Taskira H Online TV

Taskira H Online TV Taskira H Online TV, Kafa ce da ke kawo muku sahihan labarai daga sassa daban-daban na duniya, za ku iya turo mana labarin domin sanar da al'umma kai tsaye!
(1)

Hotunan: Yadda Hon. Alh. Murtala Sule Garo, Ya samu rakiyar jagororin APC Gandujiyya zuwa gaban Kwamitin Majalisar Dokok...
23/04/2026

Hotunan: Yadda Hon. Alh. Murtala Sule Garo, Ya samu rakiyar jagororin APC Gandujiyya zuwa gaban Kwamitin Majalisar Dokokin Kano don tantance shi a Mataimakin Gwamnan Jihar.

📷 Abubakar Aminu Ibrahim

Hukumar tsaro ta farin kaya ta DSS ta gurfanar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, bisa zargin sauraron waya...
23/04/2026

Hukumar tsaro ta farin kaya ta DSS ta gurfanar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, bisa zargin sauraron wayar mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu.

A cikin bayanan da s**a fito daga DSS, an bayyana cewa ana zargin El-Rufai da shiga harkar da ta shafi satar bayanan sirri ta hanyar shiga cikin kiran waya ba bisa ka’ida ba.

Rahotanni sun nuna cewa shari’ar na daga cikin matakan da hukumomin tsaro ke dauka domin dakile ayyukan leken asiri da kuma kare sirrin gwamnati a Najeriya.

Me za ku ce?.

Sojoji Sun Dakile Harin Ƴan Ta’adda a KukaretaDakarun Operation HADIN KAI sun dakile wani harin ƴan ta’adda a Kukareta, ...
23/04/2026

Sojoji Sun Dakile Harin Ƴan Ta’adda a Kukareta

Dakarun Operation HADIN KAI sun dakile wani harin ƴan ta’adda a Kukareta, inda s**a kashe ƴan ta’adda 24 tare da kwato makamai da dama.

Harin ya faru ne da sanyin safiyar 23 ga Afrilu, 2026, amma dakarun rundunar karkashin Sector 2 sun yi gaggawar mayar da martani, lamarin da ya tilasta maharan janyewa.

Kakakin rundunar Laftanal Sani Uba ya shaidawa Dimokuraɗiyya Tv cewa an kwato bindigogi kirar AK-47, manyan bindigogi, RPG, motoci da kuma alburusai masu yawa.

An kuma jikkata sojoji biyu, amma suna samun kulawa, yayin da wata mota mai sulke ta samu matsala.

Hukumomin soji sun ce ana ci gaba da farautar ƴan ta’addan domin tabbatar da tsaron yankin baki daya.

Shugaba ​Tinubu Ya Ware Biliyan 17 Domin Bunƙasa Cigaba da Walwalar al'umma a Mazabu 8,804 na Najeriya​Shugaba Bola Ahme...
22/04/2026

Shugaba ​Tinubu Ya Ware Biliyan 17 Domin Bunƙasa Cigaba da Walwalar al'umma a Mazabu 8,804 na Najeriya

​Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da fitar da kudi naira biliyan 17 domin gudanar da wani babban shiri na samar da ci gaba a matakin mazabu (Wards) da ke faɗin ƙasar nan.

​Wannan tallafi, wanda aka yi wa laƙabi da "Community-Based National Social Action Fund", an kafa shi ne domin taba rayuwar talakawa kai-tsaye a dukkanin mazabu 8,804 na Najeriya, ta hanyar ba su damar gudanar da ayyukan da s**a fi damunsu a yankunansu.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Lafiya da Walwalar Jama’a ta Tarayya ta fitar ranar Laraba, wadda mataimakin daraktan yaɗa labarai, Ado Bako ya sanya wa hannu, an bayyana cewa kowace mazaba za ta haɗa gwiwa ne da ƙungiyoyin sa-kai na cikin gida (CBOs) domin gano ayyukan da s**a fi buƙata.

​Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya bayyana cewa wannan sabon salo ne na mika mulki ga talakawa. Ya ce, "Wannan tsari ya sanya al'umma a gaba wajen neman ci gaba. Ta hanyar barin kowace mazaba ta zaɓi abin da ya fi damunta, muna buɗe hanyoyin samar da maslaha da za su inganta rayuwa da kuma ayyukan gwamnati a inda aka fi buƙata."

