Mr.perfection novels

Mr.perfection novels BOOK📚
STROY WRITER ✒📙
MUSLIM 👤❤
20🌹❤

04/08/2025

*A GIDAN AUREN NA*👰‍♀️🤵👩‍❤️‍👨

*( in my marital home )*

https://chat.whatsapp.com/EoKZbPkphsuJIxZECUVZlE

*_Stroy and writing_*
by
*_Seven star writer’s_*

______________________________________________________________________________________
Wani Littafi ne dake cike da ƙalu b***n da ake fuskanta a gidan auren........
____________________________________________________________

An rubuta wannan littafi ne karkashin jagorancin kungiyar:

🖋 TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOATION 💫

Team ɗin da ke da alhakin wannan aikin:

✨ SEVEN STAR'S WRITER'S TEAM ✨
______________________________________________________________________________

Membobin cikin ta:

1. [Rukayya Yusuf Ibrahim (CEO A Y M place)]

2. [Hussaina Abdullahi (Oumu Muwaddah)]

3. [Salamatu Hussaini (Queen Bee ko Àutar mama)]

4. [Fatima .Y. Zakariyya(Tymer's Henna)]

5. [Sani Muhammad Lawan (S M Lawan )]

6. [Maijidda Bashir Sharu (Jidda Pretty )]

7.⁠ [Hadizatu mrs kd]
___________________________________________________________________

[Page 2]

Tagumi Fatima ta zuba dan tasan komi zata gayawa Hauwa da Aisha ba lallai su yarda ba, kallon su tasake yi cikin nutsuwa sanan tace.

“Haƙuri dai wanda kika ji nafaɗa.“

Tsaki Aisha ta ja tare da cillawa Fatima harara.

“with due respect ƙarya k**e Fatima duk soyayyar da ake sha a waje, sanan ace hakuri za’ayi a ciki”

“faɗa mata dai Aisha, ya za'ai ce haƙuri ake a gidan auren, ina amfanin soyayya da kalaman soyayya?.”

Hauwa tafaɗa tana harar Fatima da tayi magana.

Sadiya ce tace.

“Wallahi Allah Aisha maganar Fatima tana kan dai-dai, dan nasha karo aciki wasu litatafai na manyan marubuta masu fasaha,da fikira wanda ko da a zahiri sunsan ilimin aure dan wasu zasu haifi k**ar mu kin ga kuwa suna da Experience”

Hauwa da maganar Sadiya take ɓatawa rai ta taɓe baki sanan tace.

“Ko jikina kunene sai dai ki barni dan Gidan Habibi duniya ne”

A fusace Fatima tace.

“Tom Shikenan Hauwa amma ku sani A matsayina na na marubuciya, ina da experience da yawa akan rayuwar Aure.”

“uhm sannu marubuciya! fad’amana experince ɗin naki.”

Zainab ta faɗa tare da ta sakkowa zuwa inda suke, gyara zama Fatima tayi sanan tace.

“A iya nazari na, da tunani na Aure ba abunda zaku yi tunanin kasancewa cikin farin ciki a ko da yaushe bane, Aure zamane da ake fatan yin shi har abada, to harshe da hak’uri ma ana saɓawa b***e mutane Yan adam da muke tara bamu cika goma ba”

“Ban tari numfashin ki ba Fatima Amma kina nufin ba’a samun soyayya a gidan Aure?.”

Zainab da ta taso tadawo cikin su ta tambaya.

“Ban isaba Zainab! ban isa nace a gidan aure ba a samun soyayya ba, amma tabbas soyayyar da kika yi tunani ko kika samu a waje ba ita ake samu a gidan aure ba, saboda haka ban ɗorawa raina ba,tunda har yanzu banyi aure ba.

“Maganar Fatima tana kan dai dai, k*ma hakan yana cikin abubuwan da yasa nakai aure last plan ɗina, naga aure da dama wa ɗanda ba in da suke zuwa, wasu k*ma ana tare amma kullum cikin tashin hankali, mazaje na wahalal dasu wasu k*ma matayen ke wahalal dasu idan sunga sunfi rufim asiri.”

Zainab tafad’a tana kallon su, sai da ta gama kallon tsaf sanan ta d’ora da cewa.

“Ina da burin nayi karatu mai zurfi, na zama babbar mace wanda ko da nayi aure mijina ba zai kalleni da rashin daraja ba acikin Gidan Aure na ba, yiwa yarinya Aure a ƙananu shekaru bashi da amfani.”

“Tabbas Zainab tunda ake maganar Aure baki taɓa ta hankali ba sai yau.”

Cewar Rabi'ah k**ar masu jira Rabi'ah ta tsagaita s**a fashe da dariya baki ɗayan su.

Daga nan k*ma hirar tasu ta koma kan ƙalub***n Gidan Aure har zuwa sanda bacci ya fara ɗauke su.
________________________________________________________________

Tsaye suke cikin compound ɗin school ɗin gaban su cike da trolleys da sauran kayayyakin su.

Sak**akon k**allh pepar ƙarshe k*ma yau duk wani wanda ya gama GGSS ZARIA, Aji na Shida yake komawa gida.

Fatima ce cikin Muryar kuka tace

“I wished aure ya kawo ni kano ko kaduna ko zaria, saboda na dinga ganin ku a ko yaushe.”

Dariya Sadiya tayi sanan tace.

