Taskira H Online TV

Taskira H Online TV Taskira H Online TV, Kafa ce da ke kawo muku sahihan labarai daga sassa daban-daban na duniya, za ku iya turo mana labarin domin sanar da al'umma kai tsaye!
(1)

Sheik Lawal Triumph Ya Kaiwa Sheik Sani Yahaya Jingir Da Tawagarsa Ziyara A Masaukinsa Dake Saudiyya A Yayin Da S**a Je ...
29/10/2025

Sheik Lawal Triumph Ya Kaiwa Sheik Sani Yahaya Jingir Da Tawagarsa Ziyara A Masaukinsa Dake Saudiyya A Yayin Da S**a Je Umrah

Sojoji sun fara binciken zargin yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu inda s**a yiwa gidan tsohon Gwamnan Bayelsa ƙawanya M...
29/10/2025

Sojoji sun fara binciken zargin yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu inda s**a yiwa gidan tsohon Gwamnan Bayelsa ƙawanya

Masu bincike na rundunar soji sun tsare wani Daraktan Gudanarwa na hukumar gwamnatin tarayya da ke Kudu maso Kudu bisa zargin hannu a cikin shirin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Rahotanni sun ce an k**a shi ne bayan ya aika da kuɗi masu yawa zuwa ga tsohon karamin Ministan Harkokin Mai, Timipre Sylva, wanda ake zargin yana daga cikin masu tallafawa juyin mulkin.

Majiyoyi sun bayyana cewa an kai samame gidan Sylva da ke Abuja a ranar Asabar, inda aka k**a ƙaninsa, Paga, da direbansa, yayin da shi Sylva ke ƙasashen waje.

An ce ya fasa dawowa Najeriya bayan samun labarin k**a shugabannin juyin mulkin.

Sai dai jami’an hulɗa da jama’a na rundunar soji, Manjo-Janar Markus Kangye da Birgediya-Janar Tukur Gusau, ba su amsa kiran wayar ‘yan jarida ba kan batun.

A baya, rundunar soji ta tabbatar da tsare jami’ai 16 saboda karya dokokin aiki da rashin ladabi, amma rahoton SaharaReporters ya nuna cewa jami’an daga matakin Kyaftin zuwa Birgediya-Janar ne ake zargin suna shirin kifar da gwamnati.

A lissafin gidan yari, shekara daya ba watanni 12 bace, kimanin watanni 8 ne. Saboda haka, tunda Maryam Sanda ta shafe c...
29/10/2025

A lissafin gidan yari, shekara daya ba watanni 12 bace, kimanin watanni 8 ne. Saboda haka, tunda Maryam Sanda ta shafe cikakkun shekaru 6 da watanni 8 din da Maryam Sanda a gidan yari, idan aka juya su zuwa shekarun gidan yari, zai kai kusan shekaru 10.

Tunda yanzu shugaban kasa ya maida zaman gidan yarin da zata yi zuwa shekaru 12, kuma tayi 10 (a lissafin gidan yari), shekaru 2 da s**a rage, ba su wuce watanni 16 ba.

Saboda haka, ka iya cewa nan da shekara 1 da watanni 4 Maryam Sanda zata shaki iskar yanci.

Inji Lauya Abba Hikima

IKON ALLAH: Cikin Shekara Biyu Wannan Dan Majalisar Ya Murmure Ya Koma HakaDan majalisar jiha ne da yake wakiltar karama...
29/10/2025

IKON ALLAH: Cikin Shekara Biyu Wannan Dan Majalisar Ya Murmure Ya Koma Haka

Dan majalisar jiha ne da yake wakiltar karamar hukumar Nguru a jihar Yobe, wato Honarabul Musa Lawal Maja Kura, a cikin shekaru biyu kacal da hawan sa kujerar amma kun ga yadda rayuwarsa ta sauya.

Nan hotunansa a lokacin da yake koyarwa a makaranta da sana'ar POS, da kuma bayan ya zama dan majalisa.

