04/08/2025
*A GIDAN AUREN NA*👰♀️🤵👩❤️👨
*( in my marital home )*
https://chat.whatsapp.com/EoKZbPkphsuJIxZECUVZlE
*_Stroy and writing_*
by
*_Seven star writer’s_*
______________________________________________________________________________________
Wani Littafi ne dake cike da ƙalu b***n da ake fuskanta a gidan auren........
____________________________________________________________
An rubuta wannan littafi ne karkashin jagorancin kungiyar:
🖋 TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOATION 💫
Team ɗin da ke da alhakin wannan aikin:
✨ SEVEN STAR'S WRITER'S TEAM ✨
______________________________________________________________________________
Membobin cikin ta:
1. [Rukayya Yusuf Ibrahim (CEO A Y M place)]
2. [Hussaina Abdullahi (Oumu Muwaddah)]
3. [Salamatu Hussaini (Queen Bee ko Àutar mama)]
4. [Fatima .Y. Zakariyya(Tymer's Henna)]
5. [Sani Muhammad Lawan (S M Lawan )]
6. [Maijidda Bashir Sharu (Jidda Pretty )]
7. [Hadizatu mrs kd]
___________________________________________________________________
[Page 2]
Tagumi Fatima ta zuba dan tasan komi zata gayawa Hauwa da Aisha ba lallai su yarda ba, kallon su tasake yi cikin nutsuwa sanan tace.
“Haƙuri dai wanda kika ji nafaɗa.“
Tsaki Aisha ta ja tare da cillawa Fatima harara.
“with due respect ƙarya k**e Fatima duk soyayyar da ake sha a waje, sanan ace hakuri za’ayi a ciki”
“faɗa mata dai Aisha, ya za'ai ce haƙuri ake a gidan auren, ina amfanin soyayya da kalaman soyayya?.”
Hauwa tafaɗa tana harar Fatima da tayi magana.
Sadiya ce tace.
“Wallahi Allah Aisha maganar Fatima tana kan dai-dai, dan nasha karo aciki wasu litatafai na manyan marubuta masu fasaha,da fikira wanda ko da a zahiri sunsan ilimin aure dan wasu zasu haifi k**ar mu kin ga kuwa suna da Experience”
Hauwa da maganar Sadiya take ɓatawa rai ta taɓe baki sanan tace.
“Ko jikina kunene sai dai ki barni dan Gidan Habibi duniya ne”
A fusace Fatima tace.
“Tom Shikenan Hauwa amma ku sani A matsayina na na marubuciya, ina da experience da yawa akan rayuwar Aure.”
“uhm sannu marubuciya! fad’amana experince ɗin naki.”
Zainab ta faɗa tare da ta sakkowa zuwa inda suke, gyara zama Fatima tayi sanan tace.
“A iya nazari na, da tunani na Aure ba abunda zaku yi tunanin kasancewa cikin farin ciki a ko da yaushe bane, Aure zamane da ake fatan yin shi har abada, to harshe da hak’uri ma ana saɓawa b***e mutane Yan adam da muke tara bamu cika goma ba”
“Ban tari numfashin ki ba Fatima Amma kina nufin ba’a samun soyayya a gidan Aure?.”
Zainab da ta taso tadawo cikin su ta tambaya.
“Ban isaba Zainab! ban isa nace a gidan aure ba a samun soyayya ba, amma tabbas soyayyar da kika yi tunani ko kika samu a waje ba ita ake samu a gidan aure ba, saboda haka ban ɗorawa raina ba,tunda har yanzu banyi aure ba.
“Maganar Fatima tana kan dai dai, k*ma hakan yana cikin abubuwan da yasa nakai aure last plan ɗina, naga aure da dama wa ɗanda ba in da suke zuwa, wasu k*ma ana tare amma kullum cikin tashin hankali, mazaje na wahalal dasu wasu k*ma matayen ke wahalal dasu idan sunga sunfi rufim asiri.”
Zainab tafad’a tana kallon su, sai da ta gama kallon tsaf sanan ta d’ora da cewa.
“Ina da burin nayi karatu mai zurfi, na zama babbar mace wanda ko da nayi aure mijina ba zai kalleni da rashin daraja ba acikin Gidan Aure na ba, yiwa yarinya Aure a ƙananu shekaru bashi da amfani.”
“Tabbas Zainab tunda ake maganar Aure baki taɓa ta hankali ba sai yau.”