“Aifa mu nan duk kusa muke, ke kaɗai ce kika luluƙa can katsina”

“Shiyasa ai duk nafi damuwa saboda nasan ganin ku sai dai nina zo, amma ko kam babu wacce za tazo Tudun Matawale”

“Haba darling sis! ya za’ai kice haka zamu haɗu sosai, yanzu ga bikin sister Rabi'ah nan,promised you inda kika zo bikin sister Rabi'ah zan biki muje Tudun Matawale insha Allah,

amma sai kin fara zuwa gidan mu kin kwana biyu bayan biki.”

cewar Jamila kenan, rungume ta Fatima tayi sanan tace

“shikenan darling sis.”

cikin muryar kuka.

Matsowa zainab tayi ta rumgume su tace.

“ I love you girls wallahi nasan zanyi kewar ku, waya ko group chat bazai ɗebemun kewarku ba.”

Haka sauran s**a marmatso s**a rungume juna suna hawaye,

students s**a tsaya suna kallon su wasu harda tayasu kukan, domin kowa yasan irin alaƙar dake tsakanin saven stars, ko irin munafuncin nan da akeyi na cikin ƙawaye to su basu.

Malam Madu driver school ne mai kai daliban kano, shine yayi musu sallama tare da cewa.

“ To 'yan bakwai abani tagawaye na nahuce dasu.”

Dariya s**a yi dukkan su sanan su Aisha da Hauwa s**a fara ɗaukan kayansu.

“Am Baba madu ko zan biko ku sauke ni a Zaria.”

Jamila tafaɗa cikin zolayar da duk hutu sai ta tsokani Baba Madu.

“Ai fa sai dai Zaria Jamsee”
Cewar Zainba da ta kin-kimi tata trolley da zumar ta matsa daga guri.

Dariya Baba Madu yayi ya ɗauki kayan Aisha dana Hauwa ya dubi Jamila.

“Badamuwa ɗako kayan naki.”

Ya faɗa yana nufar inda motar sa take ajiye.

Muryar Zainab s**a ji tana fad’in

“Kutumar uba! Auzubillahi.”

ta haɗe a lokaci guda.

“Ke zainab lafiyan ki? k**e wa mutane zagi k**ar arniya.”

Sadiya ta faɗa tana kallon zainab

“Uhm Sadiya barni bakisan masifar da na gano ba.”

tana mai komawa inda Rabi’ah ke tsaye

“Ke rabi kalli.”

Zainab ta faɗa tana nuna inda mota ke shigowa

“Auzubillahi yau ranar ƙarshen ma sai an turo mana tashin hankali.”

Dariya su Hauwa s**a fashe da ita dan su gano abinda ya tsorata Zainab yasa ta zagi sanan ya ki ɗima rabi.

YAYA SAIYYID

dodon Zainab da Rabi kenan

“Kunga girls, sai mun
haɗu ban shirya karɓar tashin hankali ba.”

Zainab ta faɗa tana fara jan trolley ɗin da wasu kayan ta

k’ame wa tayi cak hango mutumin da tafi jin haushi a duniya.

______________________________

Daga cikin mota kam Saiyyid ne ya kalli Jawad yace.

“i’m always telling you ka fita sabgar marasa kunyar yaran nan amma kaƙi gashinan yarinya na ganin ka har ta haɗe rai saboda raini, ko mene abun burgewa a tare da ƙana nan yara oho?.”

“Buddy ba abin da zaka gane amma tabbas ƙananan yara sunfi daɗi soyayya, iya kulawa da mutunta miji ina son *A Gidan Aure na* nakasance Sarki ko na kasance Yariman da ake lallaɓawa.”

Jawad ya bawa Saiyyid amsa yana ƙoƙarin buɗe murfi motar ya fita.

“Jawad dan allah ka dinga k**a kanka a gaban yaran nan kar su raina ka fa.”


Bai bashi amsa ba ya bud’e mota ya fice, Zainab da tayi tsayuwar dole ta fara ƙok’arin had’e kayanta, daga can gefe k*ma Rabi ce tace dasu.

“Kuzo na baku gulma ta k’arshe a GGSS.”

Da sauri s**a tawo tare da cewa

“All ears with you.”

“Kunga wanan Yaya Jawad d’in abokin Yaya saiyyid ne, tun muna 'yan ƙanana yake mugun son Zainab, ita kam a rayuwar ta babu wanda ta tsana k**ar shi, ba wai k*ma shine kad’ai ta tsana ba duk wanda zai zo mata da maganar soyayya zainab ta tsane shi, kunsan wanda zan aura ɗan gidan chairman ne! kunga dai suna da kuɗi iya ka cik kud’i to wallahi sanda brother d’inshi ya nuna yanason zainab tun daga nan ta tsaneshi, zainab ta d’auki duniya da zafi akan aure yanzu ku tsaya kuga yanda zata kaya da Zainab da Yaya Jawad.”

Jamila ce tace.

“nikam yanzu bana ganin laifin Zainab tunda a jiya tafad’a mana dalilin ta.”

“Amma hakan ba ya bata dama ta dinga yiwa mutane rashin kirki ba, kiga sanda wanan copper d’in yace yana sonta.”

Hauwa tafad’a cikin ɓacin rai domin tabbas zainab ta fara kaita bango akan wanan mummunar ɗabi’ar tata.



“Zainab ba tada lissafin aure to mu kyale ta dan allah kowa dai yana da ra’ayin shi.”

Fatima tafad’a tana cigaba da haɗe kayanta wands take jiran drive da yake ɗaukar ɗaliban daga Zaria zuwa katsina.

A hankali ya tako zuwa inda take.

