23/06/2025
YANZU YANZU: Shugaban ƙasar Amurika Trump ya roƙi China ta sa baki kada Ir@n ta rufe mashigar tekun Hormuz inda ya bayyana cewa Al'ummar ƙasar Amurika Zasu Shiga Wani Mawuyacin Halin idan ƙasar Iran ta rufe Tekon Hormuz, inji Trump
Gwamnatin Amurka ta roƙi ƙasar China da ta sa baki a lamarin Iran, domin hana ta aiwatar da shirin rufe mashigar ruwa ta Hormuz – wata hanya mai matuƙar muhimmanci ga safarar Man fetur a duniya.
Shugaban ƙasar Amurika Trump ne ya bayyana haka a wata sanarwa, inda ya ce kiran ya biyo bayan rahoton da kafar yada labaran Iran, Press TV, ta wallafa cewa Majalisar Dokokin Iran ta amince da shirin rufe mashigar.
Duk wani cikas ga harkar jigilar mai zai yi tasiri mai muni kan tattalin arzikin duniya gaba ɗaya, inji Trump
Mashigar Hormuz na daga cikin manyan hanyoyin ruwa da ake jigilar sama da kashi 20 cikin 100 na man fetur da duniya ke amfani da shi, kuma duk wani hargitsi a yankin yana da tasiri kai tsaye kan farashin fetur da kwanciyar hankali a kasuwannin duniya.
MKK Hameex TV