12/11/2025
Ɗan Majalisar Wakilai na Kano, Sagir Koki ya bar jam'iyyar NNPP
Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar daga mazabar Birnin Kano, Injiniya Sagir Ibrahim Koki, ya sanar da focrwar sa daga jam'iyyar NNPP mai mulki a jihar.
A wata wasika mai ɗauke da kwanan wata 11 ga Nuwamba, 2025, Koki ya bayyana cewa rikicin shugabanci da ke kara tsananta a cikin jam’iyyar ne ya sa ya ɗauki wannan mataki.
A wasiƙar da aka aika wa shugaban jam'iyyar na mazaɓar Zaitawa da ke cikin Ƙaramar Hukumar Birnin Kano, Koki ya ce ya yanke wannan shawara ne bisa haƙƙinsa na doka da ya ba shi ‘yancin zaɓin jam'iyyar da zai shiga.
Ya bayyana cewa rikicin cikin gida da ke tsakanin shugabannin jam’iyyar a matakin ƙasa ya sanya ya ji cewa da wuya ya ci gaba da zama a jam'iyyar.