“Congratulations queen 👸 yanzu an kammala secondary school.”

ya fad’a cikin wani irin kwantar da murya, a d’an ya tsine ta d’ago ta kalleshi sanan tace.

“Thanks Yaya.”

“let me help you with the luggages.”

ya fad’a yana k’ok’arin k**a mata kayan, bata hanashi ba ta sakar masa sanan ta koma dakko sauran kayan, shik*ma yayi mota da wayancan.

“Sannu bawan mata.”
Saiyyid ya fad’a dai dai lokacin da Jawad ya k’araso wajen rik’e da jakunkunan, bai ko kalleshi ba yace.

“malam fito ka bud’e mana musa kayan mu.”

“You dey craze! nine zan taka k’asar makarantar nan? tabbas kaci kai.”

Saiyyid ya fad’a in i don’t care, domin tabbas tunda Saiyyid yake zuwa d’aukan su Rabi da Zainab bai tab’a taka kafara sa a wanan makarantar ba.

“Kuzo muje ku gaida su mana.”

Rabi’ah tafad’a dai dai lokacin da zainab ta k’araso wajen.

“Kunji jiki manyan munafukai.”

Zainab ta faɗa cikin masifar da ta zame mata jiki.
Dariya s**a saki gaba d’ayan su, sanan s**a taimaka musu wajen d’aukan ragowar kayan banda Sadiya da taji wani irin bugu da zuciyar ta wanda gaba ɗaya ya gama tsorata ta

“Sadiya ba zaki tawo bane.”

Fatima ta fad’a ganin duk sun tafi sun barta tsaye.

Sauri taita k’araso inda suke s**a taka.

Kamar kullum dai ba sakin fuska haka ya amsa.

Jawad ne dai sai da s**a gaji da magana ma.

___________________________________________

Lokaci da Rabi'ah da Zainab s**a bar makaran tar Babu wanda bai kuka ba.

Har get s**a bi motar suna musu bye bye..

Kafin s**a dawo suna tsaiwa motar da Zata kai Su Fatima katsina tazo.

Haka Aunty Hanney tazo da Keke napep ɗaukar Jamila.

A tare kowa ya shiga nasu Abin hawar dan k**a han yar garin su......


*Me yake jiran seven stars a gida?.”*

Karatu ne ko aure.

“Uhm this is just the beginning.”

Komai bai fara ba, wanan farkon farko ne.

*Daga zuk’atan mu zuwa shafinku*

Reaction da comment sune k’arfin gwiwar mu

Lallai saven star’s suncika taurari.

04/08/2025

A GIDAN AUREN NA👰‍♀️🤵👩‍❤️‍👨

*( in my marital home)*

https://chat.whatsapp.com/EoKZbPkphsuJIxZECUVZlE

*Stroy and Writing*
by
*Seven star writer’s*

_______________________________________________________________________________________

Wanan Littafi ne dake cike da ƙalu b***n da ake fuskanta a rayuwar gidan auren……….........
_______________________________________________________________________________________________________________________________________________

An rubuta wannan littafi ne karkashin jagorancin kungiyar:

🖋 TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOATION 💫

Team ɗin da ke da alhakin wannan aikin:

✨SEVEN STAR WRITERS TEAM✨

__________________________________________________________________________________

Membobin cikin ta:

1. [Rukayya Yusuf Ibrahim (CEO A Y M place)]

2. [Hussaina Abdullahi (Oumu Muwaddah)]

3. [Salamatu Hussaini (Queen Bee ko Àutar mama)]

4. [Fatima .Y. Zakariyya(Tymer's Henna)]

5. [Sani Muhammad Lawan (S M Lawan Hasken marubuta)]

6. [Maijidda Bashir Sharu (Jedderh pretty)]

7. (Hadizatu mrs kd)

____________________________________________________________________________________________________

Gabatarwa

Bismillahir-Rahmanir-Rahim
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

A GIDAN AUREN MU littafi ne da ya samo asali daga haɗin guiwar marubuta guda bakwai, waɗanda ke karkashin ƙungiyar “TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION”, a ƙarƙashin team ɗin"SEVEN STAR'S WRITER'S TEAM. Mun ɗauki wannan aiki ne domin kawo haske, ilmantarwa da k*ma nishadantarwa da nuna irin illar dake cikin rayuwar aure ta yau da kullum cikin hanyar da zata dace da al’adun mu da addini.

Wannan littafi zaiyi nuni da irin matsaloli da Ƙalubale da ake samu a cikin duniyar auren gaskiya na daga farin ciki, gwagwarmaya, har zuwa yadda soyayya ke girma da ƙarfafa cikin gida inshallah. Muna fatan ku ji daɗi da k*ma amfana da karantawa k**ar yadda mu muka ji daɗin rubutawa.

_________________________________________________________________________________

(Page 1)

*the beginning*

*GOVERNMENT GIRLS SECONDARY SCHOOL ZARIA*

Zaria gari ne dake da makarantar kwana mafi shahara ga 'yan mata masu burin zama ababen alfahari a rayuwar su.

Makarantar na na tsakiyar birni, cike da bishiyoyi masu inuwa da kwararan dokoki a kan kowanne ɗalibi,

*Cikin Makaranta*

Sautin karar motsin bel na daga kofar office ɗin Principal, da alama tashi aka yi break.

Wasu ƴan mata ne wainda baza su wuce shekara 18 ba, su bakwai suna tafiya cikin farin ciki wanda duk wanda yagan su yasan akwai alaka mai ƙarfi a tsakanin su.

