01/06/2026
Gwamnatin jihar Kano ta nesanta kanta daga dukkan wasu masu hannu a faɗace-faɗacen daba da masu ɗaukar nauyinsu, tare da shan alwashin tabbatar da ɗaukar matakin shariʼa kan duk wanda aka samu da hannu a lamarin.
Arewa Updates ta rawaito cewa, Kwamishinan Shariʼ na Kano Abdulkarim Kabir Maude SAN ne ya bayyana hakan a wani faifan bidiyo da ya fitar.
Ya ce, Gwamnatin Kano ba ta tare da duk wanda ya ke tada fiitina ko ya ke sanyawa a yi faɗan daba.
Ya ci gaba da cewa, a shirye gwamnati take wajen yin aiki ba sani ba sabo ga duk wanda aka k**a da hannu a ayyyukan ƴan daba da ke addabar jihar.
Maude ya ce, tunda ya shigo ofis Gwamna bai taɓa ba shi umarnin a saki wani mai laifi ko wani da ake zargi ba.
Ya ce, koda yaushe Gwamna na ba da goyon bayan a yi shariʼa ba sani ba sabo.
A ƙarshe ya ce, za su murƙushe duk wani matsin lamba da wani zai yi don ganin an yi sassauci wajen yaƙi da matsalar.