kwance a Asibitin JUTH da ke cikin garin Jos inda yake samu sauƙi, a ƙarkashin kulawar ma'aikatan lafiya.

‎Dan haka, "Masu yada jita-jitar ya mutu saurin me kuke yi ,kowa zai mutu. Dan haka mu kiyaye, mutuwa de tana kan kowa", in ji Sadik, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta samu rahoto.

Bama goyon bayan dawo da tallafin man fetur domin zai dawo da kasar mu baya sosai Cewar Abdullahi Sule Gwamnan Nasarawa
21/08/2026

Bama goyon bayan dawo da tallafin man fetur domin zai dawo da kasar mu baya sosai Cewar Abdullahi Sule Gwamnan Nasarawa

Hotuna: Yadda aka gudanar da jana'izar Hamza Usman Darma wanda Allah Ya yi wa rasuwa yau Juma'a 21 ga watan Agusta, 2026...
21/08/2026

Hotuna: Yadda aka gudanar da jana'izar Hamza Usman Darma wanda Allah Ya yi wa rasuwa yau Juma'a 21 ga watan Agusta, 2026.

Kazalika, Daga cikin wanda s**a halarci jana'izar akwai mataimakin gwamnan Jihar Kano, Murtala Sule Garo da sauran malamai da masu faɗa aji a gwamnatin tarayya da ta jihar Kano

Dan takarar Gwamna na jam'iyyar APC a jihar Osun, Bola Oyebamiji, ya ziyarci shugaba Bola Tinubu a fadar dhugaban kasa d...
21/08/2026

Dan takarar Gwamna na jam'iyyar APC a jihar Osun, Bola Oyebamiji, ya ziyarci shugaba Bola Tinubu a fadar dhugaban kasa da ke Abuja.

Mataimaki na musamman ga shugaba Tinubu kan kafafen sada zumunta, Olusegun Dada ne ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafin X.

Dada ya wallafa bidiyon ganawar tare da cewa: “shugaba Bola Tinubu ya karɓi Asiwaju Bola Oyebamiji, dan takarar APC a zaɓen gwamnan jihar Osun da aka kammala kwanan nan.

Ɗan uwan matar Kwankwaso Hon. Nasiru Sulen Garo, shi ne zai yiwa Jamiyyar NDC takarar Sanata a Kano ta arewa
21/08/2026

Ɗan uwan matar Kwankwaso Hon. Nasiru Sulen Garo, shi ne zai yiwa Jamiyyar NDC takarar Sanata a Kano ta arewa

Yadda Matakan Gyaran Tinubu S**a Kawo Ƙarshen Matsalar Biyan Albashi A Jihohi 27A watan Mayun 2023, lokacin da gwamnatin...
21/08/2026

Yadda Matakan Gyaran Tinubu S**a Kawo Ƙarshen Matsalar Biyan Albashi A Jihohi 27

A watan Mayun 2023, lokacin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta fara aiki, jihohi 27 daga cikin 36 na Najeriya na fuskantar matsalar biyan albashin ma’aikatansu yadda ya kamata. Shekaru uku bayan haka, wannan adadi ya sauya, babu wata jiha da take kasa biyan albashin ma'aikatan ta a cewar alkaluman da gwamnatin tarayya ta gabatar a cikin "Nigeria’s Reform Scorecard".

Wannan sauyi na zuwa ne bayan wasu manyan gyare-gyaren tattalin arziki da s**a hada da cire tallafin man fetur da sake fasalin tsarin canjin kudaden waje. Tsakanin Yunin 2023 da Disamban 2025, an samu Naira tiriliyan 15.8 na tanadin kudaden tallafin man fetur, inda aka raba wa jihohi da kananan hukumomi Naira tiriliyan 10.4.

Karin kudaden da jihohi s**a samu ya kara musu damar gudanar da ayyukansu, ciki har da biyan albashi da kuma daukar nauyin ayyukan ci gaba. A matakin tarayya kuma, an ware Naira tiriliyan 9.39 domin karin albashi, sabon mafi karancin albashi da alawus-alawus ga ma’aikatan gwamnati.

Wannan ya kuma taimaka wajen samun karin albarkatun da s**a bai wa gwamnati damar kara mafi karancin albashi daga Naira 30,000 zuwa Naira 70,000. Bayanai irin wadannan na nuna cewa gyaran tattalin arziki ba ya tsaya kan alkaluman gwamnati kadai ba, yana shafi ma’aikata da iyalansu kai tsaye.

Duk da cewa har yanzu akwai kalubalen tsadar rayuwa da bukatar kara inganta jin dadin jama’a, sauyi daga jihohi 27 masu fama da matsalar albashi zuwa yanzu da babu wata jiha da ke da wannan kalubalen na daga cikin muhimman alamomin da ke nuna kokarin sake gina tsarin tattalin arzikin Najeriya. Gyaran ya fara samar da daidaito, babban aikin yanzu shi ne tabbatar da amfaninsa ya isa ga talaka.

21/08/2026

BIDIYO: Yadda Bola Tinubu, Ya fusata da kalaman Alh. Atiku Abubakar na cewa zai dawo da tallafin man fetur in ya ci zabe, Ku kalli yadda yake maida wa Atiku martani da kansa tare da caccar batun dawo da tallafin

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata ranar hutu saboda Maulidin Manzon RahamaGwamnatin Tarayya ta ayyana Talata, 25 ga Agu...
21/08/2026

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata ranar hutu saboda Maulidin Manzon Rahama

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata, 25 ga Agustan 2026, a matsayin ranar hutu ta ƙasa domin bikin Maulidin Annabi Muhammad (SAWA).

Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya sanar da hakan a madadin Gwamnatin Tarayya, inda ya taya Musulmi a Najeriya da sauran ƙasashen duniya murnar zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAWA).

Ministan ya ce Maulidi na ba da damar yin tunani kan darussan da ake samu daga rayuwar Annabi, musamman tausayi da hidima ga sauran mutane, yana mai cewa waɗannan halaye na daga cikin abubuwan da Najeriya ke matuƙar buƙata a yanzu.

Ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi amfani da lokacin wajen yin addu’o’in samun zaman lafiya da haɗin kan ƙasa, tare da gudanar da bikin cikin natsuwa da mutunta juna. Tunji-Ojo ya tabbatar da aniyar Gwamnatin Tarayya na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa da tabbatar da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

Address

Sheikh Ja'afar Mahmud Adam Road, Dorayi
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskira H Online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share