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan takardun bayar da afuwa da sassauci ga wasu mutane da aka yanke wa hu...
29/10/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan takardun bayar da afuwa da sassauci ga wasu mutane da aka yanke wa hukunci, domin kammala aiwatar da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi na ba da afuwa. Wannan mataki, k**ar yadda fadar shugaban ƙasa ta bayyana, ya biyo bayan shawarar Majalisar Koli ta Ƙasa da kuma jin ra’ayoyin jama’a kan batun.

Bisa sabuwar duba da aka yi, an cire sunayen mutanen da aka samu da manyan laifuka irin su satar mutane, safarar miyagun ƙwayoyi, zamba, cinikayyar mutane da mallakar mak**ai ba bisa ka’ida ba daga jerin waɗanda za su ci gajiyar afuwar. Haka kuma, wasu daga cikin waɗanda aka yiwa afuwar a baya, an sauya hukuncinsu zuwa ɗaurin rai da rai ko wasu sassauci masu tsanani. Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa wannan mataki yana da nasaba da la’akari da tsaron ƙasa, mutuncin waɗanda abin ya shafa da kuma ƙarfafa hukumomin tsaro.

Shugaba Tinubu ya kuma bayar da umarni a maye gurbin Ofishin Hukumar Ba da Afuwa daga Ma’aikatar Harkokin Musamman zuwa Ma’aikatar Shari’a, domin tabbatar da ingantaccen tsarin aiki a nan gaba. Ya kuma umarci Babban Lauyan Ƙasa da ya samar da ƙa’idoji da s**a haɗa da shawarar hukumomin tuhuma kafin bayar da kowane irin afuwa. Shugaban ƙasa ya gode wa jama’a bisa goyon baya da shawarwarinsu, tare da jaddada aniyarsa ta ci gaba da gyaran tsarin shari’a da inganta gaskiya da adalci a Najeriya.

Ba a tauye ’yancin addini a Nijeriya, inji  Ministan Yaɗa Labarai a hirar CNNMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alha...
29/10/2025

Ba a tauye ’yancin addini a Nijeriya, inji Ministan Yaɗa Labarai a hirar CNN
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ƙara maida hankali wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan domin tabbatar da tsaro da walwalar ’yan ƙasa.

Da yake magana a cikin wata hira da gidan talbijin na CNN ya yi da shi a London a daren Talata, Idris ya ƙaryata iƙirarin da wasu jami’an ƙasashen waje suke yi cewa wai ’yan ta’adda a Nijeriya suna kai hare-hare ne kan Kiristoci kawai.

Ya bayyana cewa irin waɗannan iƙirari ba su da tushe kuma ba su bayyana haƙiƙanin yanayin tsaron ƙasar nan, inda ya jaddada cewa ’yancin yin addini yana cikin kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Ya ce: “Wasu daga cikin iƙirarin da wasu jami’an Amurka s**a yi sun ta’allaƙa ne kan bayanai marasa inganci da kuma zato cewa yawancin waɗanda ake kai wa hare-hare Kiristoci ne. E, ana kai wa Kiristoci hari, amma waɗannan miyagun ba mabiya addini ɗaya kawai suke kai wa farmaki ba. Suna kai wa Kiristoci hari, suna kuma kai wa Musulmi hari, musamman a arewacin ƙasar.”

Idris ya ce masu yaɗa irin waɗannan labaran ƙaryar suna taimaka wa ’yan ta’addar ne, saboda manufar ’yan ta’adda ita ce su haddasa rikici tsakanin Musulmi da Kiristoci a ƙasar.

Ya ƙara da cewa Nijeriya ƙasa ce da ta yi yarda da bambancin addinai, don haka yaɗa labaran ƙarya na nuna rashin jituwa zai iya haifar da rarrabuwar kai.

