
12/02/2025
*MA'UM*
πππππππ
*stroy and written*
*By*
_*sani Muhammad lawan*_
SMLAWAN AKA MR
perfection
_ALLAH YASAKAWA IYAYEN MU DA MAFIFICIN ALHERI_
*β¨TAURARIN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATIONβ¨*
*T.M.W.A.βοΈ*
β¨β¨β¨β¨β¨
πͺπ
*TUNANI MAI ZURFI KAFIN RUBUTU SHINE TAKEN MU, RUBUTU MAI FAD'AKARWA DOMIN AL'UMMA,AL'K'ALAMIN MU ABIN AL'FAHARINMU, RUBUTU BAIWA CE GA WANDA ALLAH YA BAWA,TAKENMU SHINE HASKAWA A CIKIN AL'UMMA DA FIKIRAR DA ALLAH YA MANA, TAURARU A DUNIYAR MARUBUTA.*
β¨β¨β¨β¨β¨
πͺπ
Bismillahi rahmanirraheem
page 2
*[The history]*
.......Ihu take tare da neman taimako ba abinda bakin ta yake fadi sai meena meena
...........Asalin labarin
Mal Usman dan asalin garin barno ne wanda kasuwanci yakawoshi garin Kano tare da matarsa aisha batare da yasan kowa ba tun zuwanshi Allah yahadashi da malam abdullahi Wanda yake dan asalin garin Kano malam Abdullahi irin fulanin nanne da bangaren uwa da matarsa bilkisu wacce take bafula tanar gombe tun zuwan malam usman garin Kano allah yahadashi da mal Abdullahi inda s**a fara abota har ta koma yan uwantaka haka bangaren matansu ma haka suke kamar yan uwa bilkisu tarike aisha kamar kanwarta dasuke uwa daya uba daya har wasu cikin makwafta ma basusan ba yan uwa bane suna zaune cikin unguwa daya taxarar gidajen su bashida yawa suna taimakon junansu sosai da sosai malam Abdullahi yana da yara biyu umar shine babba tazarar shekarar 12 ce tsakanisa da kanwarsa naima shikuma malam usman yana da yara 4 mata 3 saikuma namiji guda daya khadija ce babba wacce shekara biyu ne tsakanin ta da umar saikuma hauwa datake biye mata wacce ita kuma umar yabata shekara 3 saikuma namiji wanda akayiwa malam Abdullahi takwara anacemasa abdul sai bayan shekara aka Haifi maryam wacce itakuma sati 3 ne tsakaninsu da shatu wacce kayiwa umma takwara haka yaran s**a taso cikin soyayyar juna baka tababa banbance tsakaninsu a haka rayuwa taita tafiya a cikin wayanan a hali guda biyu tun maryam nada shekara biyu umar yakejin yarinyar a cikin ranshi fiye da yanda yakejin shatu tun tana shekara biyar Umar yasan yanason maryam wani irin so yakeji yana mata mai zauna mutum sanda takai shekara Goma lokacin kowa yagani Umar yana matukar Sonta kuma shima lokacin ya fito da soyayyarsa gareta haka maryam tatashi da soyayyar umar a cikin zuciyarta *MAUM* shine sunan sunan da kawayenta ke kiranta sunan yayiwa umar dadi hakan yasa shima yamaida inkiyarshi *MAUM* soyayya ake gudanarwa mai tsafta bangaren rayuwa maryam tana da sanyi hali sosai da sosai bada hayaniya ko kadan haka shima ma umar bashida hayaniya sosai akwai miskilanci kasancewar umar shine babba a wajen mahaifiyarshi hakan yasa takesa umar tayata ayyukan gidan umar yanason yin girki sosai da sosai idan yayi girki kowa jindadin shi yake a gidan har wani lokacin abba yakance masa malam umar ko dai abincin ka a girki yake hakan yasa ummanshi ta hanashi girkin domin bata jindadi anacewa anan abincinshi yake sanda umar yagama secondary school yahuce school of hygiene yayi diploma dinshi bangaren health bayan ya kammala ne yajuya catering inda yayi certificate anan sanda umar yagama school of hygiene tabbas inda yayi maka girki zakace irin akasar turawan nanne bayan gama certificate dinsa yakoma kasuwanci tare da iyayensa a lokacin khadija da hauwa duk sunyi aure soyayya kam kara guda na take tsakanin umar da maryam wacce take bawa kowa shaawa shakuwa kam ba a magana
Cigaban labari.........!!
*comment and share fisabilillah*
_Please follow_ππ
*whatsapp group*
https://chat.whatsapp.com/DRdQmNLHoqmDle4kdM3Thr
*WhatsApp channel*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb5SXd98fewwEByet33d