Cewar Rabi'ah k**ar masu jira Rabi'ah ta tsagaita s**a fashe da dariya baki ɗayan su.
Daga nan k*ma hirar tasu ta koma kan ƙalub***n Gidan Aure har zuwa sanda bacci ya fara ɗauke su.
________________________________________________________________
Tsaye suke cikin compound ɗin school ɗin gaban su cike da trolleys da sauran kayayyakin su.
Sak**akon k**allh pepar ƙarshe k*ma yau duk wani wanda ya gama GGSS ZARIA, Aji na Shida yake komawa gida.
Fatima ce cikin Muryar kuka tace
“I wished aure ya kawo ni kano ko kaduna ko zaria, saboda na dinga ganin ku a ko yaushe.”
Dariya Sadiya tayi sanan tace.
“Aifa mu nan duk kusa muke, ke kaɗai ce kika luluƙa can katsina”
“Shiyasa ai duk nafi damuwa saboda nasan ganin ku sai dai nina zo, amma ko kam babu wacce za tazo Tudun Matawale”
“Haba darling sis! ya za’ai kice haka zamu haɗu sosai, yanzu ga bikin sister Rabi'ah nan,promised you inda kika zo bikin sister Rabi'ah zan biki muje Tudun Matawale insha Allah,
amma sai kin fara zuwa gidan mu kin kwana biyu bayan biki.”
cewar Jamila kenan, rungume ta Fatima tayi sanan tace
“shikenan darling sis.”
cikin muryar kuka.
Matsowa zainab tayi ta rumgume su tace.
“ I love you girls wallahi nasan zanyi kewar ku, waya ko group chat bazai ɗebemun kewarku ba.”
Haka sauran s**a marmatso s**a rungume juna suna hawaye,
students s**a tsaya suna kallon su wasu harda tayasu kukan, domin kowa yasan irin alaƙar dake tsakanin saven stars, ko irin munafuncin nan da akeyi na cikin ƙawaye to su basu.
Malam Madu driver school ne mai kai daliban kano, shine yayi musu sallama tare da cewa.
“ To 'yan bakwai abani tagawaye na nahuce dasu.”
Dariya s**a yi dukkan su sanan su Aisha da Hauwa s**a fara ɗaukan kayansu.
“Am Baba madu ko zan biko ku sauke ni a Zaria.”
Jamila tafaɗa cikin zolayar da duk hutu sai ta tsokani Baba Madu.
“Ai fa sai dai Zaria Jamsee”
Cewar Zainba da ta kin-kimi tata trolley da zumar ta matsa daga guri.
Dariya Baba Madu yayi ya ɗauki kayan Aisha dana Hauwa ya dubi Jamila.
“Badamuwa ɗako kayan naki.”
Ya faɗa yana nufar inda motar sa take ajiye.
Muryar Zainab s**a ji tana fad’in
“Kutumar uba! Auzubillahi.”
ta haɗe a lokaci guda.
“Ke zainab lafiyan ki? k**e wa mutane zagi k**ar arniya.”
Sadiya ta faɗa tana kallon zainab
“Uhm Sadiya barni bakisan masifar da na gano ba.”
tana mai komawa inda Rabi’ah ke tsaye
“Ke rabi kalli.”
Zainab ta faɗa tana nuna inda mota ke shigowa
“Auzubillahi yau ranar ƙarshen ma sai an turo mana tashin hankali.”
Dariya su Hauwa s**a fashe da ita dan su gano abinda ya tsorata Zainab yasa ta zagi sanan ya ki ɗima rabi.
YAYA SAIYYID
dodon Zainab da Rabi kenan
“Kunga girls, sai mun
haɗu ban shirya karɓar tashin hankali ba.”
Zainab ta faɗa tana fara jan trolley ɗin da wasu kayan ta
k’ame wa tayi cak hango mutumin da tafi jin haushi a duniya.
______________________________
Daga cikin mota kam Saiyyid ne ya kalli Jawad yace.
“i’m always telling you ka fita sabgar marasa kunyar yaran nan amma kaƙi gashinan yarinya na ganin ka har ta haɗe rai saboda raini, ko mene abun burgewa a tare da ƙana nan yara oho?.”
“Buddy ba abin da zaka gane amma tabbas ƙananan yara sunfi daɗi soyayya, iya kulawa da mutunta miji ina son *A Gidan Aure na* nakasance Sarki ko na kasance Yariman da ake lallaɓawa.”
Jawad ya bawa Saiyyid amsa yana ƙoƙarin buɗe murfi motar ya fita.
