14/07/2026
Ƙarin Kuɗin NECO Ya Jefa Makomar Ilimi Cikin Barazana
Ilimi da Rayuwa
Editor Khadija sunusi Gwadabe
Ƙudirin ƙara kuɗin rijistar jarabawar NECO Senior Secondary Certificate Examination (SSCE) zuwa Naira 50,000 daga shekarar 2027 ya haifar da cece-kuce a Najeriya, inda masu ruwa da tsaki ke nuna damuwa kan tasirin da hakan zai iya yi ga makomar ilimi. International Human Rights Commission – Relief Fund Trust (IHRC-RFT), Reshen Najeriya, ta bayyana cewa wannan ƙarin na iya hana dubban ɗalibai, musamman 'ya'yan iyalai masu ƙaramin ƙarfi, damar rubuta jarabawar kammala sakandare, lamarin da zai ƙara yawan yaran da za su daina karatu.
Kungiyar ta jaddada cewa ilimi haƙƙi ne na kowane ɗan Adam, kuma gwamnati na da alhakin tabbatar da cewa kowane yaro ya samu damar yin karatu ba tare da cikas ba. Ta kuma yi gargadin cewa ƙarin kuɗin jarabawa a wannan lokaci na tsadar rayuwa na iya ƙara matsalolin rashin ilimi, talauci da rashin tsaro, domin masana sun daɗe suna bayyana cewa ilimi na daga cikin manyan hanyoyin gina al'umma mai zaman lafiya.
Saboda haka, IHRC-RFT ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Ma'aikatar Ilimi da su sake nazarin wannan shiri tare da janye shi, tare da mayar da hankali kan manufofin da za su faɗaɗa damar samun ilimi ga kowa. A cewar kungiyar, saka hannun jari a ilimi ba kawai zai amfani ɗalibai ba ne, har ma zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki, rage aikata laifuffuka da gina makoma mai kyau ga Najeriya.