Suna tafe suna dariya wata acikin su har da daukawa kasa tana dariya,

niko nace sai na leka naji mai suke ma dariya haka,ƙarasawa nayi cikin sauri domin naji mai suke cewa

Wata doguwa ce daga cikin su take bada labari tana cewa

"Ai ko jiya muna karatu a class shine malam Zubairu yake tambaya shin waye zai faɗa masa 5 pillars of Islam.
shine kafin nayi magana sarauniyar azarɓaɓi ta ɗaga hannu wallahi kowa yasha zata faɗi abin arziki kawai sai tace acikin akwai alwala,kiran salla,tsarki, har tana cewa akwai salati aiko anan ne kowa ya fara dariya to kusan halin malam Zubairu nan ya hana kowa yin dariya niko nakasa juriya wa na fashe da dariya shine yace in tashi in faɗa masa nace masa Zakka,hajji,azumin watan Ramadan,kalimatush shahada, sai salla
Ina gama faɗa yace clap for me nan ƴan aji s**a fara tafi ita k*ma yace ma sarauniyar azarɓaɓi "everybody clap for her misunderstanding and I hope kinji gyaran ki nan kowa ya fara tafi"

Hauwa ce tace'' aini wallahi A'isha wannan yarinyar bata birgeni ta cika iyayi gashi ita ba kokari ba "

dukkan su s**a amsa da wallahi kuwa.......
______________________________________________________________________________________

Wainnan yan mata guda bakwai sunyi shakuwa ta hanyar musamman wanda yakai ga duk wani ɗalibin makarantar yasan seven stars Kai har ma da Malam makarantar babu wanda bai san labarin su ba ta gurin ilimi da wasa duka sun haɗa kowanne su da irin burin su

____________________________________________________________________________

**Aisha Musa** – daga Kano. Mahaifinta Alhaji Musa Ƙaramin ɗan kasuwa ne mai wadatar zuci da rufin asiri, mahaifiyarta Hajiya Luba mai dinki ce. Aisha burinta shine ta zama babbar lawyer wacce zata taimaka wajen gyara “Zamantakewar Al’umma”
_____________________________

**Hauwa’u Bala**– itama yar garin kano ce anguwar Fagge, amma suna da nisa tsakanin ta da Aisha. Mahaifinta Malam Aminu Malami Primary ne,matar sa ɗaya Hajiya Maryam ƙaramar yar kasuwa ce mai siye da siyarwa ce a cikin gida. Hauwa’u bata da burin dogon karatu a rayuwar ta, babban burin ta shine tayi aure ta tara zuri’ah.
______________________________

**Rabi’ah Abdullahi** – daga Kaduna. Amma Mahaifin ta asalin ɗan kano ne, wanda nema ya kaisu garin kaduna shi da ɗan uwan sa, har s**a auri mata ye yan kaduna. Alhaji Abdullahi Injiniya ne, mahaifiyarta Bilkisu k*ma nurse ce. Ita ma Rabi ba tada wani burin dogon karatu mai zurfi k**ar yar uwar ta.
______________________________
**Zainab Umar** – itace yar uwar Rabi’ah wanda Mahaifan su suke yan uwa,waƴanda nema ya baro su daga kano ya dawo da su kaduna. Mahaifinta Alhaji Umar Babban kafin tane wanda Allah ya dauka kalashi ya sharaha aduniyar Kafinta, har ya buɗe manyan shaguna na sai da kayan furnitures wandda gidan su yake cikin layi man-mayan gidaduwan da suke cikin *Gwari Road* duk da bai kai nasu Rabi'ah girma da fadi ba sai dai da yake gidane na basu furnitures kana shiga parlour zaka san an narka dukiya ba ta sawa ba, hata part ɗin Sayyid yayan Zainab da ban yake, Mahaifiyarta k*ma ƙwararriyar mai girki ce a garin kaduna kowa yasan da ita. Zainab ce mai burin dogon karatu sosai shiyasa ko a cikin team din su na makaranta tata tafi zuwa ɗaya da Aisha mai son zama babbar lawyer.
______________________________
**Sadiya Salisu** – itama daga kaduna take. Mahaifinta bawani mai rufin asiri bane kusan duk ƙawayen sun fisu hali,Mahaifin ta ɗan kasuwa ne mai ƙaramin ƙarfi. mahaifiyarta k*ma Malamar primary ce. Sadiya Umar bata da buri dogo karatu Saboda tasan ko ta ɗora hakan zata wahalar da kanta ne.
______________________________
**Fatima Garba** –Ƴar Asalin jahar katsina ce cikin Unguwar *Tudun Matawale Katsina* Mahaifinta manomi ne,Wanda ya samu Albarkar noma da Ake fitar masa dashi Jaha jaha har da ƙasahe ƙetare k**ar su Niger, k**aru da Su Chadi, hakan yasa gidan sa baza ka taɓa ɗauka gidan Manomi ba ne,ta taso da buri ta zama sharariyar marubuciyar litatafan hausa dan kara tun tana Primary ta fara harkar butu,
Fatima ita ce 'ya Ta uku tana da Yayu biyu a ma'aura Sai ita ta Uku, Mahaifin ta bai bari Yayan Fatima sunyi zurfi akaratu ba yake musu Aure wanda Fatima ta nuna sonta da karatu dan ta inganta harkar rubutu ta, gani ta zurfafa, yasa shi barin ta tafi karatu Zaria, mahaifiyarta mai gyaran jiki ce,suna da rufin asiri dai dai gwargwado. Fatima ma na da burin dogon karatu saboda ta ɗauki son rubuta litatafan hausa ta ɗorawa kanta agani ta nance hanya mafi sauki guri isar da saƙon ta, duk da son karatu ta bai kai na zainba da Aisha ba.
______________________________
**Jamila Adamu** –Ƴar Asalin garin Zariya ce unguwar *Kabala consting Zaria* Ita kaɗai ce daga cikisu haifafiyar Zaria. Mahaifin Finta Alhaji Adamu Umar Ma'aikaci Banki ne ya riƙe muƙamai da dama shi yasa yake da buri 'ya'yan sa suyi karatu mai zurfi. mahaifiyar ta Fatima wace a ke Kiranta Da Ummi kasuwanci take na gida iri Online Business na material, Atanfofi da Takalma har adashi gata take yi na masu ƙaramin ƙarfi wanda basu da kuɗi haɗa kayan kitchen. Buri Jamila ta zama shararriyar mai ilimin kimiyya
______________________________