Ya ce: “Kiran lamarin da cewa hare-haren kan Kiristoci ne kawai zai iya haifar da rarrabuwar kai a Nijeriya. Miyagun suna son a ɗauka k**ar ana faɗa ne tsakanin Musulmi da Kiristoci. Mun shaida akwai hare-hare kan Kiristoci, kuma mun shaida akwai hare-hare kan Musulmi. Amma ba daidai ba ne a ce Nijeriya ƙasa ce da ba ta mutunta ’yancin addini, ko a ce ko'ina babu tsaro a Nijeriya. Nijeriya ƙasa ce mai aminci.”

Ministan ya amince cewa akwai matsalolin tsaro, amma kuma gwamnati tana ɗaukar matakai masu ƙarfi da tsari don magance su.

Ya bayyana cewa gwamnati ta ƙarfafa rundunonin tsaro tare da zuba jari a fannoni k**ar noma da ayyukan jinƙai domin ƙarfafa zaman lafiya.

Ya ce: “Ko canje-canjen da aka yi na shugabannin hafsoshin tsaro kwanan nan duk don a ƙarfafa tsarin tsaron ƙasar ne, domin gwamnati ta iya magance kowace irin matsala a kan lokaci.”

Gwamnatin Katsina Ta Kafa Kwamitin Duba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Tsakanin Yan Bindiga Da Al’ummomin Yankunansu Gwamnati...
29/10/2025

Gwamnatin Katsina Ta Kafa Kwamitin Duba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Tsakanin Yan Bindiga Da Al’ummomin Yankunansu

Gwamnatin Jihar Katsina karkashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umar Radda ta kafa wani kwamiti na musamman da zai duba yarjejeniyar zaman lafiya da aka kulla tsakanin barayin daji da al’ummomin yankunan da ke fama da matsalolin tsaro a fadin jihar.

An kafa kwamitin ne a ranar Talata, 28 ga watan Oktoba, 2025, karkashin jagorancin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Alhaji Abdullahi Garba Faskari, wanda ya jagoranci taron kafa kwamitin tare da kaddamar da ayyukansa.

Kwamitin, wanda Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Katsina zai jagoranta, ya ƙunshi wakilai daga muhimman hukumomin tsaro da sassan gwamnati. Ciki har da Kwamishinan Harkokin Tsaro na Cikin Gida na Jihar Katsina wanda zai kasance Sakataren kwamitin, da kuma wakilai daga rundunar Sojoji ta 17 Brigade, da 213 Forward Operation Base (FOB), da hukumar ‘Yan Sanda Farin Kaya, da wakilci daga Babbar Kotun Jihar Katsina, da wasu muhimman hukumomi.

Manufar kafa kwamitin ita ce duba yadda aka gudanar da yarjejeniyar zaman lafiya, da kuma bayar da shawarwari ga gwamnati kan matakan da za su tabbatar da dorewar yarjejeniyar da kuma tabbatar da cikakken zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.

A yayin kaddamar da kwamitin, Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Abdullahi Garba Faskari, ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin dabarun Gwamna Radda na tabbatar da tsaro da zaman lafiya mai dorewa a jihar.

Ya ce, “Gwamnatin Katsina ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin cewa an samu zaman lafiya mai dorewa a dukkan yankuna. Wannan kwamiti zai bayar da cikakken rahoto cikin makonni biyu masu zuwa domin samar da sahihan matakai na ci gaba.”

Kwamitin zai fara aikin sa nan take, tare da ziyarar sassan da s**a fi fuskantar matsalar tsaro domin tattara bayanai kai tsaye daga al’ummomin da abin ya shafa.

Zuwa yanzu, gwamnatin jihar ta nuna jajircewarta wajen haɗa kai da hukumomin tsaro da shugabannin al’umma don tabbatar da dorewar zaman lafiya a fadin Katsina.

Daga Muhammad Ali Hafizy, Katsina Times
Katsina – Talata, 28 Oktoba, 2025

Hukumar Tsaro ta DSS ta k**a wani mutum da ya yi kira ga rundunar sojin Najeriya da ta kifar da gwamnatin Shugaba Tinubu...
29/10/2025

Hukumar Tsaro ta DSS ta k**a wani mutum da ya yi kira ga rundunar sojin Najeriya da ta kifar da gwamnatin Shugaba Tinubu.