Sanarwar ta nuna cewa za a kashe kuɗaɗen ne a fannonin da s**a haɗa da​Samar da abinci mai gina jiki ga al'umma, ​Samar da magunguna da kayayyakin kiwon lafiya, ​Gyaran makarantu, asibitoci, da samar da tsarin tsaftar muhalli.

​An tsara cewa za a fara aiwatar da wannan shiri ne daga ranar 1 ga watan Maris, 2026 zuwa watan Disambar 2026, inda Ma’aikatar Kuɗi da Ofishin Akanta-Janar na Ƙasa za su kula da asusun da aka ware wa shirin.

A wani labarin kuma mai alaƙa da wannan, Shugaba Tinubu ya amince da ɗaga matsayin Cibiyar Horar da Masu Maganin Kanjamau da Kuturta ta Ƙasa (NTBLTC) da ke Zariya, zuwa matsayin Babbar Cibiyar Bincike da Kula Lafiyar Jama'a da Cututtuka Masu Yaduwa (National Institute of Public Health and Infectious Diseases).

​Wannan mataki na nufin mayar da cibiyar ta Zariya ta zama tungar bincike, horarwa, da kuma shirin taryar duk wata annoba ko barazanar cututtuka da ka iya ɓallowa a ƙasar nan.

Hotuna: Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya gana da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Ebele Jonathan, a fadarsa da ke A*o Ro...
22/04/2026

Hotuna: Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya gana da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Ebele Jonathan, a fadarsa da ke A*o Rock Villa.

📷 Bayo Onanuga

Karfafa Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Masu Aiki Da Gas (CNG)A wani gagarumin mataki na zam...
22/04/2026

Karfafa Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Masu Aiki Da Gas (CNG)

A wani gagarumin mataki na zamanantar da aikin dan sanda da rage radadin tsadar man fetur, Gwamnatin Tarayya ta mika wa Rundunar ’Yan Sandan Najeriya (NPF) wasu manyan motocin bas guda uku masu amfani da iskar gas (CNG).

Wannan tallafi, wanda ya fito ne ta hannun Asusun Tallafawa ’Yan Sanda (NPF-TF) da kuma Kwamitin Shugaban Kasa kan Motocin Gas da Lantarki (PI-CNG & EV), an mika shi ne a ranar Laraba a helkwatar rundunar da ke Abuja.

Sufeto Janar na ’Yan Sanda, IGP Olatunji Rilwan Disu, ya bayyana jin dadinsa ga wannan hangen nesa na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana cewa, Wannan canji zuwa amfani da makamashin gas da lantarki wani muhimmin mataki ne da zai sanya aikin dan sandan Najeriya ya tafi daidai da yadda ake yi a kasashen da s**a ci gaba.

“Za a yi amfani da wadannan motoci ne domin inganta walwalar jami’ai da kuma saukaka zirga-zirgarsu yayin gudanar da ayyukan tsaro.” Inji shi.

Rundunar tana shirin samar da cibiyoyin canza fasalin motoci (conversion centres) a cikin gida domin su rika gyara da kuma kula da motocin da kansu.

Shugabannin hukumomin biyu, a karkashin jagorancin Sakataren NPF-TF, Mohammad Sheidu, da Shugaban PI-CNG & EV, Barista Ismail Ahmed (OON), sun tabbatar da cewa wannan somin-tabi ne.

"Wannan mataki na daya ne daga cikin babban shirin Gwamnatin Tarayya na sauya fasalin dukkan motocin aiki na ’yan sanda zuwa masu amfani da iskar gas (CNG). Wannan zai rage kudin da ake kashewa wajen sayen man fetur da kusan kashi 50% ko fiye da hakan."

Taron ya samu halartar manyan jami’ai daga hukumomin biyu, ciki har da CP Tony Emafale, Alhaji Sanusi Aliyu, da sauran wakilai daga bangaren kwamitin CNG na fadar shugaban kasa.

Wannan hadin gwiwa wata hujja ce dake nuna yadda Gwamnatin Tarayya take jajircewa wajen samar da ingantattun kayan aiki ga hukumomin tsaro ta hanyar amfani da fasahar zamani mai rahusa kuma marar illa ga muhalli.

Matakin zai kara wa rundunar karsashi wajen kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya a wannan sabon zamani.