*Kaɗan daga cikin Tarihin Saven stars*

Aisha,sadiya da fatima anan su kayi junior ɗinsu, sun kasance taurari masu haskawa acikin ɗaliban GGSS,

Suna shekarar ƙarshe a junior jamila ta shigo makarantar, Irin ƙoƙarin da ta shigo da shi makarantar yasa ko da tayi niya shiga team din su na 3 star’s basu hana taba.

Haka s**ayi ta baza capacity a cikin makaranta, yan mata masu ƙoƙari, kyau, gayu uwa uba tsafta. Suna burge duk wata ɗaliba dake cikin GGSS Zaria.

Shigar su Senior secondry section yayi dai dai da kawo su Rabi’ah da Zainab, waƴanda s**a shigo a 2 stars, kasancewar su yan uwa cousin sister ga kyau ga gayu ga ƙoƙari.

Basu sha wahala ba s**a haɗe da four star’s kasancewar duk wanda take makarantar yasan labarin waƴanan ƴan mata, hakan ya mai da su six star’s.

Ƙarshen gama s.s 1 ɗinsu akayi wa Hauwa bala transfer daga GGSS kwatar kwashi zuwa zaria, wacce itama ta kasance tauraruwa acan.

Sir Ɗanladi da kansa ya haɗa six stars da Hauwa sabida yasan irin ƙoƙarin ta kwatar kwashi,

Tundaga wanan lokaci s**a koma seven stars for life, Taurarin ɗalibai da ake ji dasu kaf faɗin GGSS ZARIA tunsuna S.S 2 s**a doke yan S.S.3 ko quiz ko debate su ake sawa.



Malamai da ɗalibai suna alfahari dasu, shigar su S.S.3 akayi musu prefect.tabbas kowa yasan saven stars sun yi gyara a GGSS ZARIA, sun saita kan ɗalibai.



Sun yi gyara yanda yak**ata acikin wanan makarantar, k**a daga tsaftar ɗalibai, gyaran hostel, school compound, classes dasu liabiry.

Haka wajen turancin ɗalibai ma sunyi ƙoƙarin da ko bayan basa GGSS ZARIA za’ayi alfahri da saven star’s

___________________________________________________________

Yau ta k**a ranar Juma'a ce, wacce ta kasance ranar karshe a wanan term din, bayan sun gama WAEC mock test.

Ƙarar buga bell yasa Makaranta ta cika da ihu da murna, ɗalibai na fitowa da ihu da murnar samun hutu.

Saven star ne suke tafiya cikin gayu da jan aji da nuna zallan yan matance, tafe suke suna hira cikin gayu abinda ke burge duk wata ɗaliba daga GGSS, kai tsaye hostel s**a nufa domin su basu a hotun zasu zauna rubuta exam,

Duk wata ɗaliba idan tagansu sai ta tsugunna ƙasa ta gaishe su cikin harshen turanci, har s**a ƙarasa hostel.

“Sister leenah a rayuwa ta bani da wasu role models k**ar saven stars, yan matan nan duniya ne.”

“Bari ke dai sis Misha, idan nazama ɗaya daga cikin su, nasan bani da wata damuwa daga nan har A GIDAN AURE NA, domin waƴanan ƴan matan sun haɗa komai da zai hana su damuwa a ko ina.”


Wasu yan mata guda biyu dake tsaye da trolleys ɗinsu alamun tafiya zasuyi suke hirar

Haka ɗalibai s**a watse daga GGSS ZARIA s**a bar iya seniors a cikin makaranta waƴanda suke shirin fara exam ranar monday.
_________________________________________________

An fara exam, saven stars sun dage sun mai da hankali kowacce peaper buge ta suke batare da wata damuwa ba.


A haka har ɗalibai s**a dawo daga hutun term s**a same su, dai dai lokacin dasuke rubuta final exam.



Ɗalibai sun sha kuka sosai tare da faɗin

“We love you seven stars, we will miss you saven stars.”

Basu sami damar tafiya gida a wanna ranar ba sai zuwa gobe, zama s**ayi suna kafa hira domin yau kwanan zaune s**a shirya.

“Ba time ɗin da nake tunawa sai sanda malam
Zubairu ya tambaye ni menene 'photosynthesis', sai nace masa 'wata sinadari ce da ake amfani da ita wajen gyaran fata'. Sai yace, 'duk class ɗin ku photoshame ne.'” Jamila fafaɗa tana dariya

Dukkansu suma s**a fashe da dariya. Fatima Garba kam cewa tayi.
“Nikam sanda muke S.S.2 lokacin da muka cinye su Anty Hanny yan S.S.3 a wanan spelling B competition ɗinan..”