“Jawad dan allah ka dinga k**a kanka a gaban yaran nan kar su raina ka fa.”
Bai bashi amsa ba ya bud’e mota ya fice, Zainab da tayi tsayuwar dole ta fara ƙok’arin had’e kayanta, daga can gefe k*ma Rabi ce tace dasu.
“Kuzo na baku gulma ta k’arshe a GGSS.”
Da sauri s**a tawo tare da cewa
“All ears with you.”
“Kunga wanan Yaya Jawad d’in abokin Yaya saiyyid ne, tun muna 'yan ƙanana yake mugun son Zainab, ita kam a rayuwar ta babu wanda ta tsana k**ar shi, ba wai k*ma shine kad’ai ta tsana ba duk wanda zai zo mata da maganar soyayya zainab ta tsane shi, kunsan wanda zan aura ɗan gidan chairman ne! kunga dai suna da kuɗi iya ka cik kud’i to wallahi sanda brother d’inshi ya nuna yanason zainab tun daga nan ta tsaneshi, zainab ta d’auki duniya da zafi akan aure yanzu ku tsaya kuga yanda zata kaya da Zainab da Yaya Jawad.”
Jamila ce tace.
“nikam yanzu bana ganin laifin Zainab tunda a jiya tafad’a mana dalilin ta.”
“Amma hakan ba ya bata dama ta dinga yiwa mutane rashin kirki ba, kiga sanda wanan copper d’in yace yana sonta.”
Hauwa tafad’a cikin ɓacin rai domin tabbas zainab ta fara kaita bango akan wanan mummunar ɗabi’ar tata.
“Zainab ba tada lissafin aure to mu kyale ta dan allah kowa dai yana da ra’ayin shi.”
Fatima tafad’a tana cigaba da haɗe kayanta wands take jiran drive da yake ɗaukar ɗaliban daga Zaria zuwa katsina.
A hankali ya tako zuwa inda take.
“Congratulations queen 👸 yanzu an kammala secondary school.”
ya fad’a cikin wani irin kwantar da murya, a d’an ya tsine ta d’ago ta kalleshi sanan tace.
“Thanks Yaya.”
“let me help you with the luggages.”
ya fad’a yana k’ok’arin k**a mata kayan, bata hanashi ba ta sakar masa sanan ta koma dakko sauran kayan, shik*ma yayi mota da wayancan.
“Sannu bawan mata.”
Saiyyid ya fad’a dai dai lokacin da Jawad ya k’araso wajen rik’e da jakunkunan, bai ko kalleshi ba yace.
“malam fito ka bud’e mana musa kayan mu.”
“You dey craze! nine zan taka k’asar makarantar nan? tabbas kaci kai.”
Saiyyid ya fad’a in i don’t care, domin tabbas tunda Saiyyid yake zuwa d’aukan su Rabi da Zainab bai tab’a taka kafara sa a wanan makarantar ba.
“Kuzo muje ku gaida su mana.”
Rabi’ah tafad’a dai dai lokacin da zainab ta k’araso wajen.
“Kunji jiki manyan munafukai.”
Zainab ta faɗa cikin masifar da ta zame mata jiki.
Dariya s**a saki gaba d’ayan su, sanan s**a taimaka musu wajen d’aukan ragowar kayan banda Sadiya da taji wani irin bugu da zuciyar ta wanda gaba ɗaya ya gama tsorata ta
“Sadiya ba zaki tawo bane.”
Fatima ta fad’a ganin duk sun tafi sun barta tsaye.
Sauri taita k’araso inda suke s**a taka.
Kamar kullum dai ba sakin fuska haka ya amsa.
Jawad ne dai sai da s**a gaji da magana ma.
___________________________________________
Lokaci da Rabi'ah da Zainab s**a bar makaran tar Babu wanda bai kuka ba.
Har get s**a bi motar suna musu bye bye..
Kafin s**a dawo suna tsaiwa motar da Zata kai Su Fatima katsina tazo.
Haka Aunty Hanney tazo da Keke napep ɗaukar Jamila.
A tare kowa ya shiga nasu Abin hawar dan k**a han yar garin su......
*Me yake jiran seven stars a gida?.”*
Karatu ne ko aure.
“Uhm this is just the beginning.”
Komai bai fara ba, wanan farkon farko ne.
*Daga zuk’atan mu zuwa shafinku*
Reaction da comment sune k’arfin gwiwar mu
Lallai saven star’s suncika taurari.