HOTUNA: Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Kakakin Majalisar Wakilai,Tajuddeen Abbas; Ministan Labarai da...
22/04/2026

HOTUNA: Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Kakakin Majalisar Wakilai,
Tajuddeen Abbas; Ministan Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris; tare da sauran manyan baƙi a wurin taron Makon Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya (Nigerian Institute of Public Relations, NIPR), karo na 3, a Kaduna. An gudanar da taron ne ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, wanda kuma aka ba shi lambar girmamawa ta Gwarzon NIPR (Fellow).

Bikin ya gudana a sabon zauren liyafa na Birgediya Abba Kyari wanda aka ƙaddamar, a Gidan Sa Kashim Ibrahim, wato Fadar Gwamnatin Jihar Kaduna, a ranar 21 ga Afrilu, 2026.

Alhamdulillah, Yanzu jihar Kano za a san ana mulkin dimokiradiyya, Domin an zaɓo mataimakin gwamnan da ba a taɓa yin iri...
22/04/2026

Alhamdulillah, Yanzu jihar Kano za a san ana mulkin dimokiradiyya, Domin an zaɓo mataimakin gwamnan da ba a taɓa yin irin sa ba - Inji Engr. Miqdad Yusuf Chiranchi

Ba na goyon bayan shugaba Bola Ahmad Tinubu, amma bai kamata mulkin Najeriya ya dawo arewa a 2027 ba - Inji Dr. Mu'azu B...
22/04/2026

Ba na goyon bayan shugaba Bola Ahmad Tinubu, amma bai kamata mulkin Najeriya ya dawo arewa a 2027 ba - Inji Dr. Mu'azu Babangida Aliyu, tsohon gwamnan jihar Neja.

Me za ku ce?

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya soki ƴan adawa inda ya zarge su da rashin gaskiya wajen bin tafarkin dimokuraɗiyya, duk d...
22/04/2026

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya soki ƴan adawa inda ya zarge su da rashin gaskiya wajen bin tafarkin dimokuraɗiyya, duk da cewa suna ikirarin suna goyon bayanta.

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin da ya karɓi tawagar shugabannin siyasa daga jihar Enugu ƙarƙashin jagorancin gwamna Peter Mbah a fadar sa da ke Abuja.

Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Ofishin APC a Taura, Ya Karɓi Sabbin MambobiGwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, Ya kai ziyar...
22/04/2026

Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Ofishin APC a Taura, Ya Karɓi Sabbin Mambobi

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, Ya kai ziyara ƙaramar hukumar Taura domin ƙaddamar da ofishin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar APC tare da karɓar sabbin mambobi daga jam’iyyun NNPP da PDP.

Daga cikin waɗanda s**a sauya sheƙa har da tsohon ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Taura/Ringim, Safiyanu Ubale Taura, wanda ya zo tare da magoya bayan sa.

A wajen taron, wanda Mataimakin Gwamna, Aminu Usman, Ya halarta, an nuna goyon baya ga manufofin gwamnati tare da maraba da sabbin ƴan jam’iyyar, Kuma gwamnan ya jaddada muhimmancin haɗin kai da aiki tare domin ci gaban jihar, yana mai kira ga al’umma da su ci gaba da mara wa gwamnati baya.

DA ƊUMI-ƊUMI: Umar Muda Lawal Ya Yi Kira Ga Al’ummar Bauchi Su Mara Wa Shehu Buba Baya A Takarar GwamnaTsohon dan majali...
22/04/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Umar Muda Lawal Ya Yi Kira Ga Al’ummar Bauchi Su Mara Wa Shehu Buba Baya A Takarar Gwamna

Tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar Toro Federal Constituency, Umar Muda Lawal, ya yi kira ga al’ummar Bauchi State da su mara wa Shehu Buba baya a kudirinsa na zama gwamnan jihar.

Yayin da yake magana a wata hira da tashar DCL Hausa TV, ya ce Sanata Shehu Buba ya nuna kyakkyawan jagoranci da jajircewa ta hanyar aikinsa na wakiltar Bauchi South Senatorial District.

Umar Muda Lawal ya bayyana cewa nasarori da jajircewar da sanatan ya nuna wajen kawo ci gaba sun nuna cewa yana da kwarewa da cancantar jagorantar jihar Bauchi zuwa gagarumin ci gaba.

Saboda haka ya bukaci al’ummar jihar da su hada kai domin mara wa kudirin takarar gwamnan Shehu Buba baya.

Address

Sheikh Ja'afar Mahmud Adam Road, Dorayi
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskira H Online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share