Ba takai ga ƙarasa wa ba duka s**a fashe da dariya, inda Jamila tace

“Unforgettable memories kenan a kaf zaman mu a GGSS ZARIA.”

“ Girls we have something to discuss.”

Aisha tafaɗa tana tasowa daga inda take zuwa tsakiyar su, da kallo s**a bita har sanda ta ƙarasa zama.


Kasancewar duk cikin su tafi kowa iyayi, yasa sai da ta gyara bakin ta sanan tace

“Kunsan Rabi is getting married ƴan watanni bayan candy din mu, to k**a ta yayi muyi magana akan rayuwar Gidan Aure, dan ni in ada burin *A Gidan Aure Na* na kasance sarauniya mai juya zuciyar mijin ta, k*m ina son k*ma duk ku kasance haka.”

“ To *A Gidan Aure Na* inda banzama sarauniya mai juya zuciyar mijin ta ba me zanyi?.”

Hauwa tafaɗa tana gyara zama

“Uhm anzo maganar Aure anzo fanin dasu Hauwa ke so.”

Sadiya tafaɗa domin kowa yasan yansa Hauwa ke son aure.

“Mitcheww inada abinda yafi Aure da rayuwar gidan aure mahimmanci dan haka bada Zainab.”

Tafaɗa tana tashi ta nufu bed, da kallo s**a bita Jamila ce ta kalli Rabi sanan tace.

“Nasha faɗamiki yarinyar nan ba lafiya take ba kinƙi yarda,Allah idan kuka koma kifaɗawa su Daddy a nema mata magani.”

“Asibitin dawanau na kano ne akaina.”

Zainab tafaɗa daga nan inda take shirin kwanciya.

“Kunga dan Allah don't spoil our mood,Muyi maganar gidan Auren nan ita tafi Muhimmanci.”

Aisha tafaɗa tana taɓosu alamun su ƙyale zainab.

“Yanzu me k**eso?.”
Hauwa ta faɗa alamun tambaya ga Aisha

“uhm kaji shegiya yanda tayi magana k**ar wata uwar mata.”

Zainab dake kwance ta ƙara faɗa.

“Zainabu gidan ku! dan Allah karki raba mana hankali, tunda you are not with us.”

Aisha tafaɗa sanan ta maida hankali kan Hauwa.

“Yanda *A Gidan Aure na* zanzama Tauraruwa k**ar yanda nake a makaranta! Yanda *A gidan Aure na*
zanzama sarauniya! Yanda a gidan Aure na…

Ke daka ta uwar yan son zuciya A gidan Auren mu dai.”

Rabi ta tare mata numfashi, dariya s**a saki gaba ɗayan su sanan Hauwa ta gyara zama k**ar zata basu lecture.

“Kunga abu nafarko shine Kissa da Kisisina😂.”

Dariya s**a ƙara fashewa da ita gaba ɗayan su, Zainab dake kwance tace.

“ Ko ni da ba lissafin aure nake ba nasan kissa da kisisi na ba abunda zai riƙe miki sure bane.”

Fatima da kusan tunda aka fara magana bata ce komai ba,gyaran murya tayi sanan face

“Kun san ance A gidan Aure Haƙuri kawai akeyi.”

“Hakuri k*ma Fatima wane kalan Haƙuri?.” Aisha ta tambayeta

“Haƙuri dai wanda kika ji nafaɗa.”

“with due respect ƙarya k**e Fatima duk soyayyar da ake sha sanan ace za’ayi hakuri.”

“faɗa mata dai Aisha, ya zaai ce haƙuri ake a gidan auren, ina amfanin soyayya da kalaman soyayya.”

Hauwa tafaɗa tana harar Fatima da tayi magana.

“Wallahi Allah sister zaman aure hak’uri ake yi.”
“Kin tabayin aure ne da zaki sani?.”..

uhm This is just the beginning yan mata suna magana akan gidan Aure

Komai fa baifara ba, wanan farkon farko ne, domin basu masan me zasu zama ba.

*Daga zukatan mu zuwa shafin ku*

Reaction da comment sune karfin gwiwar mu

Lallai taurari bakwai suncika taurari

*MA'UM*💕💕💕💕💕💕💕   *stroy and written*              *By*_*sani Muhammad lawan*_         SMLAWAN AKA MR             perfect...
12/02/2025

*MA'UM*
💕💕💕💕💕💕💕

*stroy and written*
*By*
_*sani Muhammad lawan*_
SMLAWAN AKA MR
perfection

_ALLAH YASAKAWA IYAYEN MU DA MAFIFICIN ALHERI_

*✨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION✨*

*T.M.W.A.✍️*

✨✨✨✨✨
💪😊

*TUNANI MAI ZURFI KAFIN RUBUTU SHINE TAKEN MU, RUBUTU MAI FAD'AKARWA DOMIN AL'UMMA,AL'K'ALAMIN MU ABIN AL'FAHARINMU, RUBUTU BAIWA CE GA WANDA ALLAH YA BAWA,TAKENMU SHINE HASKAWA A CIKIN AL'UMMA DA FIKIRAR DA ALLAH YA MANA, TAURARU A DUNIYAR MARUBUTA.*

✨✨✨✨✨
💪😊

Bismillahi rahmanirraheem

page 2

*[The history]*
.......Ihu take tare da neman taimako ba abinda bakin ta yake fadi sai meena meena