Mutumin wanda ke zaune a garin Fatakwal na Jihar Ribas ya yi kira da sojojin da su kifar da wannan gwamnati ne a shafinsa na “X” mai suna , Innocent Chukwuma.

Ya ce ana buƙatar juyin mulki a Najeriya tare da kira ga sojoji su kifar da gwamnatin Tinubu.

DA ƊUMI-ƊUMIN SA: Ya k**ata gwamnati ta samar da hukumar ta tantance masu Wa'azi a ƙasar, duba da irin abubuwan da suke ...
29/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMIN SA: Ya k**ata gwamnati ta samar da hukumar ta tantance masu Wa'azi a ƙasar, duba da irin abubuwan da suke faruwa - Inji Farfesa Sheikh Isa Ali Pantami

Kada Ku Kasance 'Yan Amshin Shatan Shugaban Ƙasa, Ku Zama Masu Faɗa Masa Gaskiya Tare Da Ba Shi Shawarwarin Hanyoyin Da ...
29/10/2025

Kada Ku Kasance 'Yan Amshin Shatan Shugaban Ƙasa, Ku Zama Masu Faɗa Masa Gaskiya Tare Da Ba Shi Shawarwarin Hanyoyin Da Za A Bi Don Ciyar Da Tattalin Arzikin Ƙasar Nan Gaba, Saƙon Sarki Sanusi II Ga Ministoci Da Sauran Mukarraban Shugaba Tinubu

Me zaku ce?

A makon da ya gabata ne aka zaɓi Kwamared Nasir S Isah, Ɗaya daga cikin abokan hulɗar Taskira H Online TV a matsayin "Le...
29/10/2025

A makon da ya gabata ne aka zaɓi Kwamared Nasir S Isah, Ɗaya daga cikin abokan hulɗar Taskira H Online TV a matsayin "Legal Advisor" na ƙungiyar ɗalibai ta National Association of Nigeria Student (NANS ), Reshen jihar Kano.

Muna taya shi murna, Allah Ta'ala ya riƙa ya basu ikon sauke nauyin da ke kan su, Amin

Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Muhammadu Sanusi II, Ya ce bai dace gwamnatin Shugaban Kas...
29/10/2025

Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Muhammadu Sanusi II, Ya ce bai dace gwamnatin Shugaban Kasa Bola tinubu ta ci gaba da ciyo bashi ba bayan ta cire tallafin man fetur.

Yayin da yake jawabi a Abuja ranar Talata, a taron Oxford Global Think Tank Leadership da ƙaddamar da wani littafi, Sanusi ya ce cire tallafin man ya haifar da ƙaruwar kuɗaɗen shiga na gwamnati.

Sanusi ya kuma yaba wa gwamnatin Tinubu kan cire tallafin man fetur da daidaita farashin musayar kuɗi, yana mai bayyana matakan a matsayin masu raɗaɗi amma na wajibi.

Sai dai ya yi gargaɗin cewa waɗannan gyare-gyare ba za su yi tasiri ba sai an haɗa su da tsari mai kyau na kashe kuɗi da gaskiya a cikin gudanar da gwamnati.

In ka daina biyan tallafi amma ka ci gaba da yin rance, hakan na nufin ka rufe rami guda ne sai ka buɗe wani. Kalubalen da ke gabanmu yanzu shi ne ingancin yadda gwamnati ke kashe kuɗi da kuma yadda ake tafiyar da kuɗaɗen da aka ce an ajiye, in ji shi.

Sanusi, wanda ya jagoranci CBN daga 2009 zuwa 2014, ya ce matsalolin tattalin arzikin Najeriya a yanzu sun faru ne a sak**akon rashin daidaito a manufofi da siyasar neman sai an faranta wa jama’a da aka dade ana yi.

Address

BUK Road
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskira H Online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share