...........Asalin labarin
Mal Usman dan asalin garin barno ne wanda kasuwanci yakawoshi garin Kano tare da matarsa aisha batare da yasan kowa ba tun zuwanshi Allah yahadashi da malam abdullahi Wanda yake dan asalin garin Kano malam Abdullahi irin fulanin nanne da bangaren uwa da matarsa bilkisu wacce take bafula tanar gombe tun zuwan malam usman garin Kano allah yahadashi da mal Abdullahi inda s**a fara abota har ta koma yan uwantaka haka bangaren matansu ma haka suke k**ar yan uwa bilkisu tarike aisha k**ar kanwarta dasuke uwa daya uba daya har wasu cikin makwafta ma basusan ba yan uwa bane suna zaune cikin unguwa daya taxarar gidajen su bashida yawa suna taimakon junansu sosai da sosai malam Abdullahi yana da yara biyu umar shine babba tazarar shekarar 12 ce tsakanisa da kanwarsa naima shik*ma malam usman yana da yara 4 mata 3 saik*ma namiji guda daya khadija ce babba wacce shekara biyu ne tsakanin ta da umar saik*ma hauwa datake biye mata wacce ita k*ma umar yabata shekara 3 saik*ma namiji wanda akayiwa malam Abdullahi takwara anacemasa abdul sai bayan shekara aka Haifi maryam wacce itak*ma sati 3 ne tsakaninsu da shatu wacce kayiwa umma takwara haka yaran s**a taso cikin soyayyar juna baka tababa banbance tsakaninsu a haka rayuwa taita tafiya a cikin wayanan a hali guda biyu tun maryam nada shekara biyu umar yakejin yarinyar a cikin ranshi fiye da yanda yakejin shatu tun tana shekara biyar Umar yasan yanason maryam wani irin so yakeji yana mata mai zauna mutum sanda takai shekara Goma lokacin kowa yagani Umar yana matukar Sonta k*ma shima lokacin ya fito da soyayyarsa gareta haka maryam tatashi da soyayyar umar a cikin zuciyarta *MAUM* shine sunan sunan da kawayenta ke kiranta sunan yayiwa umar dadi hakan yasa shima yamaida inkiyarshi *MAUM* soyayya ake gudanarwa mai tsafta bangaren rayuwa maryam tana da sanyi hali sosai da sosai bada hayaniya ko kadan haka shima ma umar bashida hayaniya sosai akwai miskilanci kasancewar umar shine babba a wajen mahaifiyarshi hakan yasa takesa umar tayata ayyukan gidan umar yanason yin girki sosai da sosai idan yayi girki kowa jindadin shi yake a gidan har wani lokacin abba yakance masa malam umar ko dai abincin ka a girki yake hakan yasa ummanshi ta hanashi girkin domin bata jindadi anacewa anan abincinshi yake sanda umar yagama secondary school yahuce school of hygiene yayi diploma dinshi bangaren health bayan ya kammala ne yajuya catering inda yayi certificate anan sanda umar yagama school of hygiene tabbas inda yayi maka girki zakace irin akasar turawan nanne bayan gama certificate dinsa yakoma kasuwanci tare da iyayensa a lokacin khadija da hauwa duk sunyi aure soyayya kam kara guda na take tsakanin umar da maryam wacce take bawa kowa shaawa shakuwa kam ba a magana
Cigaban labari.........!!

*comment and share fisabilillah*

_Please follow_👇👇

*whatsapp group*

https://chat.whatsapp.com/DRdQmNLHoqmDle4kdM3Thr

*WhatsApp channel*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb5SXd98fewwEByet33d

*MA'UM* 💕💕💕💕💕💕💕       *Story and written*                  *By**_Sani Muhammad Lawan_*       SMLAWAN AKA MR            P...
11/02/2025

*MA'UM*
💕💕💕💕💕💕💕

*Story and written*
*By*
*_Sani Muhammad Lawan_*
SMLAWAN AKA MR
Perpection

TSOKACIN FARKO!!!
*_LABARIN SOYAYYAR UMAR DA MARYAM WANAN LABARIN SOYAYYA NE DAYA ZO MUKU DA SABON SALO WANAN KIRKIRAREN LABARI NE BAN RUBUTA SHI DOMIN CIN ZARAFIN WANI KO WATA BA IDAN KUMA YAYI KARO/SHIGE KO KALA DA WANI BARI NA RAYUWARKA INA DAGA HANNU BIYU INANEMAN AFUWARKA_*

*_SADAUKARWA!!!_*
_NA SADAUKAR DA WANAN LABARIN SOYAYYAR ZUWA GA MAHAIFIYATA (zahrau kabir bature) ALLAH YAFARANTA MIKI YA SAKA MIKI DA GIDAN ALJANNA SANAN NAKARA SADAUKAR DASHI GA YAYATA YAR UWATA (Fatima Muhammad lawan) ALLAH YA HASKAKA RAYUWA SANAN NAKARA SADAUKAR DASHI GA DIMBIN MAKARANTA LABARAN HAUSA MAZA DA MATA ALLAH YABIYA MUKU BUKATUN KU YAFARANTA RAYUWARKU_

_ALLAH YASAKAWA IYAYEN MU DA MAFIFINCIN ALHERI_

TSOKACI NA BIYU!!!
*KAMAR YANDA NAFADA ABAYA WANAN LABARIN SOYAYYA NE DA YAZO MUKU DA SABON SALO AKWAI ABUBUWA DA ZASUYI MUKU DADI LABARIN SOYAYYA NE MAI TABA ZUCIYA ZAKU KARU DA ABUBUWA DA DAMA SANAN DA AKWAI* *ABUBUWANDA BAZASUYI MUKU DADI BA TO INASO KUYI AMFANI DAABUBUWAN DASUKAYI* *MUKU DADI WAJEN ADALCI GARENI SANAN KUYI WATSI DA ABUBUWANDA BADAIDAI BA KASANCEWA TA NA DAN ADAM AJIZI KUMA WANAN SHINE LITTAFI NA NAFARKO DUKDA BASHI NE LABARI NAFARKO BA*

*GODIYA*
_INA KARA MIKA GODIYA TA GA ALLAH SUBAHANAHU WATA ALA DAYABANI DAMAR RUBUTA WANAN LABARINDUMBIN GAISUWA TARE DA TARIN SOYAYYA GA DAN UWANA AMMAR HARUNA MUHAMMAD_

*GARGADI!!!*
_KADA WANI KO WATA YASAUYA MUN WANAN LABARIN KO YAYI AMFANI DA WANI BANGARE DAGA CIKI BATARE DA IZINI BA_

*Muje zuwa......✍️*

Bismillahi rahmanirraheem

Page 1

*[The beginning of the Story]*

......kano state Nigeria unguwar sharada tana daya daga cikin manyan ungoyoyi da suke cikin garin Kano, unguwar sharada unguwa ce mai girma da allah ya albarkace su da ruwansha mai dadi kasancewa shekaru kafin yanzu unguwar fadamace hakan yasa suke da wadattacen ruwan sha mai dadi dak*ma lambo kasancewar unguwar tanada sanyi da danshi,
Cikin sharada phase2 bangaren masu matsakaicin Karfi cikin wani babban layi wanda ake kira da babbar hanya zaratan samari ne zaune kan Benci suna hira cikin zaratan samarin ido na yasauka kan wani guda Wanda yake daga gefe k**ar badashi ake caftar ba sanye yake cikin white sheat da wando na jeans,

hankalinshi na kan babbar hanya da alamu akwai abinda yake jira baki ne amma ba can ba chocolate colour tarin yan mata ne s**a kutsu babbar hanyar sanye do coffee colour din hijabi da alamu daga islamiyya suke duk tarin yan mata da suke kutsuwa hakan bai hana idanu sa gano masa abar kaunarsa ba wacce yazauna jiranta a koda wane lokaci yakan zauna jiranta tafiya take cikin nustuwa dukda suma sauran yan matan a nusten suke tafiya yan mata suna tafiya ne in group k**an yanda suke tafe cikin group su uku daya a cikinsu mai suna haleema ce tace shatu ga yayanki fa yana jiranka wacce a kira da naima ce tace yayan maryam dai tundaga kallo daya zaka k**anninta da Guy din wacce aka Kira da maryam tace eeyh yayana nikadai to daman ai sai ke din cewar shatu dariya halima tayi sanan tace to yayan maryam murmushi maryam din tayi wanda yasa dimple din ta dake bari daya ya loba maryam kyakyawa ce irin kyawawan nan na gaske a haka har s**a karaso inda yake tsaye halima ce tafara gaidashi sanan shatu maryam kam a hankali ta gaidashi cikin salon soyayya amsawa yayi fuskarshi dauke da murmushi wanda ya kara bayyana zallan kyawun sa kyakyawa ne nagaske as I said Bakine irin black beauties dinan Yanada dara daran idanu masu kyau da kwarjini hancinsa mai matsakaicin tsayi ne sanan Yanada kyawawan pink lips kasancewar shima dauke yake da murmushi hakan yabawa dimple dinshi damar bayyana (yaya umar) sunan da na tsinkayo muryar shatu na fada baby andawo yafada amma still idanunsa na kan maryam da murmushi Yaki barin fuskarta eeyh yaya nadawo to akai lada gida bari naraka antin ki ko dariya halima tayi dan duk wanda yake tare da maryam da naima yasan ta waje daya suke fada acewa maryam antin shatu maryam ce tace da naima kanwata sai anjima sanan tabi bayan yaya umar dayayi gaba shatu bata tankaba tayi gaba halima tabi bayansa saida takaraso wajenshi sanan tace my man naam my angel yafada yana kallonta my man kayi kyau ai kullum acikin kyau nake a wajenki allah my man kayi kyau naji amma ai kinfini kyau dariya maryam tayi kafin tace nidinwa nakai ka kyau yayana kedin yaya umar yafada to nayarda maryam tafada tana k*mshe dariyar umar dayahade rai kasancewar sunzo hucewa ta wajen wasu maza suk*ma sun kurawa maryam din idanu babban abinda yake karawa maryam matsayi a zuciyar umar bata taba musu dashi ba ko da awasa yana fadin abu zatace tayarda a haka har s**a karaso kofar gidan su maryam din wanda ananma s**a tsaya a waje s**a cigaba da hirar su wacce take kara musu shakira saida sika kwashe kimanin Mintuna 20 sanan Umar yace my angel kishiga gida kinga anfara kiran sallah to sheknn yaya me xantawo miki dashi idan zandawo komai ma tafada sanan tashige gida shima masallaci yanufa gida tashiga dauke da sallama umma dake zaune a bakin famfo tana daura alwala ce ta amsa mata tare Dacewa juliyat iyayen soyayya sai yanzu aka shigo murmushi maryam tayi sanan tashige dakinta.!!

*Comment and share fisabilillah 🙏*

For WhatsApp group 👇
https://chat.whatsapp.com/DRdQmNLHoqmDle4kdM3Thr

08181170719
*WhatsApp channel*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb5SXd98fewwEByet33d
*_~Mr.perfection gareku~_*

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mr.perfection novels posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share